< Nombres 1 >

1 Yahvé parla à Moïse dans le désert de Sinaï, dans la tente de la Rencontre, le premier jour du second mois, la deuxième année après leur sortie du pays d'Égypte, et il dit:
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2 « Recense toute l'assemblée des enfants d'Israël, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, d'après le nombre de leurs noms, tous les mâles, un par un,
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3 depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui sont en état de porter les armes en Israël. Toi et Aaron, vous les compterez selon leurs divisions.
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4 Il y aura avec vous un homme de chaque tribu, chacun à la tête de la maison de ses pères.
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5 Voici les noms des hommes qui se tiendront à vos côtés: De Reuben: Elizur, fils de Shedeur.
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6 De Siméon: Shelumiel, fils de Zurishaddai.
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7 De Juda: Nahshon, fils d'Amminadab.
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8 D'Issachar: Nethanel, fils de Zuar.
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9 De Zabulon: Eliab, fils de Helon.
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10 Des fils de Joseph: d'Éphraïm: Élischama, fils d'Ammihud; de Manassé: Gamaliel, fils de Pedahzur.
daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11 De Benjamin: Abidan, fils de Gideoni.
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12 De Dan: Ahiezer, fils d'Ammishaddai.
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13 d'Asher: Pagiel, fils d'Ochran.
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14 De Gad: Eliasaph, fils de Deuel.
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15 Pour Nephtali: Ahira, fils d'Enan. »
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16 Voici les appelés de l'assemblée, les princes des tribus de leurs pères; ils étaient les chefs des milliers d'Israël.
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
17 Moïse et Aaron prirent ces hommes qui sont mentionnés par leur nom.
Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
18 Ils convoquèrent toute l'assemblée le premier jour du second mois, et ils déclarèrent leurs ancêtres selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, d'après le nombre des noms, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, un par un.
suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
19 Comme Yahvé l'avait ordonné à Moïse, celui-ci les compta dans le désert de Sinaï.
yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
20 Les fils de Ruben, premiers-nés d'Israël, selon leurs générations, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, d'après le nombre des noms, un par un, tous les mâles depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient en état de porter les armes.
Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
21 Ceux de la tribu de Ruben dont on fit le dénombrement furent quarante-six mille cinq cents.
Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
22 On fit le dénombrement des fils de Siméon, selon leurs générations, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, en comptant les noms, un par un, tous les mâles depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient en état de porter les armes.
Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
23 On fit le dénombrement des fils de la tribu de Siméon: cinquante-neuf mille trois cents.
Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
24 On enregistra les fils de Gad, selon leurs générations, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, en comptant les noms depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient en état de porter les armes.
Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
25 On compta quarante-cinq mille six cent cinquante hommes de la tribu de Gad.
Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
26 Des fils de Juda, selon leurs générations, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, en comptant les noms depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient propres à faire la guerre:
Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
27 ceux de la tribu de Juda dont on fit le dénombrement furent soixante-quatorze mille six cents.
Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
28 On enregistra les fils d'Issacar, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, d'après le nombre des noms, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient en état de porter les armes.
Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
29 On fit le dénombrement des fils de la tribu d'Issacar: cinquante-quatre mille quatre cents.
Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
30 On enregistra les fils de Zabulon, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, d'après le nombre des noms, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient propres à faire la guerre:
Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
31 ceux de la tribu de Zabulon dont on fit le dénombrement furent cinquante-sept mille quatre cents.
Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
32 Fils de Joseph: des fils d'Éphraïm, selon leurs générations, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, en comptant les noms depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient propres à faire la guerre:
Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
33 ceux de la tribu d'Éphraïm dont on fit le dénombrement furent quarante mille cinq cents.
Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
34 On enregistra les fils de Manassé, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, d'après le nombre des noms, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient propres à faire la guerre:
Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
35 ceux de la tribu de Manassé dont on fit le dénombrement furent trente-deux mille deux cents.
Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
36 On enregistra les fils de Benjamin, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, en comptant les noms depuis l`âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient propres à faire la guerre:
Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
37 ceux de la tribu de Benjamin dont on fit le dénombrement furent trente-cinq mille quatre cents.
Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
38 On enregistra les fils de Dan, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, d'après le nombre des noms, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient propres à faire la guerre:
Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
39 ceux de la tribu de Dan dont on fit le dénombrement furent soixante-deux mille sept cents.
Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
40 On enregistra les fils d`Aser, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, en comptant les noms depuis l`âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient propres à faire la guerre:
Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
41 ceux de la tribu d'Aser dont on fit le dénombrement furent quarante et un mille cinq cents.
Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
42 On enregistra les fils de Nephthali, selon leurs familles, selon les maisons de leurs pères, d'après le nombre des noms, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient propres à faire la guerre:
Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
43 ceux de la tribu de Nephthali dont on fit le dénombrement furent cinquante-trois mille quatre cents.
Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
44 Ce sont là ceux dont Moïse et Aaron firent le compte, et les douze hommes qui furent princes d'Israël, chacun pour sa maison de pères.
Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
45 Tous ceux des enfants d'Israël qui furent comptés selon leurs maisons de pères, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui étaient en état de porter les armes en Israël -
Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
46 tous ceux qui furent comptés furent six cent trois mille cinq cent cinquante.
Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
47 Mais les Lévites, selon la tribu de leurs pères, ne furent pas comptés parmi eux.
Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
48 Car Yahvé avait parlé à Moïse, en disant:
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
49 « Tu ne compteras pas la tribu de Lévi et tu ne la recenseras pas parmi les enfants d'Israël;
“Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
50 mais tu établiras les Lévites sur le tabernacle du témoignage, sur tout son mobilier et sur tout ce qui lui appartient. Ils porteront le tabernacle et tous ses ustensiles; ils en prendront soin et camperont autour de lui.
A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
51 Lorsque le tabernacle devra être déplacé, les Lévites le descendront; et lorsque le tabernacle devra être dressé, les Lévites le dresseront. L'étranger qui s'approchera sera mis à mort.
Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
52 Les enfants d'Israël dresseront leurs tentes, chacun selon son camp, chacun selon sa bannière, selon leurs divisions.
Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
53 Les Lévites camperont autour de la tente du Témoignage, afin qu'il n'y ait pas de colère sur l'assemblée des enfants d'Israël. Les Lévites seront responsables du Tabernacle du Témoignage. »
Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
54 Les enfants d'Israël firent ainsi. Ils firent tout ce que Yahvé avait ordonné à Moïse.
Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Nombres 1 >