< Isaïe 7 >

1 Du temps d'Achaz, fils de Jotham, fils d'Ozias, roi de Juda, Retsin, roi de Syrie, et Pékah, fils de Remalia, roi d'Israël, montèrent à Jérusalem pour lui faire la guerre, mais ils ne purent l'emporter.
Sa’ad da Ahaz ɗan Yotam, ɗan Uzziya, yake sarkin Yahuda, Sarki Rezin na Aram da Feka ɗan Remaliya sarkin Isra’ila suka haura don su yaƙi Urushalima, amma ba su iya cinta da yaƙi ba.
2 On dit à la maison de David: « La Syrie est alliée à Ephraïm. » Son cœur trembla, et le cœur de son peuple, comme les arbres de la forêt tremblent sous l'effet du vent.
Sai fa aka faɗa wa gidan Dawuda cewa, “Aram ya haɗa kansa da Efraim”; saboda haka zuciyar Ahaz da ta mutanensa suka firgita, sai ka ce itatuwa a kurmin da iska ta girgiza.
3 Et Yahvé dit à Ésaïe: « Va à la rencontre d'Achaz, toi et Shearjashub, ton fils, à l'extrémité du conduit de l'étang supérieur, sur la route du champ du foulon.
Sai Ubangiji ya ce wa Ishaya, “Fita, kai da ɗanka Sheyar-Yashub, don ku sadu da Ahaz a ƙarshen wuriyar da take kawo ruwa daga Tafkin Tudu, a hanyar Filin Mai Wanki.
4 Tu lui diras: « Prends garde et reste calme. N'aie pas peur, et que ton cœur ne s'affaiblisse pas à cause de ces deux queues de torches fumantes, à cause de la colère ardente de Retsin et de la Syrie, et du fils de Remalia.
Ka faɗa masa, ‘Ka yi hankali, ka natsu kada kuma ka ji tsoro ko ka damu, kada ka ji tsoron fushin sarki Rezin da na Aram da na ɗan Remaliya, ba wani abu mai hatsari ba ne, bai fi hayaƙin’yan ƙirare biyu da suke cin wuta ba.
5 Car la Syrie, Éphraïm et le fils de Remalia ont comploté contre toi, en disant:
Aram, Efraim da ɗan Remaliya sun ƙulla maƙarƙashiya, suna cewa,
6 « Montons contre Juda, et déchirons-le, et partageons-le entre nous, et établissons-y un roi, le fils de Tabeel. »
“Bari mu kai wa Yahuda hari; bari mu yayyage su mu rarraba su a tsakaninmu, mu naɗa Tabeyel sarki a kansu.”
7 Voici ce que dit le Seigneur Yahvé: « Cela ne tiendra pas, cela n'arrivera pas. »
Duk da haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “‘Ba zai faru ba, ba zai auku ba,
8 Car le chef de la Syrie est Damas, et le chef de Damas est Rezin. Dans l'espace de soixante-cinq ans, Éphraïm sera brisé en morceaux, de sorte qu'il ne sera plus un peuple.
gama kan Aram shi ne Damaskus, kan Damaskus kuma kawai shi ne Rezin. Cikin shekaru sittin da biyar za a wargaje Efraim har ba za tă iya rayuwa ta zama al’umma ba.
9 Le chef d'Éphraïm, c'est Samarie, et le chef de Samarie, c'est le fils de Remalia. Si vous ne voulez pas croire, vous ne serez pas établis.'"
Kan Efraim shi ne Samariya, kan Samariya kuma kawai shi ne ɗan Remaliya. In ba ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiyarku ba, ba za ku dawwama ba.’”
10 Yahvé parla de nouveau à Achaz et dit:
Ubangiji ya kuma yi magana wa Ahaz ya ce,
11 « Demande un signe à Yahvé ton Dieu; demande-le soit dans la profondeur, soit dans la hauteur. » (Sheol h7585)
“Ka roƙi Ubangiji Allahnka yă ba ka alama, ko daga zurfafa masu zurfi ko kuwa daga can cikin sama.” (Sheol h7585)
12 Mais Achaz dit: « Je ne demanderai rien. Je ne tenterai pas Yahvé. »
Amma Ahaz ya ce, “Ba zan nema ba; ba zan gwada Ubangiji ba.”
13 Il dit: « Écoutez maintenant, maison de David. N'est-ce pas assez pour vous d'éprouver la patience des hommes, que vous éprouviez aussi la patience de mon Dieu?
Sa’an nan Ishaya ya ce, “To, ku saurara, ya ku gidan Dawuda! Abin kirki kuke yi ne da kuka ƙure haƙurin jama’a? Ko haƙurin Allah ne kuma kuke so ku ƙure?
14 C'est pourquoi le Seigneur lui-même vous donnera un signe. Voici que la vierge concevra et enfantera un fils, et elle lui donnera le nom d'Emmanuel.
Saboda haka Ubangiji kansa zai ba ku alama. Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, za tă kuwa kira shi Immanuwel.
15 Il mangera du beurre et du miel, quand il saura refuser le mal et choisir le bien.
In ya yi girma har ya isa yanke shawara don kansa, madara da zuma ne abincinsa.
16 Car avant que l'enfant sache refuser le mal et choisir le bien, le pays dont vous avez les deux rois en horreur sera abandonné.
Amma kafin yaron yă isa yanke shawara yă ƙi abin da yake mummuna, yă zaɓi abin da yake nagari, ƙasashen sarakunan nan biyu da kuke tsoro za su zama kango.
17 Yahvé fera venir sur toi, sur ton peuple et sur la maison de ton père des jours qui ne sont pas venus, depuis le jour où Éphraïm s'est séparé de Juda, jusqu'au roi d'Assyrie.
Ubangiji zai aukar maka da kwanakin wahala, kai da jama’arka, da dukan iyalin gidan sarauta, waɗanda suka fi muni tun lokacin da aka raba mulkin Efraim daga na Yahuda, zai kawo sarkin Assuriya.”
18 En ce jour-là, l'Éternel sifflera pour la mouche qui est à l'extrémité des fleuves d'Égypte, et pour l'abeille qui est au pays d'Assyrie.
A wannan rana Ubangiji zai yi feɗuwa yă kira ƙudaje daga rafuffuka masu nisa na Masar da kuma ƙudan zuma daga ƙasar Assuriya.
19 Elles viendront et se reposeront toutes dans les vallées désolées, dans les fentes des rochers, sur toutes les haies d'épines et sur tous les pâturages.
Za su zo su mamaye kwazazzabai da kogwanni cikin duwatsu, a kan dukan ƙayayyuwa da dukan rammukan ruwa.
20 En ce jour-là, l'Éternel rasera avec un rasoir loué dans les régions situées au-delà du fleuve, avec le roi d'Assyrie, la tête et le poil des pieds, et il consumera aussi la barbe.
A wannan rana Ubangiji zai yi amfani da rezan da aka yi haya daga ƙetaren Kogi, sarkin Assuriya ke nan, yă aske kanku da gashin ƙafafunku, zai kuma aske gemunku.
21 Il arrivera en ce jour-là qu'un homme gardera en vie une jeune vache et deux brebis.
A ranar, mutum zai bar karsana ɗaya da awaki biyu da rai.
22 Il arrivera qu'à cause de l'abondance du lait qu'elles donneront, il mangera du beurre, car tout le monde mangera du beurre et du miel qui restera dans le pays.
Kuma saboda yalwa madarar da suke bayarwa, zai kasance da madarar da zai sha. Dukan waɗanda suka rage a ƙasar za su sha madara da zuma.
23 Il arrivera en ce jour-là que tout endroit où il y avait mille vignes valant mille sicles d'argent, sera pour des ronces et des épines.
A wannan rana, a kowane wuri inda akwai kuringa dubu da kuɗinsu ya kai shekel dubu na azurfa, ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne kawai za su kasance a can.
24 On s'y rendra avec des flèches et avec l'arc, car tout le pays ne sera que ronces et épines.
Mutane za su je can da baka da kibiyoyi, gama ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya ne za su rufe ƙasar.
25 Toutes les collines qui ont été cultivées à la houe, vous n'y viendrez pas par crainte des ronces et des épines; mais on y enverra des bœufs et on y piétinera des moutons. »
Game da dukan tuddai da dā ake nome da garemani kuwa, ba za ku ƙara je wurin ba saboda tsoron ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiya; za su zama wuraren da ake kai shanu a sake su su yi ta yawo da kansu, tumaki kuma su yi ta gudu.

< Isaïe 7 >