< Deutéronome 32 >

1 Cieux, prêtez l'oreille, et je parlerai. Que la terre entende les paroles de ma bouche.
Ku saurara, ya ku sammai, zan yi magana; bari duniya ta ji maganar bakina.
2 Ma doctrine tombera comme la pluie. Mon discours se condensera comme la rosée, comme la pluie brumeuse sur l'herbe tendre, comme les averses sur l'herbe.
Bari koyarwata tă zubo kamar ruwan sama kalmomina kuma su sauko kamar raɓa, kamar yayyafi a kan sabuwar ciyawa, kamar ruwan sama mai yawa a kan tsirai marasa ƙarfi.
3 Car je proclamerai le nom de Yahvé. Attribuez la grandeur à notre Dieu!
Zan yi shelar sunan Ubangiji. Ku yabi girman Allahnmu!
4 The Rock: son travail est parfait, car toutes ses voies sont justes. Un Dieu de fidélité qui ne fait pas de mal, Il est juste et droit.
Shi Dutse ne, ayyukansa cikakku ne, dukan hanyoyinsa kuwa masu adalci ne. Allah mai aminci, wanda ba ya yin rashi gaskiya, shi mai adalci ne, nagari ne kuma.
5 Ils l'ont corrompu. Ils ne sont pas ses enfants, à cause de leur défaut. C'est une génération perverse et tordue.
Sun aikata mugunta a gabansa; saboda abin kunyarsu, su ba’ya’yansa ba ne, amma wata muguwar tsara ce, karkatacciya.
6 Est-ce ainsi que vous remboursez Yahvé, des gens stupides et imprudents? N'est-ce pas ton père qui t'a acheté? Il vous a fait et vous a établi.
Haka za ku biya Ubangiji, Ya ku wawaye da kuma mutane marasa hikima? Shi ba Ubanku ba ne, Mahaliccinku, wanda ya yi ku, ya kuma siffanta ku?
7 Souviens-toi des jours d'autrefois. Considérez les années de plusieurs générations. Demande à ton père, et il te montrera; vos aînés, et ils vous le diront.
Ku tuna da kwanakin dā, ku tuna da tsararrakin da suka wuce tun tuni, Ku tambayi iyayenku, za su faɗa muku, dattawanku, za su kuma bayyana muku.
8 Quand le Très-Haut donna aux nations leur héritage, quand il a séparé les enfants des hommes, il a fixé les limites des peuples selon le nombre des enfants d'Israël.
Sa’ad da Mafi Ɗaukaka ya ba da al’ummai gādonsu, sa’ad da ya raba dukan’yan adam, ya kafa iyakoki wa mutane bisa ga yawan’ya’yan Isra’ila maza.
9 Car le partage de Yahvé, c'est son peuple. Jacob est le lot de son héritage.
Gama rabon Ubangiji shi ne mutanensa, Yaƙub shi ne rabon gādonsa.
10 Il le trouva dans une terre déserte, dans le désert hurlant. Il l'a entouré. Il se souciait de lui. Il l'a gardé comme la prunelle de ses yeux.
A cikin hamada ya same shi, a jeji marar amfani, inda namomi suke kuka. Ya tsare shi, ya kuma lura da shi; ya bi da shi kamar ƙwayar idonsa,
11 Comme un aigle qui remue son nid, qui flottent sur ses jeunes, il a déployé ses ailes, il les a pris, il les portait sur ses plumes.
kamar gaggafar da take yawo a kan sheƙarta tana rufe’ya’yanta, ta buɗe fikafikanta don tă kwashe su tă ɗauke su a kafaɗunta.
12 Yahvé seul l'a conduit. Il n'y avait pas de dieu étranger avec lui.
Ubangiji kaɗai ya jagorance shi; babu wani baƙon gunkin da yake tare da shi.
13 Il l'a fait monter sur les hauts lieux de la terre. Il a mangé les fruits des champs. Il lui a fait sucer le miel de la roche, l'huile de la roche silex;
Ya sa shi ya hau ƙwanƙolin dutse ya ciyar da shi da amfanin gona. Ya shayar da shi da zuma daga dutse, da kuma mai daga dutsen ƙanƙara,
14 le beurre du troupeau, et le lait du troupeau, avec de la graisse d'agneau, des béliers de la race de Bashan, et des chèvres, avec le meilleur des blés. Du sang du raisin, vous avez bu du vin.
da kindirmo da madara daga shanu da tumaki da ƙibabbun tumaki da awaki, da zaɓaɓɓun ragunan Bashan da kuma ƙwayoyin alkama mafi kyau. Ka sha ruwan inabi ja wur mai kumfa.
15 Mais Jeshurun devint gras, et donna des coups de pied. Tu as grossi. Tu es devenu épais. Vous êtes devenu élégant. Puis il a abandonné Dieu qui l'a créé, et a rejeté le Rocher de son salut.
Yeshurun ya yi ƙiba, ya yi kauri; cike da abinci, ya zama da nauyi, ya kuma zama sumul. Ya yashe Allahn da ya yi shi, ya ƙi Dutse Cetonsa.
16 Ils l'ont excité à la jalousie avec des dieux étrangers. Ils l'ont irrité par des abominations.
Suka sa shi kishi saboda baƙin allolinsu, suka husata shi da gumakan banƙyamarsu.
17 Ils sacrifiaient aux démons, pas à Dieu, à des dieux qu'ils ne connaissaient pas, aux nouveaux dieux qui sont apparus récemment, que vos pères n'ont pas redouté.
Suka yi hadaya ga aljanu, waɗanda ba Allah ba, ga allolin da ba su sani ba, ga allolin da aka shigo da su daga baya, allolin da kakanninku ba su ji tsoronsu ba.
18 Vous ne vous souvenez pas du Rocher qui est devenu votre père, et vous avez oublié le Dieu qui vous a donné la vie.
Kuka rabu da Dutsen da ya zama mahaifi gare ku; kuka manta da Allahn da ya haife ku.
19 L'Éternel a vu et abhorré, à cause de la provocation de ses fils et de ses filles.
Ubangiji ya ga wannan ya kuma ƙi su, domin’ya’yansa maza da mata sun husata shi.
20 Il a dit: « Je leur cacherai ma face. Je verrai ce que sera leur fin; car c'est une génération très perverse, des enfants en qui il n'y a pas de fidélité.
Ya ce, “Zan ɓoye fuskata daga gare su, in ga ƙarshensu; gama su muguwar tsara ce,’ya’ya ne marasa aminci.
21 Ils m'ont excité à la jalousie par ce qui n'est pas Dieu. Ils m'ont provoqué à la colère par leurs vanités. Je les pousserai à la jalousie envers ceux qui ne sont pas un peuple. Je les provoquerai à la colère d'une nation insensée.
Sun sa ni kishi ta wurin abin da ba allah ba, suka kuma husata ni da gumakansu na wofi. Zan sa su yi kishi ta wurin waɗanda ba mutane ba; zan sa su yi fushi ta wurin al’ummar da ba ta da sani.
22 Car un feu s'est allumé dans ma colère, qui brûle jusqu'au plus profond du Sheol, dévore la terre avec son accroissement, et met le feu aux fondations des montagnes. (Sheol h7585)
Gama fushina ya kama wuta, tana ci har ƙurewar zurfin lahira. Za tă cinye duniya da girbinta, tă kuma sa wuta a tussan duwatsu. (Sheol h7585)
23 « Je les accablerai de maux. Je vais dépenser mes flèches pour eux.
“Zan tula masifu a kansu in kuma gama kibiyoyina a kansu.
24 Ils seront épuisés par la faim, et dévorés par une chaleur brûlante et une destruction amère. J'enverrai sur eux les dents des animaux, avec le venin des vipères qui glissent dans la poussière.
Zan aika da yunwa mai tsanani a kansu, zazzaɓi mai zafi da muguwar annoba; zan aika da haƙoran namun jeji a kansu, da dafin mesa masu ja da ciki.
25 Dehors l'épée arrachera, et dans les chambres, la terreur sur le jeune homme et la vierge, le nourrisson avec l'homme aux cheveux gris.
Waɗanda suke a waje, takobi zai kashe su, a cikin gidajensu kuma tsoro zai mamaye su.’Yan maza da’yan mata za su hallaka, haka ma jarirai da maza masu furfura.
26 J'ai dit que je les disperserais au loin. Je ferais en sorte que leur souvenir disparaisse d'entre les hommes;
Na ce zan watsar da su in sa a manta da su a tunanin’yan adam.
27 si je ne craignais la provocation de l'ennemi, de peur que leurs adversaires ne jugent mal, de peur qu'ils ne disent: « Notre main s'est élevée »; Yahvé n'a pas fait tout cela. »
Amma ina tsoron tsokanar abokin gāba, don kada abokan gāba su kāsa ganewa har su ce, ‘Hannunmu ne ya yi nasara; ba Ubangiji ne ya aikata dukan wannan ba.’”
28 Car c'est une nation sans conseil. Il n'y a aucune compréhension en eux.
Al’ummai ne marasa azanci, babu ganewa a cikinsu.
29 Oh, qu'ils soient sages, qu'ils comprennent cela, qu'ils considèrent leur fin dernière!
A ce su masu hikima ne har su gane wannan su gane abin da ƙarshensu zai zama!
30 Comment un seul pourrait-il chasser un millier, et deux ont mis en fuite dix mille personnes, à moins que leur Rock ne les ait vendus, et Yahvé les avait livrés?
Yaya mutum guda zai kore dubu, mutum biyu su sa dubu goma su gudu, sai ko Dutsensu ya sayar da su, sai ko Ubangiji ya bashe su.
31 Car leur rocher n'est pas comme notre rocher, que même nos ennemis eux-mêmes concèdent.
Gama dutsensu ba kamar Dutsenmu ba ne, abokan gābanmu sun san da haka.
32 Car leur vigne est de la vigne de Sodome, des champs de Gomorrhe. Leurs raisins sont des raisins empoisonnés. Leurs grappes sont amères.
Kuringarsu ta fito daga kuringar Sodom ne, daga gonakin Gomorra kuma.’Ya’yan inabinsu dafi ne, nonnansu masu ɗaci ne.
33 Leur vin est le poison des serpents, le venin cruel des aspics.
Ruwan inabinsu dafin macizai ne, mugun dafin gamshaƙa ne.
34 « N'est-ce pas là ce qui est mis en réserve chez moi, scellé parmi mes trésors?
“Ban jibge wannan a ma’ajiya na kuma yimƙe shi a taskokina ba?
35 A moi la vengeance, la rétribution! au moment où leur pied glisse, car le jour de leur calamité est proche. Leur destin se précipite sur eux. »
Sakayya nawa ne, zan kuwa ɗau fansa. A cikin lokaci, ƙafarsu za tă yi santsi; ranar masifarsu ta yi kusa hallakarsu kuma tana gaggautawa a kansu.”
36 Car Yahvé jugera son peuple, et avoir de la compassion pour ses serviteurs, quand il voit que leur pouvoir a disparu, qu'il n'y a plus personne qui reste, enfermé ou laissé en liberté.
Ubangiji zai shari’anta mutanensa yă kuma ji tausayin bayinsa sa’ad da ya ga ƙarfinsu ya ƙare babu kowa kuma da ya rage, bawa ko’yantacce.
37 Il dira: « Où sont leurs dieux? le rocher dans lequel ils se sont réfugiés,
Zai ce, “To, ina allolinsu, dutsen da suka yi mafaka a ciki,
38 qui mangeaient la graisse de leurs sacrifices, et buvaient le vin de leur libation? Laissez-les se lever et vous aider! Laissez-les être votre protection.
allolin da suka ci kitsen hadayunsu suka kuma sha ruwan inabin hadayunsu? Ku sa su tashi su taimake ku mana! Bari su ba ku mafaka!
39 « Voyez maintenant que c'est moi qui suis lui. Il n'y a pas de dieu avec moi. Je tue et je fais vivre. Je blesse et je guéris. Il n'y a personne qui puisse délivrer de ma main.
“Ku duba yanzu cewa ni ne Shi! Ba wani allah in ban da ni. Nakan kashe in kuma rayar, nakan sa rauni in kuma warkar, ba wanda yake da iko yă cece wani daga hannuna.
40 Car je lève ma main vers le ciel et je déclare, comme je vis pour toujours,
Na ɗaga hannu sama na kuma furta. Muddin ina raye har abada,
41 si j'aiguise mon épée étincelante, ma main la saisit en guise de jugement; Je me vengerai de mes adversaires, et rendra la pareille à ceux qui me haïssent.
sa’ad da na wasa takobi mai walƙiya hannuna kuwa ya cafke shi don yin hukunci, zan ɗau fansa a kan abokan gābana in sāka wa waɗanda suke ƙina.
42 Je vais rendre mes flèches ivres de sang. Mon épée dévorera la chair avec le sang des tués et des captifs, de la tête des chefs de l'ennemi. »
Zan sa kibiyoyina su bugu da jini, yayinda takobina yana cin nama, jinin kisassu da na kamammu, kawunan shugabannin abokan gāba.”
43 Réjouissez-vous, nations, avec son peuple, car il vengera le sang de ses serviteurs. Il se vengera de ses adversaires, et fera l'expiation pour son pays et pour son peuple.
Ku yi farin ciki, ya ku al’ummai, tare da mutanensa, gama zai rama ɗau fansar jinin bayinsa; zai ɗau fansa a kan abokan gābansa yă kuma yi kafara domin ƙasarsa da mutanensa.
44 Moïse vint et prononça toutes les paroles de ce cantique aux oreilles du peuple, lui et Josué, fils de Nun.
Sai Musa ya zo da Yoshuwa ɗan Nun suka faɗa dukan waɗannan kalmomi wannan waƙa a kunnen mutane.
45 Moïse acheva de réciter toutes ces paroles à tout Israël.
Sa’ad da Musa ya gama karanta waɗannan kalmomi ga dukan Isra’ila,
46 Il leur dit: « Fixez votre cœur à toutes les paroles que je vous annonce aujourd'hui, que vous ordonnerez à vos enfants d'observer et de mettre en pratique, toutes les paroles de cette loi.
ya ce musu, “Ku riƙe dukan kalmomin da na furta muku a yau, don ku umarce’ya’yanku su lura, su yi biyayya da dukan kalmomin wannan doka.
47 Car ce n'est pas une chose vaine pour vous, car il s'agit de votre vie, et c'est par elle que vous prolongerez vos jours dans le pays où vous passerez le Jourdain pour le posséder. »
Ba kalmomi kurum ba ne dominku, amma har ranku ma. Ta wurinsu za ku yi tsawon rai a ƙasar da kuke haye Urdun ku ci gādonta.”
48 Ce même jour, Yahvé parla à Moïse et dit:
A wannan rana Ubangiji ya ce wa Musa,
49 « Monte sur cette montagne d'Abarim, sur le mont Nebo, qui est dans le pays de Moab, en face de Jéricho, et regarde le pays de Canaan que je donne en propriété aux enfants d'Israël.
“Ka hau Duwatsun Abarim zuwa Dutsen Nebo a Mowab, tsallake daga Yeriko, ka hangi Kan’ana, ƙasar da nake ba wa Isra’ilawa gādo.
50 Tu mourras sur la montagne où tu montes, et tu seras recueilli auprès de ton peuple, comme Aaron, ton frère, est mort sur la montagne de Hor, et a été recueilli auprès de son peuple;
A can kan dutsen da ka hau za ka mutu a kuma tara ka ga mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya mutu a Dutsen Hor aka kuma tara shi ga mutanensa.
51 parce que vous m'avez offensé au milieu des enfants d'Israël, aux eaux de Meriba de Kadès, dans le désert de Tsin, parce que vous n'avez pas maintenu ma sainteté au milieu des enfants d'Israël.
Wannan kuwa domin ku biyu kun fid da aminci gare ni a gaban Isra’ilawa a ruwan Meriba ta Kadesh, a Hamadar Zin kuma saboda ba ku riƙe tsarkina a cikin Isra’ilawa ba.
52 Car vous verrez le pays de loin; mais vous n'irez pas là dans le pays que je donne aux enfants d'Israël. »
Saboda haka, za ka ga ƙasar daga nesa kawai; ba za ka shiga ƙasar da nake ba wa mutanen Isra’ila ba.”

< Deutéronome 32 >