< Isaïe 12 >

1 En ce jour-là, tu diras: « Je te louerai, Yahvé, car tu t'es mis en colère contre moi, mais ta colère s'est détournée et tu m'as consolé.
A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
2 Voici, Dieu est mon salut. Je me confie, je ne crains rien, car Yahvé est ma force et mon chant, et il est mon salut ».
Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
3 C'est donc avec joie que vous puiserez de l'eau aux puits du salut.
Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
4 En ce jour-là, vous direz: « Rendez grâce à Yahvé! Invoquez son nom! Annoncez ses exploits parmi les peuples! Proclamez que son nom est exalté!
A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
5 Chantez à Yahvé, car il a fait des choses excellentes! Qu'on le sache par toute la terre!
Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
6 Criez à haute voix et poussez des cris, habitants de Sion, car le Saint d'Israël est grand au milieu de vous! »
Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”

< Isaïe 12 >