< Ézéchiel 20 >
1 La septième année, le cinquième mois, le dixième jour du mois, quelques-uns des anciens d'Israël vinrent consulter l'Éternel et s'assirent devant moi.
A shekara ta bakwai, a wata na biyar a rana ta goma, waɗansu dattawan Isra’ila suka zo don su nemi nufin Ubangiji, suka kuwa zauna a ƙasa a gabana.
2 La parole de Yahvé me fut adressée en ces termes:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
3 « Fils d'homme, parle aux anciens d'Israël, et dis-leur: « Le Seigneur Yahvé dit: « Est-ce pour me consulter que vous êtes venus? Je suis vivant, dit le Seigneur Yahvé, et je ne me laisserai pas interroger par vous ».
“Ɗan mutum, ka yi magana da dattawan Isra’ila ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kun zo ne ku nemi shawarata? Muddin ina raye, ba zan bari ku nemi shawarata ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’
4 « Les jugeras-tu, fils de l'homme? Les jugeras-tu? Fais-leur connaître les abominations de leurs pères.
“Za ka hukunta su? Za ka hukunta su, ɗan mutum? To, sai ka kalubalance su da ayyukan banƙyamar kakanninsu
5 Dis-leur: Le Seigneur Yahvé dit: « Le jour où j'ai choisi Israël, où j'ai juré aux descendants de la maison de Jacob, où je me suis fait connaître à eux au pays d'Égypte, où je leur ai juré: « Je suis Yahvé votre Dieu »,
ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na zaɓi Isra’ila, na ɗaga hannuna, na rantse wa zuriyar gidan Yaƙub na kuma bayyana kaina gare su a Masar da hannun da na ɗaga na ce musu, “Ni ne Ubangiji Allahnku.”
6 ce jour-là, je leur ai juré de les faire sortir du pays d'Égypte pour entrer dans un pays que je leur avais préparé, où coulent le lait et le miel, et qui est la gloire de tous les pays.
A ranar na yi musu rantsuwa cewa zan fitar da su daga Masar zuwa ƙasar da na samo musu, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe.
7 Je leur ai dit: « Que chacun de vous jette les abominations de ses yeux. Ne vous souillez pas avec les idoles d'Égypte. Je suis Yahvé, votre Dieu.
Na kuma ce musu, “Kowannenku ya zubar da mugayen siffofin da kuka kafa idanunku a kai, kuma kada ku ƙazantar da kanku da gumakan Masar. Ni ne Ubangiji Allahnku.”
8 "''Mais ils se sont rebellés contre moi et n'ont pas voulu m'écouter. Ils n'ont pas tous rejeté les abominations de leurs yeux. Ils n'ont pas non plus abandonné les idoles d'Égypte. Alors j'ai dit que je répandrais sur eux ma fureur, pour accomplir ma colère contre eux au milieu du pays d'Égypte.
“‘Amma sai suka yi tawaye a kaina ba su kuwa saurare ni ba; ba su zubar da mugayen siffofin da suka kafa idanunsu a kai ba, balle su ƙi gumakan Masar. Saboda haka zan zubo hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a Masar.
9 Mais j'ai agi à cause de mon nom, afin qu'il ne soit pas profané aux yeux des nations parmi lesquelles ils se trouvaient, aux yeux desquelles je me suis fait connaître à eux en les faisant sortir du pays d'Égypte.
Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da suka zauna a ciki da kuma a idanun al’ummai da na bayyana kaina ga Isra’ilawa ta wurin fitar da su daga Masar.
10 Je les fis sortir du pays d'Égypte et les conduisis dans le désert.
Saboda haka na fisshe su daga Masar na kawo su cikin hamada.
11 Je leur donnai mes lois et leur montrai mes ordonnances, que si un homme les met en pratique, il vivra en elles.
Na ba su ƙa’idodina na kuma sanar musu da dokokina, gama mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu.
12 Je leur ai aussi donné mes sabbats, comme un signe entre moi et eux, afin qu'ils sachent que je suis Yahvé qui les sanctifie.
Na kuma ba su Asabbataina kamar alama tsakaninmu, domin su san cewa Ni Ubangiji ne yake tsarkake su.
13 "''Mais la maison d'Israël s'est rebellée contre moi dans le désert. Ils n'ont pas suivi mes lois et ils ont rejeté mes ordonnances, que si un homme les observe, il vivra en elles. Ils ont grandement profané mes sabbats. Alors j'ai dit que je répandrais ma colère sur eux dans le désert, pour les consumer.
“‘Duk da haka mutanen Isra’ila suka yi mini tawaye a cikin hamada. Ba su bi ƙa’idodina ba amma suka ki dokokina, ko da yake mutumin da ya yi biyayya da su zai rayu ta wurinsu, suka ɓata Asabbataina ƙwarai. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma hallaka su a hamada.
14 Mais j'ai agi pour l'honneur de mon nom, afin qu'il ne soit pas profané aux yeux des nations sous le regard desquelles je les ai fait sortir.
Amma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
15 Je leur ai aussi juré dans le désert de ne pas les faire entrer dans le pays que je leur avais donné, ruisselant de lait et de miel, qui est la gloire de tous les pays,
Na kuma ɗaga hannu na rantse musu a hamada cewa ba zan kawo su ƙasar da na ba su ba, ƙasa mai zub da madara da zuma, ƙasa mafi kyau cikin dukan ƙasashe,
16 parce qu'ils ont rejeté mes ordonnances, qu'ils n'ont pas suivi mes lois, qu'ils ont profané mes sabbats, et que leur cœur est allé après leurs idoles.
domin sun ƙi dokokina ba su kuwa bi ƙa’idodina ba suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Gama zukatansu sun fi so su bauta wa gumakansu.
17 Mais mon œil les a épargnés, et je ne les ai pas détruits. Je ne les ai pas fait périr dans le désert.
Duk da haka na dube su ta tausayi ba zan hallaka su ko in kawo ƙarshensu a hamada ba.
18 J'ai dit à leurs enfants dans le désert: « Ne suivez pas les lois de vos pères. N'observez pas leurs ordonnances et ne vous souillez pas avec leurs idoles.
Na faɗa wa’ya’yansu a hamada, “Kada ku bi farillai kakanninku ko ku kiyaye dokokinsu ko ku ƙazantar da kanku da gumakansu.
19 Je suis Yahvé, votre Dieu. Marchez selon mes lois, observez mes ordonnances et mettez-les en pratique.
Ni ne Ubangiji Allahnku; ku bi ƙa’idodina ku kuma kula ku kiyaye dokokina.
20 Sanctifiez mes sabbats. Ils seront un signe entre moi et vous, afin que vous sachiez que je suis Yahvé votre Dieu ».
Ku kiyaye Asabbataina da tsarki, don su zama alama tsakaninmu. Ta haka za ku san cewa ni ne Ubangiji Allahnku.”
21 "''Mais les enfants se sont rebellés contre moi. Ils n'ont pas suivi mes lois et n'ont pas gardé mes ordonnances pour les mettre en pratique, ce que l'homme fait, il y vivra. Ils ont profané mes sabbats. Alors j'ai dit que je répandrais sur eux ma fureur, pour accomplir ma colère contre eux dans le désert.
“‘Amma’ya’yan suka yi mini tawaye. Ba su bi ƙa’idodina ba, ba su kula su kiyaye dokokina ba, ko da yake mutumin da ya kiyaye su zai rayu ta wurinsu, suka kuma ƙazantar da Asabbataina. Saboda haka na ce zan zuba hasalata a kansu in kuma aukar musu da fushina a hamada.
22 Mais je retirai ma main et je travaillai à cause de mon nom, afin qu'il ne fût pas profané aux yeux des nations sous le regard desquelles je les avais fait sortir.
Amma na janye hannuna, kuma saboda sunana na yi abin da zai kiyaye shi daga ƙazantuwa a idanun al’umman da a idonsu na fisshe su.
23 Je leur jurai, dans le désert, de les disperser parmi les nations et de les répandre dans les pays,
Na kuma ɗaga hannu na rantse musu cewa zan watsar da su cikin al’ummai in kuma warwatsa su cikin ƙasashe,
24 parce qu'ils n'avaient pas exécuté mes ordonnances, mais qu'ils avaient rejeté mes lois et profané mes sabbats, et que leurs yeux étaient attachés aux idoles de leurs pères.
domin ba su kiyaye dokokina ba amma suka ƙi ƙa’idodina suka kuma ƙazantar da Asabbataina, idanunsu suka yi sha’awar gumakan kakanninsu.
25 De plus, je leur ai donné des lois qui n'étaient pas bonnes, et des ordonnances dans lesquelles ils ne pouvaient pas vivre.
Na kuma ba da su ga farillan da ba su da kyau da dokokin da ba za su rayu ta wurinsu ba;
26 Je les ai pollués par leurs propres dons, en faisant passer par le feu tout ce qui ouvre le ventre, afin de les réduire en désolation, pour qu'ils sachent que je suis Yahvé. »'.
na bari suka ƙazantu ta wurin kyautai, hadayar kowane ɗan fari don in cika su da abin tsoro domin su san cewa ni ne Ubangiji.’
27 C'est pourquoi, fils de l'homme, parle à la maison d'Israël et dis-leur: « Le Seigneur Yahvé dit: « Vos pères m'ont blasphémé en ceci, qu'ils ont commis une infamie à mon égard.
“Saboda haka, ɗan mutum, ka yi magana da mutanen Isra’ila ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a wannan kuma kakanninku suka saɓe ni ta wurin yashe ni.
28 Car lorsque je les ai fait entrer dans le pays que j'avais juré de leur donner, ils ont vu toute colline élevée et tout arbre touffu, et ils y ont offert leurs sacrifices, et ils y ont présenté la provocation de leur offrande. C'est là qu'ils présentaient leurs sacrifices, et c'est là qu'ils présentaient leurs offrandes.
Sa’ad da na kawo su cikin ƙasar da na rantse zan ba su suka kuma ga tudu mai tsawo ko itace mai ganye, a can suka miƙa hadayunsu, suka yi sadakokin da suka tsokane ni na yi fushi, suka miƙa turaren ƙanshinsu suka kuma zuba sadakokinsu na sha.
29 Puis je leur ai dit: « Que signifie le haut lieu où vous allez? ". C'est ainsi que son nom est appelé Bamah jusqu'à ce jour. »''
Sai na ce musu, Wane ɗakin tsafi kuke tafiya?’” (Ana ce da shi Bama har wa yau.)
30 « C'est pourquoi tu diras à la maison d'Israël: « Le Seigneur Yahvé dit: « Vous vous souillez selon la voie de vos pères? Vous vous prostituez après leurs abominations?
“Domin haka ka faɗa wa gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa za ku ƙazantar da kanku yadda kakanninku suka yi ne ku yi sha’awar mugayen siffofinsu?
31 Quand vous offrez vos présents, quand vous faites passer vos fils par le feu, vous vous souillez par toutes vos idoles jusqu'à ce jour? Est-ce que je dois être interrogé par vous, maison d'Israël? Je suis vivant, dit le Seigneur Yahvé, je ne me laisserai pas interroger par vous!
Sa’ad da kuka miƙa kyautai naku, hadayar’ya’yanku maza a wuta, kuna cin gaba da ƙazantar da kanku da duka gumakanku har wa yau. Zan bari ku nemi shawarata, ya gidan Isra’ila? Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba zan bari ku nemi shawarata ba.
32 "« Ce qui vous vient à l'esprit ne sera pas du tout, puisque vous dites: « Nous serons comme les nations, comme les familles des pays, pour servir le bois et la pierre ».
“‘Kukan ce, “Kuna so ku zama kamar sauran al’ummai, kamar sauran mutanen duniya, waɗanda suke bauta wa itace da dutse.” Amma abin da kuke tunani ba zai taɓa faruwa ba.
33 Je suis vivant, dit le Seigneur Yahvé, et c'est à main forte, à bras étendu, à colère déversée, que je serai roi sur vous.
Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, zan yi mulki a kanku da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
34 Je vous ferai sortir du milieu des peuples, je vous rassemblerai des pays où vous êtes dispersés, à main forte, à bras étendu et avec une colère déversée.
Zan fitar da ku daga al’ummai in tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, da hannu mai iko da kuma hannu mai ƙarfi da kuma fushi.
35 Je vous conduirai dans le désert des peuples, et là j'entrerai en jugement avec vous, face à face.
Zan kawo ku cikin hamadar al’ummai a can kuwa, fuska da fuska, zan hukunta ku.
36 De même que j'ai jugé vos pères dans le désert du pays d'Égypte, de même je vous jugerai, dit le Seigneur Yahvé.
Yadda na hukunta kakanninku a hamadar ƙasar Masar, haka zan hukunta ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
37 Je vous ferai passer sous la verge, et je vous ferai entrer dans le lien de l'alliance.
Zan lura da ku yayinda kuke wucewa ƙarƙashin sanda, zan kuma kawo ku cikin daurin alkawari.
38 J'éliminerai du milieu de vous les rebelles et ceux qui me désobéissent. Je les ferai sortir du pays où ils habitent, mais ils n'entreront pas dans le pays d'Israël. Alors vous saurez que je suis Yahvé. »
Zan fitar da waɗanda suke mini tayarwa da kuma’yan tawaye. Ko da yake zan fitar da su daga ƙasar da suke zama, duk da haka ba za su shiga ƙasar Isra’ila ba. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
39 "'Quant à vous, maison d'Israël, le Seigneur Yahvé dit: « Allez, chacun sert ses idoles, et plus tard aussi, si vous ne m'écoutez pas; mais vous ne profanerez plus mon saint nom par vos dons et par vos idoles.
“‘Game da ku, ya gidan Isra’ila, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ku tafi ku bauta wa gumakanku, kowannenku! Amma daga baya tabbatacce za ku saurare ni ba kuwa za ku ƙara ɓata sunana mai tsarki da hadayunku da gumakanku ba.
40 Car sur ma montagne sainte, sur la montagne de la hauteur d'Israël, dit le Seigneur Yahvé, là toute la maison d'Israël, tous, me serviront dans le pays. Là, je les accueillerai, et là, je demanderai vos offrandes et les prémices de vos offrandes, avec toutes vos choses saintes.
Gama a kan dutsena mai tsarki, dutse mai tsayi na Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, a can a ƙasar gidan Isra’ila gaba ɗaya za su bauta mini, a can kuwa zan karɓe su. A can zan bukaci hadayunku da sadake sadakenku mafi kyau, tare da dukan tsarkakan hadayunku.
41 Je vous accueillerai comme une odeur agréable, quand je vous ferai sortir du milieu des peuples et que je vous rassemblerai des pays où vous avez été dispersés. Je serai sanctifié en toi aux yeux des nations.
Zan karɓe ku kamar turare mai ƙanshi sa’ad da na fitar da ku daga al’ummai na kuma tattara ku daga ƙasashe inda aka warwatsa ku, zan kuma nuna kaina mai tsarki a cikinku a idon al’ummai.
42 Vous saurez que je suis Yahvé, quand je vous ferai entrer dans le pays d'Israël, dans le pays que j'ai juré de donner à vos pères.
Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji sa’ad da na kawo ku cikin ƙasar Isra’ila, ƙasar da na ɗaga hannu na rantse zan ba wa kakanninku.
43 Là, vous vous souviendrez de vos voies et de toutes vos actions par lesquelles vous vous êtes souillés. Alors vous vous détesterez à vos propres yeux, à cause de tous les maux que vous avez commis.
A can za ku tuna da halinku da kuma dukan ayyukanku waɗanda kuka ɓata kanku da su, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda mugayen abubuwan da kuka aikata.
44 Vous saurez que je suis Yahvé, quand je vous aurai traités à cause de mon nom, non pas selon vos mauvaises voies, ni selon vos actions corrompues, maison d'Israël, dit le Seigneur Yahvé.'"
Za ku san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na yi muku haka saboda sunana ba bisa ga mugayen hanyoyinku da ayyukanku marasa kyau ba, ya gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
45 La parole de Yahvé me fut adressée, en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
46 « Fils d'homme, tourne ta face vers le midi, prêche vers le midi, et prophétise contre la forêt des champs du midi.
“Ɗan mutum, ka kafa fuskarka wajen kudu; ka yi wa’azi a kan kudu ka kuma yi annabci a kan kurmin ƙasar kudu.
47 Dis à la forêt du midi: « Écoute la parole de Yahvé: Le Seigneur Yahvé dit: « Voici, je vais allumer chez toi un feu qui dévorera tout arbre vert et tout arbre sec. La flamme ardente ne s'éteindra pas, et tous les visages, du sud au nord, en seront brûlés.
Ka faɗa wa kurmin kudanci, ‘Ji maganar Ubangiji. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gab da sa maka wuta, za tă kuwa cinye dukan itatuwanki sarai, da ɗanye da busasshe. Ba za a kashe wutar da take ci ba, kuma kowace fuska a kudu zuwa arewa za tă ƙone.
48 Toute chair verra que c'est moi, Yahvé, qui l'ai allumée. Elle ne s'éteindra pas. »'"
Kowa zai san cewa Ni Ubangiji ne ya ƙuna ta; ba za a kashe ta ba.’”
49 Alors je dis: « Ah, Seigneur Yahvé! On dit de moi: « N'est-il pas un orateur de paraboles? ».
Sai na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Suna zance a kaina cewa, ‘Ba misalai kawai yake yi ba?’”