+ Genèse 1 >

1 Au commencement, Dieu créa les cieux et la terre.
A farko-farko, Allah ya halicci sama da ƙasa.
2 La terre était informe et vide. Les ténèbres étaient à la surface de l'abîme et l'Esprit de Dieu planait au-dessus de la surface des eaux.
To, ƙasa dai ba ta da siffa, babu kuma kome a cikinta, duhu ne kawai ya rufe ko’ina, Ruhun Allah kuwa yana yawo a kan ruwan.
3 Dieu dit: « Que la lumière soit! » et la lumière fut.
Sai Allah ya ce, “Bari haske yă kasance,” sai kuwa ga haske.
4 Dieu vit la lumière, et il vit qu'elle était bonne. Dieu sépara la lumière d'avec les ténèbres.
Allah ya ga hasken yana da kyau, sai ya raba tsakanin hasken da duhu.
5 Dieu appela la lumière « jour », et il appela les ténèbres « nuit ». Il y eut un soir et il y eut un matin: ce fut le premier jour.
Allah ya kira hasken “yini,” ya kuma kira duhun “dare.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta fari ke nan.
6 Dieu dit: « Qu'il y ait une étendue au milieu des eaux, et qu'elle sépare les eaux d'avec les eaux. »
Allah ya ce, “Bari sarari yă kasance tsakanin ruwaye domin yă raba ruwa da ruwa.”
7 Dieu fit l'étendue, et il sépara les eaux qui étaient au-dessous de l'étendue des eaux qui étaient au-dessus de l'étendue; et il en fut ainsi.
Saboda haka Allah ya yi sarari ya raba ruwan da yake ƙarƙashin sararin da ruwan da yake bisansa. Haka kuwa ya kasance.
8 Dieu appela l'étendue « ciel ». Il y eut un soir et il y eut un matin, un second jour.
Allah ya kira sararin “sama.” Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyu ke nan.
9 Dieu dit: « Que les eaux qui sont sous le ciel se rassemblent en un seul lieu, et que la terre sèche apparaisse »; et il en fut ainsi.
Allah ya ce, “Bari ruwan da yake ƙarƙashin sama yă tattaru wuri ɗaya, bari kuma busasshiyar ƙasa tă bayyana.” Haka kuwa ya kasance.
10 Dieu appela la terre sèche « terre », et il appela le rassemblement des eaux « mer ». Dieu vit que cela était bon.
Allah ya kira busasshiyar ƙasar “doron ƙasa,” ruwan da ya taru kuma, ya kira “tekuna.” Allah ya ga yana da kyau.
11 Dieu dit: « Que la terre produise de l'herbe, des herbes portant des graines, et des arbres fruitiers portant des fruits selon leur espèce, avec leurs graines, sur la terre ».
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari ƙasa tă fid da tsire-tsire, da shuke-shuke, da itatuwa a bisa ƙasa masu ba da amfani da’ya’ya a cikinsu, bisa ga irinsu.” Haka kuwa ya kasance.
12 La terre produisit de l'herbe, des herbes portant de la semence selon leur espèce, et des arbres fruitiers portant du fruit selon leur espèce, avec leur semence en elle; et Dieu vit que cela était bon.
Ƙasar ta fid da tsire-tsire, da shuke-shuke masu ba da’ya’ya bisa ga irinsu, ta fid kuma da itatuwa masu ba da’ya’ya da iri a cikinsu bisa ga irinsu. Allah ya ga yana da kyau.
13 Il y eut un soir, et il y eut un matin: ce fut le troisième jour.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta uku ke nan.
14 Dieu dit: « Qu'il y ait des luminaires dans l'étendue du ciel pour séparer le jour d'avec la nuit, et qu'ils servent de signes pour marquer les saisons, les jours et les années;
Allah kuma ya ce, “Bari haskoki su kasance a sararin sama domin su raba yini da dare, bari su zama alamu domin su nuna yanayi, da ranaku, da kuma shekaru,
15 et qu'ils servent de luminaires dans l'étendue du ciel pour éclairer la terre ».
bari kuma haskokin su kasance a sararin sama domin su ba da haske a duniya.” Haka kuwa ya kasance.
16 Dieu fit les deux grands luminaires: le grand luminaire pour régir le jour, et le petit luminaire pour régir la nuit. Il fit aussi les étoiles.
Allah ya yi manyan haskoki biyu, babban hasken yă mallaki yini, ƙaramin kuma yă mallaki dare. Ya kuma yi taurari.
17 Dieu les plaça dans l'étendue du ciel pour éclairer la terre,
Allah ya sa su a sararin sama domin su ba da haske a duniya,
18 pour dominer le jour et la nuit, et pour séparer la lumière des ténèbres. Dieu vit que cela était bon.
su mallaki yini da kuma dare, su kuma raba haske da duhu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
19 Il y eut un soir et il y eut un matin: ce fut le quatrième jour.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta huɗu ke nan.
20 Dieu dit: « Que les eaux regorgent d'êtres vivants, et que les oiseaux volent au-dessus de la terre dans l'étendue du ciel. »
Allah ya ce, “Bari ruwa yă cika da halittu masu rai, bari tsuntsaye kuma su tashi sama a bisa duniya a sararin sama.”
21 Dieu créa les grands animaux marins et tous les êtres vivants qui se meuvent, dont les eaux fourmillent, selon leur espèce, et tout oiseau ailé selon son espèce. Dieu vit que cela était bon.
Allah ya halicci manyan halittun teku, da kowane mai rai da abin da yake motsi a ruwa, bisa ga irinsu, da kuma kowane tsuntsu mai fiffike bisa ga irinsa. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
22 Dieu les bénit, en disant: « Soyez féconds, multipliez, remplissez les eaux des mers, et que les oiseaux se multiplient sur la terre. »
Allah ya albarkace su ya ce, “Ku yi ta haihuwa ku kuma ƙaru da yawa, ku cika ruwan tekuna, bari kuma tsuntsaye su yi yawa a bisa duniya.”
23 Il y eut un soir, et il y eut un matin: ce fut le cinquième jour.
Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta biyar ke nan.
24 Dieu dit: « Que la terre produise des êtres vivants selon leur espèce, du bétail, des reptiles et des animaux de la terre selon leur espèce »; et il en fut ainsi.
Allah kuwa ya ce, “Bari ƙasa tă ba da halittu masu rai bisa ga irinsu; dabbobi da halittu masu rarrafe, da kuma namun jeji, kowane bisa ga irinsa.” Haka kuwa ya kasance.
25 Dieu fit les animaux de la terre selon leur espèce, le bétail selon son espèce, et tout ce qui rampe sur le sol selon son espèce. Dieu vit que cela était bon.
Allah ya halicci namun jeji bisa ga irinsu, dabbobi bisa ga irinsu, da kuma dukan halittu masu rarrafe a ƙasa bisa ga irinsu. Allah kuwa ya ga yana da kyau.
26 Dieu dit: « Faisons l'homme à notre image, selon notre ressemblance. Qu'ils dominent sur les poissons de la mer, sur les oiseaux du ciel, sur le bétail, sur toute la terre et sur tous les reptiles qui rampent sur la terre. »
Sa’an nan Allah ya ce, “Bari mu yi mutum cikin siffarmu, cikin kamanninmu, bari kuma su yi mulki a bisa kifin teku, tsuntsayen sama, da kuma dabbobi, su yi mulki a bisa dukan duniya, da kuma a bisa dukan halittu, da masu rarrafe a ƙasa.”
27 Dieu a créé l'homme à son image. Il le créa à l'image de Dieu; il les créa mâle et femelle.
Saboda haka Allah ya halicci mutum cikin siffarsa. Cikin kamannin Allah, Allah ya halicci mutum. Miji da mace ya halicce su.
28 Dieu les bénit. Dieu leur dit: « Soyez féconds, multipliez, remplissez la terre et soumettez-la. Dominez les poissons de la mer, les oiseaux du ciel et tout être vivant qui se meut sur la terre. »
Allah ya albarkace su, ya kuma ce musu, “Ku yi ta haihuwa ku ƙaru da yawa, ku mamaye duniya, ku mallake ta. Ku yi mulki a bisa kifin teku, da tsuntsayen sararin sama, da kuma bisa kowace halitta mai rai wadda take rarrafe a ƙasa.”
29 Dieu dit: « Voici, je vous ai donné toute herbe portant de la semence, qui est à la surface de toute la terre, et tout arbre portant du fruit et portant de la semence. Ce sera votre nourriture.
Sa’an nan Allah ya ce, “Ga shi, na ba ku kowane tsiro mai ba da’ya’ya masu kwaya da suke a fāɗin duniya, da dukan itatuwa masu ba da’ya’ya, don su zama abinci a gare ku.
30 A tout animal de la terre, à tout oiseau du ciel, et à tout ce qui rampe sur la terre et qui a de la vie, j'ai donné toute herbe verte pour nourriture.
Na kuma ba da dukan dabbobin ƙasa, da dukan tsuntsayen sama, da dukan abin da yake rarrafe a ƙasa, da dai iyakar abin da yake numfashi; haka kuma na ba da ganyaye su zama abinci.” Haka kuwa ya kasance.
31 Dieu vit tout ce qu'il avait fait, et voici, cela était très bon. Il y eut un soir et il y eut un matin, un sixième jour.
Allah ya ga dukan abin da ya yi, yana da kyau ƙwarai. Yamma ta kasance, safiya kuma ta kasance, kwana ta shida ke nan.

+ Genèse 1 >