< Isaïe 13 >

1 Le fardeau de Babylone, que vit Ésaïe, fils d'Amoz.
Abubuwan da Allah ya yi magana a kai game da Babilon da Ishaya ɗan Amoz ya gani.
2 Dressez une bannière sur la montagne nue! Élève ta voix vers eux! Agite ta main, afin qu'ils entrent dans les portes des nobles.
A tā da tuta a kan tudun da yake mai fili, ka tā da murya gare su; ka ɗaga hannu ka ba su alama don su shiga ƙofofi masu alfarma.
3 J'ai donné des ordres à mes consacrés, J'ai appelé mes vaillants hommes pour ma colère, Même mes fiers exaltés.
Na umarci tsarkakana; na umarci jarumawan yaƙina su gamsar da fushina, waɗanda suke farin ciki a nasarata.
4 Le bruit d'une multitude est dans les montagnes, comme celui d'un grand peuple; le bruit d'un tumulte des royaumes des nations rassemblées! L'Éternel des armées rassemble l'armée pour la bataille.
Ka saurara, akwai surutu a kan duwatsu, sai ka ce na babban taron jama’a! Ka saurara, akwai hayaniya a cikin mulkoki, sai ka ce al’ummai ne suna ta tattaruwa! Ubangiji Maɗaukaki yana shirya mayaƙa don yaƙi.
5 Ils viennent d'un pays lointain, de l'extrémité des cieux, Yahvé, avec les armes de sa colère, pour détruire tout le pays.
Suna zuwa daga ƙasashe masu nesa, daga iyakokin duniya, Ubangiji da kuma fushinsa, zai hallaka dukan ƙasar.
6 Gémissez, car le jour de l'Éternel est proche! Il viendra comme une destruction de la part du Tout-Puissant.
Ku yi ihu, gama ranar Ubangiji ta yi kusa za tă zo kamar hallaka daga Maɗaukaki.
7 C'est pourquoi toutes les mains seront affaiblies, et le cœur de chacun se fondra.
Saboda wannan, hannun kowane mutum zai yi rauni, ƙarfin halin kowane mutum zai kāsa.
8 Ils seront consternés. Des angoisses et des douleurs les saisiront. Ils souffriront comme une femme en travail. Ils se regarderont avec étonnement les uns les autres. Leurs visages seront des visages de flamme.
Tsoro zai kama su, zafi da azaba za su ci ƙarfinsu; za su yi ta murɗewa kamar mace mai naƙuda. Za su dubi juna a tsorace, fuskokinsu a ɓace.
9 Voici, le jour de l'Éternel arrive, jour cruel, jour de colère et de fureur, pour réduire le pays en désert, et en exterminer les pécheurs.
Duba, ranar Ubangiji tana zuwa, muguwar rana, mai hasala da zafin fushi, don ta mai da ƙasar kango ta kuma hallakar da masu zunubi da suke cikinta.
10 Car les étoiles du ciel et ses constellations ne donneront plus leur lumière. Le soleil s'obscurcira en s'éteignant, et la lune ne fera pas briller sa lumière.
Taurarin sama da ƙungiyoyinsu ba za su ba da haskensu ba. Rana za tă yi duhu wata kuma ba zai ba da haskensa ba.
11 Je punirai le monde pour sa méchanceté, et les méchants pour leur iniquité. Je ferai cesser l'arrogance des orgueilleux, et j'humilierai l'arrogance des terribles.
Zan hukunta duniya saboda muguntarta, mugaye saboda zunubansu. Zan kawo ƙarshe ga girman kan masu taƙama in kuma ƙasƙantar da ɗaga kan marasa tausayi.
12 Je rendrai les hommes plus rares que l'or fin, les hommes plus rares que l'or pur d'Ophir.
Zan sa mutum yă fi zinariya zalla wuyar samuwa, fiye da zinariyar Ofir wuyan gani.
13 C'est pourquoi je ferai trembler les cieux, et la terre sera secouée de sa place, dans la colère de l'Éternel des armées et au jour de son ardente fureur.
Saboda haka zan sa sammai su yi rawar jiki; duniya kuma za tă girgiza daga inda take a fushin Ubangiji Maɗaukaki, a ranar fushinsa mai ƙuna.
14 Il arrivera que, comme une gazelle en chasse et comme des brebis que personne ne rassemble, ils se tourneront chacun vers son propre peuple, et fuiront chacun dans son pays.
Kamar barewar da ake farautarta kamar tumaki marasa makiyayi, haka nan kowane mutum zai koma ga mutanensa, kowane mutum zai gudu zuwa ƙasarsa.
15 Tous ceux qui seront trouvés seront transpercés. Tous ceux qui seront capturés tomberont par l'épée.
Duk wanda aka kama za a soke shi yă mutu; dukan waɗanda aka kama za su mutu ta takobi.
16 Leurs enfants aussi seront mis en pièces sous leurs yeux. Leurs maisons seront saccagées, et leurs femmes violées.
Za a fyaɗa’ya’yansu a ƙasa su yi kucu-kucu a idanunsu; za a washe gidajensu, a kuma kwana da matansu.
17 Voici, je vais exciter contre eux les Mèdes, qui n'apprécieront pas l'argent, et quant à l'or, ils n'y prendront pas plaisir.
Duba, zan zuga mutanen Medes su yi gāba da su, su da ba su kula da azurfa ba kuma ba sa damuwa da zinariya.
18 Leurs arcs mettront en pièces les jeunes gens, et ils n'auront pas pitié du fruit des entrailles. Leurs yeux n'épargneront pas les enfants.
Bakkunansu za su kashe samari; ba za su ji tausayin jarirai ba ba za su kuwa nuna jinƙai ga’yan yara ba.
19 Babylone, la gloire des royaumes, la beauté de l'orgueil des Chaldéens, sera comme lorsque Dieu renversa Sodome et Gomorrhe.
Babilon, kayan daraja na mulkoki, abin fariyar Babiloniyawa, Allah zai kaɓantar da ita kamar yadda ya yi da Sodom da Gomorra.
20 Elle ne sera jamais habitée, et on ne l'habitera pas de génération en génération. L'Arabe n'y dressera pas sa tente, et les bergers n'y feront pas reposer leurs troupeaux.
Ba za ƙara kasance da mazauna kuma ba ko a yi zama a cikinta dukan zamanai; Ba wani mutumin Arab da zai kafa tentinsa a can, ba makiyayin da zai taɓa kiwon garkensa a can.
21 Mais les bêtes sauvages du désert y coucheront, et leurs maisons seront remplies de chacals. Les autruches y habiteront, et les chèvres sauvages s'y ébattront.
Amma halittun hamada za su kwanta a can, diloli za su cika gidajenta; a can mujiyoyi za su zauna, a can kuma awakin jeji za su yi ta tsalle.
22 Les hyènes crieront dans leurs forteresses, et les chacals dans les palais agréables. Son temps est proche, et ses jours ne se prolongeront pas.
Kuraye za su yi ta kuka a kagarorinta, diloli kuma a cikin fadodinta masu alfarma. Lokacinta ya yi kusa, kwanakinta kuma ba za su yi tsawo ba.

< Isaïe 13 >