< Isaïe 60 >

1 « Lève-toi, brille, car ta lumière est venue, et la gloire de Yahvé s'est levée sur vous!
“Ki tashi, ki haskaka, gama haskenki ya zo, ɗaukakar Ubangiji ya taso a kanki.
2 Car voici, les ténèbres couvriront la terre, et d'épaisses ténèbres les peuples; mais Yahvé se lèvera sur vous, et sa gloire sera vue sur vous.
Duba, duhu ya rufe duniya duhu mai kauri kuma yana bisa mutane, amma Ubangiji ya taso a kanki ɗaukakarsa kuma ya bayyana a bisanki.
3 Les nations viendront à ta lumière, et les rois à l'éclat de ton lever.
Al’ummai za su zo wurin haskenki, sarakuna kuma zuwa asubahin sabon yininki.
4 « Lève tes yeux tout autour, et regarde: ils se rassemblent tous. Ils viennent à vous. Vos fils viendront de loin, et vos filles seront portées dans les bras.
“Ki ɗaga idanunki ki duba kewaye da ke. Duka sun tattaru suka kuma zo wurinki;’ya’yanki maza daga nesa, ana kuma ɗaukan’ya’yanki mata a hannu.
5 Alors tu verras et tu seras rayonnant, et votre cœur palpitera et s'élargira; car l'abondance de la mer se tournera vers vous. La richesse des nations viendra à toi.
Sa’an nan za ki duba ki kuma haskaka zuciyarki zai motsa ya kuma cika da farin ciki; za a kawo miki wadata daga tekuna, za a kawo miki arzikin al’ummai.
6 Une multitude de chameaux te couvriront, les dromadaires de Midian et d'Epha. Tous ceux de Saba viendront. Ils apporteront de l'or et de l'encens, et proclameront les louanges de Yahvé.
Manyan ayarin raƙuma za su cika ƙasar, ƙananan raƙuma ke nan daga Midiyan da Efa. Daga Sheba kuma duka za su zo, suna ɗauke da zinariya da turare suna shelar yabon Ubangiji.
7 Tous les troupeaux de Kédar seront rassemblés auprès de toi. Les béliers de Nebaioth te serviront. Ils seront acceptés comme offrandes sur mon autel; et j'embellirai ma glorieuse maison.
Dukan garkunan Kedar za su taru a wurinki ragunan Nebayiwot za su yi miki hidima; za a karɓe su kamar hadayu a kan bagadenki, zan kuma darjanta haikalina mai ɗaukaka.
8 « Qui sont ceux qui volent comme une nuée? et comme les colombes à leurs fenêtres?
“Su wane ne waɗannan da suke firiya kamar gizagizai, kamar kurciyoyi suna zuwa sheƙarsu?
9 Les îles m'attendent, et les navires de Tarsis en premier, pour faire venir vos fils de loin, leur argent et leur or avec eux, au nom de Yahvé ton Dieu, et pour le Saint d'Israël, parce qu'il vous a glorifié.
Babu shakka tsibirai suna dogara gare ni; jiragen Tarshish kuma su ne a gaba, suna kawo’ya’yanki maza daga nesa, tare da azurfa da zinariya, domin su girmama Ubangiji Allahnki, Mai Tsarkin nan na Isra’ila, gama ya cika ki da daraja.
10 « Les étrangers bâtiront vos murs, et leurs rois te serviront; car dans ma colère, je t'ai frappé, mais en ma faveur, j'ai eu pitié de toi.
“Baƙi za su sāke gina katangarki, sarakunansu kuma za su yi miki hidima. Ko da yake a cikin fushi na buge ki, da tagomashi zan yi miki jinƙai.
11 Tes portes seront toujours ouvertes, elles ne se fermeront ni jour ni nuit, afin qu'on t'apporte les richesses des nations et qu'on emmène leurs rois en captivité.
Ƙofofinki kullum za su kasance a buɗe, ba za a ƙara rufe su da rana ko da dare ba, saboda mutane su kawo miki dukiyar al’ummai, sarakunansu za su kasance a gaba a jerin gwanon nasara.
12 Car la nation et le royaume qui ne te serviront pas périront; oui, ces nations seront anéanties.
Gama al’umma ko masarautar da ba tă bauta miki ba, za tă hallaka; za tă lalace sarai.
13 « La gloire du Liban viendra à toi, le cyprès, le pin et le buis réunis, pour embellir le lieu de mon sanctuaire, et je rendrai glorieux le lieu de mes pieds.
“Darajar Lebanon za tă zo wurinki, itatuwan fir da dai ire-irensu da kuma itatuwan saifires duka za su zo don su ƙayatar da wurina mai tsarki; zan kuma ɗaukaka wurin ƙafafuna.
14 Les fils de ceux qui t'ont affligé viendront se prosterner devant toi; et tous ceux qui te méprisaient se prosterneront sous la plante de tes pieds. Ils t'appelleront la Cité de Yahvé, la Sion du Saint d'Israël.
’Ya’ya maza masu zaluntarku za su zo suna rusunawa a gabanki; dukan waɗanda suka rena ki za su rusuna a ƙafafunki su kuma ce da ke Birnin Ubangiji, Sihiyona na Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
15 « Alors que vous avez été abandonnés et haïs, pour que personne ne passe à travers toi, Je ferai de vous une excellence éternelle, une joie pour de nombreuses générations.
“Ko da yake an yashe ki aka kuma ƙi ki, har babu wani da ya ratsa a cikinki, zan mai da ke madawwamiyar abar taƙama da kuma farin cikin dukan zamanai.
16 Vous boirez aussi le lait des nations, et nourrira des seins royaux. Alors vous saurez que moi, Yahvé, je suis votre Sauveur, votre Rédempteur, le Puissant de Jacob.
Za ki sha madarar al’ummai a kuma shayar da ke da nonon sarauta. Sa’an nan za ki san cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Mai Ikon nan na Yaƙub.
17 Pour le bronze, j'apporterai de l'or; pour le fer, j'apporterai de l'argent; pour le bois, le bronze, et pour les pierres, du fer. Je ferai aussi de la paix votre gouverneur, et la droiture votre chef.
A maimakon tagulla zan kawo zinariya, azurfa kuma a maimakon baƙin ƙarfe. A maimakon katako zan kawo tagulla, baƙin ƙarfe kuma a maimakon duwatsu. Zan sa salama ta zama gwamnarki adalci kuma mai mulkinki.
18 On n'entendra plus parler de violence dans votre pays, ni désolation ni destruction dans tes frontières; mais vous appellerez vos murs le Salut, et tes portes Louanges.
Ba za a ƙara jin hayaniyar tashin hankali a ƙasarki ba, balle lalacewa ko hallaka a cikin iyakokinki, amma za ki kira katangarki Ceto ƙofofinki kuma Yabo.
19 Le soleil ne sera plus ta lumière le jour, et l'éclat de la lune ne vous éclairera pas non plus, mais Yahvé sera votre lumière éternelle, et ton Dieu sera ta gloire.
Rana ba za tă ƙara zama haskenki a yini ba, balle hasken wata ya haskaka a kanki, gama Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, Allahnki kuma zai zama ɗaukakarki.
20 Votre soleil ne se couchera plus, et votre lune ne se retirera pas non plus; car Yahvé sera votre lumière éternelle, et les jours de ton deuil prendront fin.
Ranarki ba za tă ƙara fāɗuwa ba watanki kuma ba zai ƙara shuɗewa ba; Ubangiji zai zama madawwamin haskenki, kwanakin baƙin cikinki za su ƙare.
21 Alors ton peuple sera tout à fait juste. Ils hériteront de la terre pour toujours, la branche de ma plantation, le travail de mes mains, afin que je sois glorifié.
Sa’an nan dukan mutanenki za su zama masu adalci za su kuma mallaki ƙasar har abada. Su ne reshen da na shuka, aikin hannuwana, don nuna darajata.
22 Le petit deviendra un millier, et la petite, une nation forte. Moi, Yahvé, je ferai cela rapidement en son temps. »
Mafi ƙanƙanta a cikinki za tă zama dubu, ƙarami zai zama al’umma mai girma. Ni ne Ubangiji, cikin lokacinsa zan yi haka da sauri.”

< Isaïe 60 >