< Isaïe 6 >

1 L'année de la mort du roi Ozias, je vis le Seigneur assis sur un trône, haut et élevé, et sa traîne remplissait le temple.
A shekarar da Sarki Uzziya ya mutu, na ga Ubangiji zaune a kan kujerar sarauta a sama cike da ɗaukaka, zatinsa ya cika haikali.
2 Au-dessus de lui se tenaient les séraphins. Chacun d'eux avait six ailes. De deux ailes, il se couvrait le visage. De deux, il se couvrait les pieds. De deux ailes, il volait.
A bisansa akwai serafofi, kowanne yana da fikafikai shida. Fikafikai biyu sun rufe fuskokinsu, da biyu suka rufe ƙafafunsu, biyu kuma da su suke tashi.
3 L`un d`eux appela l`autre, et dit, « Saint, saint, saint, Yahvé des armées! La terre entière est remplie de sa gloire! »
Suna kiran juna, “Mai Tsarki, Mai Tsarki, Mai Tsarki! Ubangiji Maɗaukaki ne; duniya ta cika da ɗaukakarsa.”
4 Les fondements des seuils ont tremblé à la voix de celui qui appelait, et la maison s'est remplie de fumée.
Da jin ƙarar muryoyinsu madogarai da madogaran ƙofa suka girgiza, haikali kuma ya cika da hayaƙi.
5 Alors je dis: « Malheur à moi! Car je suis perdu, parce que je suis un homme aux lèvres impures et que j'habite au milieu d'un peuple aux lèvres impures, car mes yeux ont vu le Roi, Yahvé des Armées! »
Sai na tā da murya na ce, “Kaitona! Na shiga uku! Gama ni mutum ne mai leɓuna marar tsarki, kuma ina raye a cikin mutane masu leɓuna marasa tsarki, idanuna kuma sun ga Sarki, Ubangiji Maɗaukaki.”
6 Et l'un des séraphins vola vers moi, tenant à la main un charbon vivant qu'il avait pris sur l'autel avec les pinces.
Sai ɗaya daga cikin serafofin ya yi firiya zuwa wurina tare da garwashi mai wuta a hannunsa, wanda ya ɗiba da arautaki daga bagade.
7 Il en toucha ma bouche, et dit: « Voici, ceci a touché tes lèvres; ton iniquité est effacée, et ton péché est pardonné. »
Da shi ne ya taɓa bakina ya ce, “Duba, wannan ya taɓa leɓunanka, yanzu fa an kawar da laifofinka, an kuma gafarta maka zunubanka.”
8 J'ai entendu la voix du Seigneur, qui disait: « Qui enverrai-je et qui ira pour nous? » Alors j'ai dit: « Me voici. Envoyez-moi! »
Sa’an nan na ji muryar Ubangiji tana cewa, “Wa zan aika? Wa zai tafi mana?” Sai na ce, “Ga ni! Ka aike ni!”
9 Il dit: « Va, et dis à ce peuple, Vous entendez en effet, mais ne comprennent pas. Vous voyez en effet, mais ne perçoivent pas.
Ya ce, “Je ka ka faɗa wa wannan mutane, “‘Kome yawan kasa kunne da za ku yi, ba za ku fahimta ba; Kome yawan dubar da za ku yi, ba za ku san abin da yake faruwa ba.’
10 Rends gras le cœur de ce peuple. Rendez leurs oreilles lourdes, et fermez leurs yeux; de peur qu'ils ne voient avec leurs yeux, entendent avec leurs oreilles, comprennent avec leur cœur, et retournez-vous, et soyez guéri. »
Ka sa zuciyar mutanen nan ta dushe; kunnuwansu su kurunce, idanunsu kuma su makance. In ba haka ba za su iya gani da idanunsu, su ji da kunnuwansu, su fahimta da zuciyarsu, su kuma juyo a kuma warkar da su.”
11 Alors j'ai dit: « Seigneur, combien de temps? » Il a répondu, « Jusqu'à ce que les villes soient des déchets sans habitant, des maisons sans homme, la terre devient complètement désolée,
Sa’an nan na ce, “Har yaushe, ya Ubangiji?” Ya kuma amsa, “Sai an lalatar da biranen ba kowa a ciki, sai an mai da gidaje kangwaye ƙasa kuma ta zama kango ba amfani,
12 et Yahvé a éloigné les hommes, et les lieux abandonnés sont nombreux dans le pays.
sai lokacin da Ubangiji ya kori kowa aka kuma yashe ƙasar gaba ɗaya.
13 S'il lui reste un dixième, qui seront également consommés à leur tour, comme un térébinthe, et comme un chêne dont il reste la souche lorsqu'ils sont abattus, alors la semence sainte est sa souche. »
Ko da yake kashi ɗaya bisa goma zai ragu a ƙasar, za tă sāke zama kango. Amma kamar yadda katambiri da itacen oak sukan bar kututturai sa’ad da aka yanke su, haka iri mai tsarkin nan zai zama kututture a ƙasar mai tsarki.”

< Isaïe 6 >