< Ézéchiel 3 >

1 Il me dit: « Fils d'homme, mange ce que tu trouves. Mange ce rouleau, et va, parle à la maison d'Israël. »
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ci abin da yake a gabanka, ka ci wannan littafi; sa’an nan ka tafi ka yi magana wa gidan Isra’ila.”
2 Et j'ai ouvert la bouche, et il m'a fait manger le rouleau.
Saboda haka na buɗe bakina, ya kuma ba ni littafin in ci.
3 Il me dit: « Fils d'homme, mange ce rouleau que je te donne et remplis-en ton ventre et tes entrailles. » Puis je l'ai mangé. C'était aussi doux que du miel dans ma bouche.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ci wannan littafin da nake ba ka, ka kuma cika cikinka da shi.” Sai na ci shi, ya kuma yi zaki kamar zuma a bakina.
4 Il me dit: « Fils d'homme, va vers la maison d'Israël, et dis-leur mes paroles.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka tafi gidan Isra’ila ka faɗa kalmomina gare su.
5 Car ce n'est pas à un peuple au langage étranger et à la langue difficile que tu es envoyé, mais à la maison d'Israël -
Ba ina aikan ka wurin mutanen da suke da baƙon harshe da kuma yare mai wuya ba ne, amma zuwa ga gidan Isra’ila ne,
6 et non à de nombreux peuples au langage étranger et à la langue difficile, dont tu ne comprends pas les paroles. Certes, si je t'envoyais vers eux, ils t'écouteraient.
ba ga mutane da yawa na baƙon harshe da yare mai wuya, waɗanda ba ka san kalmominsu ba. Tabbatacce da na aike ka wurin irinsu, da sun saurare ka.
7 Mais la maison d'Israël ne t'écoutera pas, car elle ne m'écoutera pas, car toute la maison d'Israël est obstinée et dure de cœur.
Amma gidan Isra’ila ba sa niyya su saurare ka domin ba sa niyya su saurare ni, gama dukan gidan Isra’ila sun taurare suna kuma kin ji.
8 Voici, j'ai rendu ta face dure contre leurs faces, et ton front dur contre leurs fronts.
Amma zan sa ka zama mai taurinkai da taurin zuciya kamar su.
9 J'ai rendu ton front comme un diamant, plus dur que le silex. Ne les crains pas et ne t'effraie pas de leurs regards, bien qu'ils soient une maison rebelle. »
Zan sa goshinka ya zama da tauri kamar dutse, da tauri fiye da dutsen ƙanƙara ƙarfi. Kada ka ji tsoronsu ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.”
10 Il me dit encore: « Fils d'homme, reçois dans ton cœur et écoute de tes oreilles toutes les paroles que je te dis.
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ji da kyau ka kuma lura da dukan kalmomin da nake maka magana.
11 Va vers les captifs, vers les enfants de ton peuple, et parle-leur, et dis-leur: 'Voici ce que dit le Seigneur Yahvé'; ils écouteront ou ils refuseront. »
Ka tafi yanzu zuwa ga’yan’uwanka waɗanda suke zaman bauta ka yi musu magana. Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa,’ ko ku ji, ko kada ku ji.”
12 Alors l'Esprit me souleva, et j'entendis derrière moi la voix d'un grand tumulte: « Bénie soit la gloire de Yahvé du haut de son lieu! »
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama, a bayana na ji wata karar babban motsi na cewa, Bari a yabi ɗaukakar Ubangiji a wurin zamansa!
13 J'entendis le bruit des ailes des êtres vivants qui se touchaient, et le bruit des roues à côté d'eux, le bruit d'un grand tumulte.
Karar fikafikan rayayyun halittun nan ne suke goge junansu da kuma karar da’irorin nan da suke kusa da su, ƙarar babban motsi.
14 Et l'Esprit me souleva et m'emporta; et je m'en allai dans l'amertume, dans la chaleur de mon esprit; et la main de l'Éternel était forte sur moi.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma tafi da ni, na kuwa tafi da ɓacin rai da kuma fushin ruhuna, tare da hannu mai ƙarfi na Ubangiji a bisa na.
15 Puis j'arrivai auprès des captifs de Tel-Aviv, qui habitaient près du fleuve Kebar, et au lieu où ils habitaient; et je restai là, accablé, au milieu d'eux, pendant sept jours.
Na zo wurin masu zaman bautan da suke zama a Tel Abib kusa da Kogin Kebar, A can kuwa, inda suke zama, na zauna a cikinsu kwana bakwai, ina mamaki.
16 Au bout de sept jours, la parole de Yahvé me fut adressée, en ces termes:
A ƙarshen kwana bakwai ɗin maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
17 « Fils d'homme, je t'ai établi comme sentinelle de la maison d'Israël. Écoute donc la parole de ma bouche, et avertis-les de ma part.
“Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro don gidan Isra’ila; saboda haka ka ji maganar da zan yi ka kuma yi musu kashedin nan da ya fito daga gare ni.
18 Si je dis au méchant: « Tu mourras », et que tu ne l'avertisses pas, et que tu ne parles pas pour détourner le méchant de sa mauvaise voie, pour lui sauver la vie, ce méchant mourra dans son iniquité, et je réclamerai son sang de ta main.
In na ce wa mugu, ‘Lalle za ka mutu,’ ba ka kuwa yi masa kashedi ko ka tsawata masa a kan mugayen hanyoyinsa don yă ceci ransa ba, wannan mugun zai mutu saboda zunubinsa, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
19 Mais si tu avertis le méchant, et qu'il ne se détourne pas de sa méchanceté ni de sa mauvaise voie, il mourra dans son iniquité; mais toi, tu as sauvé ton âme. »
Amma in ka yi wa mugun kashedi bai kuwa juya daga mugayen hanyoyinsa ba, zai mutu saboda zunubinsa; amma kai kam za ka kuɓuta.
20 « Si un homme juste se détourne de sa justice et commet l'iniquité, et que je mette devant lui une pierre d'achoppement, il mourra. Parce que tu ne l'as pas averti, il mourra dans son péché, et l'on ne se souviendra pas des bonnes actions qu'il a faites; mais je demanderai son sang par ta main.
“Har yanzu, in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya aikata mugunta, na kuma sa abin tuntuɓe a gabansa, zai mutu. Da yake ba ka yi masa kashedi ba, zai mutu saboda zunubinsa. Ba za a tuna da abin adalcin da ya yi ba, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
21 Cependant, si tu avertis le juste, afin qu'il ne pèche pas, et qu'il ne pèche pas, il vivra, parce qu'il a été averti, et tu auras sauvé ton âme. »
Amma in ka yi wa mai adalcin kashedi kada yă yi zunubi bai kuwa yi zunubi ba, tabbatacce zai rayu saboda ya ji kashedin, kuma kai kam za ka kuɓuta.”
22 La main de Yahvé était là, sur moi, et il me dit: « Lève-toi, va dans la plaine, et là je te parlerai. »
Hannun Ubangiji ya kasance a kaina a can, ya kuma ce mini, “Tashi ka fita zuwa fili, a can kuwa zan yi maka magana.”
23 Alors je me levai, et je sortis dans la plaine. Et voici que la gloire de Yahvé se tenait là, comme la gloire que j'avais vue près du fleuve Kebar. Alors je tombai sur ma face.
Saboda haka na tashi da tafi fili. Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta tsaya a can, kamar ɗaukakar da na gani kusa da Kogin Kebar, sai na fāɗi rubda ciki.
24 Alors l'Esprit entra en moi et me remit sur pied. Il me parla, et me dit: « Va, enferme-toi dans ta maison.
Sai Ruhu ya sauko a kaina ya kuma ɗaga ni na tsaya a ƙafafuna. Ya yi mini magana ya ce, “Ka fita, ka rufe kanka a cikin gida.
25 Mais toi, fils d'homme, voici qu'on te mettra des cordes et qu'on t'attachera avec elles, et tu ne sortiras pas au milieu d'eux.
Kuma kai, ɗan mutum, za su ɗaura ka da igiyoyi; za a daure ka yadda ba za ka iya fita a cikin mutane ba.
26 Je ferai coller ta langue au palais de ta bouche, de sorte que tu seras muet et que tu ne pourras pas les corriger, car c'est une maison rebelle.
Zan sa harshenka ya manne wa dasashinka don ka yi shiru ka kuma kāsa tsawata musu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
27 Mais quand je parlerai avec toi, j'ouvrirai ta bouche et tu leur diras: « Voici ce que dit le Seigneur Yahvé ». Que celui qui entende, entende, et que celui qui refuse, refuse, car c'est une maison rebelle. »
Amma sa’ad da na yi maka magana, zan buɗe bakinka za ka kuwa faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’ Duk mai ji ya ji, kuma duk wanda ya ƙi ji, ya ƙi ji; gama su gida ne na’yan tawaye.

< Ézéchiel 3 >