< Jérémie 1 >

1 Paroles de Jérémie, fils de Hilkija, l'un des prêtres qui étaient à Anathoth, dans le pays de Benjamin.
Kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistoci a Anatot a yankin Benyamin.
2 La parole de Yahvé lui fut adressée au temps de Josias, fils d'Amon, roi de Juda, la treizième année de son règne.
Maganar Ubangiji ta zo gare shi a shekara ta goma sha uku ta sarautar Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda,
3 Elle arriva aussi aux jours de Jojakim, fils de Josias, roi de Juda, à la fin de la onzième année de Sédécias, fils de Josias, roi de Juda, jusqu'à la déportation de Jérusalem au cinquième mois.
da kuma a zamanin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, har zuwa watan biyar na shekara goma sha ɗaya na Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sa’ad da aka kai mutanen Urushalima zaman bauta.
4 Or la parole de Yahvé me fut adressée, en ces termes,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
5 « Avant de te former dans le ventre de ta mère, je te connaissais. Avant ta naissance, je t'ai sanctifié. Je t'ai établi prophète des nations. »
“Kafin in siffanta ka a cikin ciki na san ka, kafin a haife ka, na keɓe ka; na naɗa ka ka zama annabi ga al’ummai.”
6 Et je dis: « Ah! Seigneur Yahvé! Voici, je ne sais pas comment parler, car je suis un enfant. »
Sai na ce, “Kayya, Ubangiji Mai Iko Duka, ban iya magana ba; ni ɗan yaro ne kawai.”
7 Mais Yahvé me dit: « Ne dis pas: « Je suis un enfant », car tu iras vers celui que je t'enverrai, et tu diras tout ce que je te commanderai.
Amma Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ce, ‘Ni ɗan yaro ne kawai.’ Dole ka je wurin kowane mutumin da na aike ka ka kuma faɗa abin da na umarce ka.
8 N'aie pas peur à cause d'eux, car je suis avec toi pour te sauver, dit l'Éternel.
Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da kai kuma zan kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
9 Alors Yahvé étendit sa main et toucha ma bouche. Et Yahvé me dit: « Voici, j'ai mis mes paroles dans ta bouche.
Sai Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina ya ce mini, “Yanzu na sa kalmomina a bakinka.
10 Voici, je t'ai établi aujourd'hui sur les nations et sur les royaumes, pour arracher et démolir, pour détruire et renverser, pour bâtir et planter. »
Duba, yau na naɗa ka a kan al’ummai da mulkoki don ka tumɓuke ka kuma rusar, ka hallaka ka kuma kakkaɓe, ka gina ka kuma shuka.”
11 La parole de Yahvé me fut adressée en ces termes: « Jérémie, que vois-tu? » J'ai dit: « Je vois une branche d'amandier. »
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa, “Me ka gani, Irmiya?” Sai na amsa na ce, “Na ga reshen itacen almon.”
12 Et Yahvé me dit: « Tu as bien vu, car je veille sur ma parole pour l'accomplir. »
Ubangiji ya ce mini, “Daidai ne ka gani, gama ina lura in ga cewa maganata ta cika.”
13 La parole de Yahvé me fut adressée pour la seconde fois, en disant: « Que vois-tu? » J'ai dit: « Je vois un chaudron en ébullition, et il bascule vers le nord. »
Maganar Ubangiji ta sāke zo mini cewa, “Me ka gani?” Na amsa na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, tana juyewa daga arewa.”
14 Alors Yahvé me dit: « Du nord, le mal se répandra sur tous les habitants du pays.
Ubangiji ya ce mini, “Daga arewa za a zubo masifa a kan dukan mazaunan ƙasar.
15 Car voici, j'appellerai toutes les familles des royaumes du nord, dit l'Éternel. « Ils viendront, et ils placeront chacun leur trône à l'entrée des portes de Jérusalem, et contre toutes ses murailles tout autour, et contre toutes les villes de Juda.
Ina shirin kiran dukan mutanen masarautar arewanci,” in ji Ubangiji. “Sarakunansu za su zo su kafa kursiyoyinsu a mashigin ƙofofin Urushalima; za su zo su kewaye dukan katangarta su kewaye dukan garuruwan Yahuda.
16 Je prononcerai contre eux mes jugements sur toute leur méchanceté, en ce qu'ils m'ont abandonné, et ont brûlé de l'encens à d'autres dieux, et adoraient les œuvres de leurs propres mains.
Zan furta hukunci a kan mutanena saboda muguntarsu na yashe ni, suna ƙona turare ga waɗansu alloli suna kuma bauta wa abin da hannuwansu suka yi.
17 « Mets donc ta ceinture à ta taille, lève-toi, et dis-leur tout ce que je t'ordonne. Ne t'effraie pas devant eux, de peur que je ne t'effraie devant eux.
“Ka kintsa kanka! Ka tashi tsaye ka faɗa musu abin da na umarce ka. Kada su firgita ka, in ba haka ba zan firgita ka a gabansu.
18 Car voici, je fais de toi aujourd'hui une ville fortifiée, une colonne de fer et des murs de bronze contre tout le pays, contre les rois de Juda, contre ses princes, contre ses prêtres et contre le peuple du pays.
Yau na mai da kai birni mai katanga, ginshiƙin ƙarfe da bangon tagulla don ka tsaya gāba da dukan ƙasar, ya kuma yi gāba da sarakunan Yahuda da fadawan, da firistoci da kuma mutanenta.
19 Ils te combattront, mais ils ne te vaincront pas, car je suis avec toi, dit l'Éternel, pour te secourir. »
Za su yi yaƙi da kai amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, zan kuma kiyaye ka,” in ji Ubangiji.

< Jérémie 1 >