< Exode 5 >

1 Moïse et Aaron vinrent ensuite et dirent à Pharaon: « Voici ce que dit Yahvé, le Dieu d'Israël: « Laisse aller mon peuple, pour qu'il me donne une fête dans le désert. »
Daga bisani sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Bari mutanena su tafi domin su yi mini biki a hamada.’”
2 Pharaon dit: « Qui est Yahvé, pour que j'écoute sa voix et laisse aller Israël? Je ne connais pas Yahvé, et je ne laisserai pas partir Israël. »
Fir’auna ya ce, “Wane ne Ubangiji da zan yi biyayya da shi, har in bar Isra’ila su tafi? Ban san Ubangiji ba, kuma ba zan bar Isra’ila su tafi ba.”
3 Ils dirent: « Le Dieu des Hébreux nous a rencontrés. Laissez-nous, je vous prie, aller à trois jours de marche dans le désert, et sacrifier à Yahvé, notre Dieu, de peur qu'il ne tombe sur nous par la peste ou par l'épée. »
Sai suka ce, “Allah na Ibraniyawa ya sadu da mu. Yanzu bari mu ɗauki tafiyar kwana uku cikin hamada domin mu miƙa hadaya ga Ubangiji Allahnmu, don kada yă buga mu da annoba ko takobi.”
4 Le roi d'Égypte leur dit: « Pourquoi, Moïse et Aaron, détournez-vous le peuple de son travail? Retournez à vos fardeaux! »
Amma sarkin Masar ya ce wa, “Musa da Haruna, don me kuke hana mutane yin aikinsu? Ku koma wurin aikinku!”
5 Pharaon répondit: « Voici que le peuple du pays est maintenant nombreux, et vous le faites reposer de ses fardeaux. »
Sa’an nan Fir’auna ya ce, “Ga shi mutane sun yi yawa a ƙasar Masar, ku kuma yanzu kuna so ku hana su yin aiki.”
6 Le même jour, Pharaon donna cet ordre aux maîtres d'œuvre du peuple et à leurs officiers:
A wannan rana Fir’auna ya ba da wannan umarni wa shugabannin masu gandu,
7 « Vous ne donnerez plus au peuple de la paille pour faire des briques, comme auparavant. Qu'ils aillent ramasser eux-mêmes de la paille.
“Kada ku ƙara ba wa mutanen ciyawar tattaka domin su yi tubula, bari su tafi su tattara tattaka da kansu.
8 Vous leur demanderez le nombre de briques qu'ils fabriquaient auparavant. Tu n'en diminueras rien, car ils sont oisifs. C'est pourquoi ils crient: « Allons sacrifier à notre Dieu ».
Ku kuma bukace su su yi tubula daidai yawan tubalin da suka saba yi, kada ku rage. Ragwaye ne, shi ya sa suke kuka cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya ga Allahnmu.’
9 Que des travaux plus lourds soient confiés aux hommes, afin qu'ils y travaillent. Qu'ils ne fassent pas attention aux paroles mensongères. »
Ku sa waɗannan mutane su yi aiki mai tsanani sosai, don kada su sami zarafin kasa kunne ga maganganun ƙarya.”
10 Les maîtres du peuple sortirent avec leurs officiers, et ils parlèrent au peuple en disant: « Voici ce que dit Pharaon: Je ne vous donnerai pas de paille.
Sai shugabannin masu aikin gandu suka fita suka gaya wa mutanen Isra’ila, “Ga abin da Fir’auna ya ce, ‘Ba zan ƙara ba ku tattaka ba.
11 Allez vous-mêmes chercher de la paille où vous pourrez en trouver, car rien de votre travail ne sera diminué. »
Ku tafi ku nemo wa kanku tattaka duk inda za ku samu, amma ba za a rage aikinku ba ko kaɗan.’”
12 Le peuple fut donc dispersé dans tout le pays d'Égypte pour ramasser du chaume en guise de paille.
Saboda haka mutane suka warwatsu ko’ina a Masar domin tattara bunnun da za su yi amfani da su, maimakon tattaka.
13 Les maîtres de corvées disaient avec insistance: « Remplissez chaque jour votre quota de travail, comme quand il y avait de la paille! »
Shugabannin gandu suka dinga matsa musu suna cewa, “Ku cika aikin da aka bukace ku na kowace rana kamar yadda kuke yi sa’ad da kuke da tattaka.”
14 Les officiers des enfants d'Israël, que les maîtres de corvées de Pharaon avaient établis sur eux, furent battus et on leur demanda: « Pourquoi n'avez-vous pas rempli votre quota hier et aujourd'hui, en fabriquant des briques comme auparavant? »
Manyan Isra’ilawa waɗanda shugabannin gandun Fir’auna suka naɗa, suka sha dūka, aka kuma yi musu tambayoyi ana cewa, “Don me ba ku cika yawan tubula na jiya da na yau kamar yadda kuka saba ba?”
15 Les officiers des enfants d'Israël vinrent et crièrent à Pharaon: « Pourquoi agis-tu ainsi avec tes serviteurs?
Sai manyan Isra’ila masu bi da aikin gandu suka tafi wurin Fir’auna suka yi roƙo suna cewa, “Don me kake yi wa bayinka haka?
16 On ne donne pas de paille à tes serviteurs, et ils nous disent: « Fais des briques », et voilà que tes serviteurs sont battus; mais la faute en revient à ton peuple. »
Ba a ba wa bayinka tattaka, duk da haka ana ce mana, ‘Ku yi tubula!’ Ana wa bayinka dūka, amma fa laifin na mutanenka ne.”
17 Mais Pharaon dit: « Tu es oisif! Vous êtes oisifs! C'est pourquoi vous dites: « Allons sacrifier à Yahvé ».
Fir’auna ya ce, “Ku ragwaye ne! Shi ya sa kuke cewa, ‘Bari mu tafi mu yi hadaya wa Ubangiji.’
18 Va donc maintenant, et travaille; on ne te donnera pas de paille, mais tu livreras le même nombre de briques! ».
Ku ɓace yanzu daga nan, ku koma wurin aikinku. Ba za a ba ku tattaka ba, kuma dole ku fid da tubula kamar yadda kuka saba.”
19 Les officiers des enfants d'Israël virent qu'ils avaient des ennuis quand on leur dit: « Vous ne diminuerez rien de votre quota quotidien de briques! »
Manyan Isra’ilawa da suke bi da aikin gandu suka gane cewa sun shiga uku, sa’ad da aka gaya musu, “Ba za ku rage yawan tubulan da aka bukace ku ku yi na kowace rana ba.”
20 Ils rencontrèrent Moïse et Aaron, qui se tenaient le long du chemin, comme ils sortaient de chez Pharaon.
Da suka bar Fir’auna, sai suka sadu da Musa da Haruna suna jira su sadu da su,
21 Ils leur dirent: « Que Yahvé vous regarde et vous juge, car vous avez fait de nous un objet d'horreur aux yeux de Pharaon et aux yeux de ses serviteurs, afin de mettre une épée dans leur main pour nous tuer! ».
sai suka ce, “Bari Ubangiji yă duba, yă kuma hukunta ku! Kun maishe mu abin ƙyama ga Fir’auna da bayinsa, kuka kuma sa musu takobi a hannunsu don su kashe mu.”
22 Moïse retourna auprès de Yahvé et dit: « Seigneur, pourquoi as-tu fait venir la détresse sur ce peuple? Pourquoi m'as-tu envoyé?
Musa ya koma wurin Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, don me ka kawo wahala a kan mutanen nan? Abin da ya sa ka aiko ni ke nan?
23 Car depuis que je suis allé parler en ton nom à Pharaon, il a fait venir le malheur sur ce peuple. Tu n'as pas du tout secouru ton peuple! »
Gama tun da na tafi wurin Fir’auna, na yi masa magana da sunanka, sai ya fara gasa wa mutanen nan azaba, ba ka kuma ceci mutanenka.”

< Exode 5 >