< Jérémie 25 >

1 La parole qui fut adressée à Jérémie sur tout le peuple de Juda, la quatrième année de Jojakim, fils de Josias, roi de Juda (c'était la première année de Nabuchodonosor, roi de Babylone),
Magana ta zo wa Irmiya game da dukan mutanen Yahuda a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wadda ta kasance shekara ta fari ta Nebukadnezzar sarkin Babilon.
2 parole que Jérémie, le prophète, adressa à tout le peuple de Juda et à tous les habitants de Jérusalem:
Saboda haka Irmiya annabi ya ce wa dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima.
3 Depuis la treizième année de Josias, fils d'Amon, roi de Juda, jusqu'à ce jour, c'est-à-dire depuis vingt-trois ans, la parole de Yahvé m'a été adressée, et je vous ai parlé, me levant de bonne heure et parlant; mais vous n'avez pas écouté.
Shekaru ashirin da uku, daga shekara ta goma sha uku ta Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda har zuwa wannan rana, maganar Ubangiji ta zo mini na kuma yi muku magana sau da sau, amma ba ku saurara ba.
4 L'Éternel vous a envoyé tous ses serviteurs, les prophètes, en se levant de bonne heure et en les envoyant (mais vous n'avez pas écouté ni prêté l'oreille pour entendre),
Ko da yake Ubangiji ya aika dukan bayinsa annabawa gare ku sau da sau, ba ku saurara ba, ba ku kuma kula ba.
5 en disant: « Que chacun revienne maintenant de sa mauvaise voie et de la méchanceté de ses actions, et qu'il habite dans le pays que l'Éternel a donné à vous et à vos pères, depuis toujours et à jamais.
Sun ce, “Ku juye yanzu, kowannenku, daga mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa iya zauna a ƙasar da Ubangiji ya ba ku da kuma kakanninku har abada abadin.
6 N'allez pas après d'autres dieux pour les servir ou vous prosterner devant eux, et ne m'irritez pas par l'œuvre de vos mains; alors je ne vous ferai aucun mal. »
Kada ku bi waɗansu alloli don ku bauta ku kuma yi musu sujada; kada ku tsokane ni in yi fushi da abin da hannuwanku suka yi. Sa’an nan ba zan kawo muku lahani ba.”
7 « Mais vous ne m'avez pas écouté, dit l'Éternel, afin de m'irriter par l'ouvrage de vos mains, pour votre propre malheur. »
“Amma ba ku saurare ni ba,” in ji Ubangiji, “kun tsokane ni da abin da kuka yi da hannuwanku, kuka kuma kawo lahani wa kanku.”
8 C'est pourquoi Yahvé des armées dit: « Parce que vous n'avez pas écouté mes paroles,
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Domin kun ƙi ku saurara ga maganata,
9 voici, j'enverrai prendre toutes les familles du nord, dit Yahvé, et j'enverrai mon serviteur Nebucadnetsar, roi de Babylone, et je les ferai venir contre ce pays, contre ses habitants et contre toutes ces nations d'alentour. Je les détruirai par interdit, et j'en ferai un objet d'étonnement, de sifflement et de désolation perpétuelle.
zan kira dukan mutanen arewa da bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon,” in ji Ubangiji, “zan kuma kawo su su yi gāba da wannan ƙasa da mazaunanta da kuma gāba da dukan al’ummai da suke kewaye. Zan hallaka su sarai in kuma mai da su abin bantsoro da abin dariya, za su kuma zama kufai har abada.
10 Je leur enlèverai la voix de la joie et la voix de l'allégresse, la voix du fiancé et la voix de la fiancée, le bruit des meules et la lumière de la lampe.
Zan kawar da muryoyin farin ciki da murna daga gare su, muryoyin amarya da na ango, ƙarar dutsen niƙa da hasken fitila.
11 Tout ce pays sera une désolation et un objet d'épouvante, et ces nations serviront le roi de Babylone pendant soixante-dix ans.
Dukan wannan ƙasa za tă zama kango, kuma waɗannan al’ummai za su bauta wa sarkin Babilon shekaru saba’in.
12 « Quand soixante-dix ans seront accomplis, je punirai le roi de Babylone et cette nation, dit Yahvé, à cause de leur iniquité. Je réduirai le pays des Chaldéens en désolation pour toujours.
“Amma sa’ad da shekaru saba’in ɗin suka cika, zan hukunta sarkin Babilon da kuma al’ummarsa, ƙasar Babiloniyawa, saboda laifinsu,” in ji Ubangiji, “in kuma mai da ita kango har abada.
13 Je ferai venir sur ce pays toutes les paroles que j'ai prononcées contre lui, tout ce qui est écrit dans ce livre, et que Jérémie a prophétisé contre toutes les nations.
Zan kawo wa wannan ƙasa dukan abubuwan na yi magana a kanta, dukan abubuwan da aka rubuta a wannan littafi, abubuwan da Irmiya kuma ya yi annabci a kan dukan al’ummai.
14 Car beaucoup de nations et de grands rois en feront des esclaves, même d'eux. Je leur rendrai selon leurs actes et selon l'œuvre de leurs mains. »
Su kansu al’ummai da sarakuna masu yawa za su bautar da su; zan sāka musu bisa ga ayyukansu da aikin hannuwansu.”
15 Car Yahvé, le Dieu d'Israël, me dit: « Prends de ma main cette coupe du vin de la colère, et fais-la boire à toutes les nations vers lesquelles je t'envoie.
Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya faɗa mini, “Ka karɓi kwaf ruwan inabin nan na fushina a wurina, ka sa dukan al’umman da na aike ka gare su, su sha.
16 Ils boiront, ils tituberont et seront fous, à cause de l'épée que j'enverrai au milieu d'eux. »
Sa’ad da suka sha, za su yi ta tangaɗi su kuma yi hauka saboda takobin da zan aika a cikinsu.”
17 Puis j'ai pris la coupe dans la main de Yahvé, et j'ai fait boire toutes les nations vers lesquelles Yahvé m'avait envoyé:
Saboda haka na karɓi kwaf daga hannun Ubangiji na sa dukan al’ummai waɗanda ya aiko ni wurinsu su sha.
18 Jérusalem et les villes de Juda, avec ses rois et ses chefs, pour en faire une désolation, un objet d'étonnement, de sifflement et de malédiction, comme il en existe aujourd'hui;
Urushalima da garuruwan Yahuda, sarakunan da fadawanta, don su mai da su kufai da kuma abin bantsoro da ba’a da la’ana, yadda suke a yau;
19 Pharaon, roi d'Égypte, avec ses serviteurs, ses chefs, et tout son peuple;
Fir’auna sarkin Masar, ma’aikatansa, fadawansa da dukan mutanensa,
20 tout le peuple mélangé, tous les rois du pays d'Uz, tous les rois des Philistins, Askalon, Gaza, Ékron, et le reste d'Asdod;
da dukan baƙin da suke can; dukan sarakunan Uz; dukan sarakunan Filistiyawa (waɗannan na Ashkelon, Gaza, Ekron da mutanen da aka bari a Ashdod);
21 Édom, Moab, et les enfants d'Ammon;
Edom, Mowab da Ammon;
22 tous les rois de Tyr, tous les rois de Sidon, et les rois de l'île qui est au delà de la mer;
dukan sarakunan Taya da Sidon; sarakunan bakin teku a ƙetaren teku;
23 Dedan, Tema, Buz, et tous ceux qui ont les coins de leur barbe coupés;
Dedan, Tema, Buz da dukan waɗanda suke a manisantan wurare;
24 tous les rois d'Arabie, tous les rois du peuple mélangé qui habite dans le désert;
dukan sarakunan Arabiya da dukan sarakunan baƙin da suke zama a hamada;
25 tous les rois de Zimri, tous les rois d'Élam, tous les rois des Mèdes,
dukan sarakunan Zimri, Elam da Mediya;
26 tous les rois du nord, les uns avec les autres, de loin et de près, et tous les royaumes du monde, qui sont à la surface de la terre. Le roi de Sheshach boira après eux.
da kuma dukan sarakunan arewa, nesa da kuma kusa, bi da bi, dukan mulkokin duniya. Bayan dukansu kuma, sai sarkin Sheshak ma yă sha.
27 Tu leur diras: « L'Éternel des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Buvez et soyez ivres, vomissez, tombez et ne vous relevez plus, à cause de l'épée que j'enverrai au milieu de vous ».
“Sa’an nan na faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ku sha, ku bugu ku kuma yi amai, ku fāɗi, kada kuma ku ƙara tashi saboda takobin da zan aiko muku.’
28 S'ils refusent de prendre la coupe dans ta main pour boire, tu leur diras: « L'Éternel des armées dit: « Vous boirez ».
Amma in suka ki su karɓi kwaf ɗin daga hannunka su sha, ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa dole ku sha!
29 Car voici que je commence à faire du mal à la ville qui s'appelle de mon nom. Vous ne resterez pas impunis, car j'appellerai l'épée sur tous les habitants de la terre, dit Yahvé des armées ».
Ga shi, na sa masifa tă yi aiki cikin birnin da ake kira da sunana, kuna gani za ku tafi ba hukunci? Ba za ku tafi ba hukunci ba, gama ina kawo wa dukan mazaunan duniya takobi, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
30 « Prophétise donc contre eux toutes ces paroles, et dis-leur, "'Yahvé rugira du haut des cieux, et faire entendre sa voix depuis sa demeure sainte. Il rugira puissamment contre son pli. Il poussera un cri, comme ceux qui foulent le raisin, contre tous les habitants de la terre.
“Yanzu ka yi annabcin dukan waɗannan maganganu a kansu ka kuma ce musu, “‘Ubangiji zai yi ruri daga bisa; zai yi tsawa daga mazauninsa mai tsarki ya kuma yi ruri da ƙarfi a kan ƙasarsa. Zai yi ihu kamar waɗanda suke matsin’ya’yan inabi, yi ihu a kan dukan waɗanda suke zaune a duniya.
31 Un bruit se fera entendre jusqu'à l'extrémité de la terre; car Yahvé a une controverse avec les nations. Il entrera en jugement avec toute chair. Quant aux méchants, il les livrera à l'épée, dit Yahvé. »
Hayaniya za tă taso har iyakar duniya, gama Ubangiji zai kawo tuhume-tuhume a kan al’ummai; zai kawo shari’a a kan dukan’yan adam ya kuma kashe mugaye da takobi,’” in ji Ubangiji.
32 Yahvé des Armées dit, « Voici que le mal se répandra de nation en nation, et une grande tempête s'élèvera des extrémités de la terre. »
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Duba! Masifa tana yaɗuwa daga al’umma zuwa al’umma; hadari mai girma yana tasowa daga iyakar duniya.”
33 En ce jour-là, les morts de Yahvé seront d'un bout à l'autre de la terre. On ne les pleurera pas. Ils ne seront ni recueillis ni enterrés. Ils seront du fumier à la surface de la terre.
A lokacin waɗanda Ubangiji ya kashe za su kasance a ko’ina, daga wannan bangon duniya zuwa wancan. Ba za a yi kuka dominsu, ba za a tattara su don a binne ba, amma za su zama kamar juji da an tsiba a ƙasa.
34 Gémissez, bergers, et criez. Va te vautrer dans la poussière, toi le chef du troupeau; car les jours de vos massacres et de vos dispersions sont arrivés, et vous tomberez comme une fine poterie.
Ku yi kuka ku kuma yi makoki, ku makiyaya; ku yi ta birgima a ƙura, ku shugabannin garke. Gama lokacin da za a yanka ku ya zo; za ku fāɗi ku kuma farfasa kamar tukunyar yumɓu mai kyau.
35 Les bergers n'auront aucun moyen de fuir. Le chef du troupeau n'aura pas d'échappatoire.
Makiyaya ba za su sami wurin da za su gudu su tafi ba, shugabannin garke ba za su sami wurin kuɓuta ba.
36 Une voix du cri des bergers, et les lamentations du chef du troupeau, car Yahvé détruit leurs pâturages.
Ji kukan makiyaya, kururuwan shugabannin garke, gama Ubangiji yana hallaka wurin kiwo.
37 Les plis paisibles sont réduits au silence à cause de l'ardente colère de Yahvé.
Rafi mai gudu a hankali zai zama kango saboda zafin fushin Ubangiji.
38 Il a quitté sa cachette, comme le lion; car leur pays est devenu un objet d'étonnement à cause de la férocité de l'oppression, et à cause de sa colère féroce.
Kamar zaki zai bar wurin ɓuyarsa, ƙasarsu kuma za tă zama kufai saboda takobin masu danniya da kuma saboda zafin fushin Ubangiji.

< Jérémie 25 >