< 1 Rois 13 >

1 Voici, un homme de Dieu sortit de Juda, par la parole de l'Éternel, pour se rendre à Béthel; et Jéroboam se tenait près de l'autel pour brûler des parfums.
Bisa ga umarnin Ubangiji, sai wani mutumin Allah ya zo daga Yahuda zuwa Betel, yayinda Yerobowam yake tsaye kusa da bagade don yă miƙa hadaya.
2 Il cria contre l'autel, par la parole de l'Éternel, et dit: « Autel! Autel! Autel! Yahvé dit: 'Voici qu'il va naître un fils à la maison de David, nommé Josias. Sur toi, il sacrifiera les prêtres des hauts lieux qui brûlent de l'encens, et ils brûleront sur toi des ossements d'hommes.'"
Sai mutumin Allah ya tā da murya a kan bagade bisa ga umarnin Ubangiji ya ce, “Ya bagade, bagade! Ubangiji ya ce, ‘Za a haifi ɗa mai suna Yosiya wa gidan Dawuda. A kanka zai miƙa firistoci na masujadai kan tuddai masu miƙa hadayu a nan, za a kuma ƙone ƙasusuwan mutane a kanka.’”
3 Il donna un signe le même jour, en disant: « Voici le signe que Yahvé a annoncé: Voici que l'autel se fendra et que les cendres qui sont dessus seront répandues. »
A wannan rana mutumin Allah ya ba da alama, “Ga alamar da Ubangiji ya furta. Wannan bagade zai tsage yă rabu kashi biyu, tokar da yake a kansa za tă zuba a ƙasa.”
4 Lorsque le roi entendit la parole de l'homme de Dieu, qu'il criait contre l'autel de Béthel, Jéroboam étendit sa main de l'autel, en disant: « Saisissez-le! » Sa main, qu'il avait étendue contre lui, se dessécha, de sorte qu'il ne put la ramener à lui.
Sa’ad da Yerobowam ya ji abin da mutumin Allah ya tā da murya ya faɗa game da bagaden Betel, sai ya miƙa hannunsa daga bagaden ya ce, “Ku kama shi!” Amma sai hannun da ya miƙa ya yanƙwane, har bai iya janye shi ba.
5 L'autel fut aussi fendu, et les cendres furent répandues de l'autel, selon le signe que l'homme de Dieu avait donné par la parole de l'Éternel.
Haka ma, bagaden ya rabu, tokarsa kuma ya zuba, bisa ga alamar da mutumin Allah ya bayar, ta wurin kalmar Ubangiji.
6 Le roi répondit à l'homme de Dieu: « Maintenant, intercède en faveur de l'Éternel, ton Dieu, et prie pour moi, afin que ma main me soit rendue. » L'homme de Dieu intercéda auprès de Yahvé, et la main du roi lui fut rendue à nouveau, et redevint comme avant.
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Ka roƙi Ubangiji Allahnka, ka kuma yi addu’a domina don hannuna ya warke.” Saboda haka mutumin Allah ya yi roƙo ga Ubangiji, hannun sarki kuwa ya warke, ya kuma zama kamar yadda yake a dā.
7 Le roi dit à l'homme de Dieu: « Viens chez moi et rafraîchis-toi, et je te donnerai une récompense. »
Sai sarki ya ce wa mutumin Allah, “Zo gida tare da ni, ka sami wani abu ka ci, zan kuwa yi maka kyauta.”
8 L'homme de Dieu dit au roi: « Même si tu me donnais la moitié de ta maison, je n'entrerais pas avec toi, et je ne mangerais pas de pain et ne boirais pas d'eau dans ce lieu;
Amma mutumin Allah ya amsa wa sarki, “Ko da za ka ba rabin mallakarka, ba zan tafi tare da kai ba, ba kuwa zan ci abinci, ko in sha ruwa a can ba.
9 car c'est ce que m'a ordonné la parole de l'Éternel, en disant: Tu ne mangeras pas de pain, tu ne boiras pas d'eau, et tu ne reviendras pas par le chemin par lequel tu es venu. »
Gama an umarce ni ta wurin kalmar Ubangiji, aka ce, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
10 Il prit donc un autre chemin, et ne revint pas par le chemin par lequel il était venu à Béthel.
Saboda haka ya ɗauki wata hanya, bai kuwa koma ta hanyar da ya zo Betel ba.
11 Or, un vieux prophète habitait à Béthel, et l'un de ses fils vint lui raconter toutes les œuvres que l'homme de Dieu avait faites ce jour-là à Béthel. Ils racontèrent aussi à leur père les paroles qu'il avait dites au roi.
To, fa, akwai wani tsohon annabi yana zama a Betel, wanda’ya’yansa suka zo suka faɗa masa dukan abin da mutumin Allah ya yi a can, a ranar. Suka kuma faɗa wa mahaifinsu abin da ya faɗa wa sarki.
12 Leur père leur dit: « Par où est-il allé? » Or ses fils avaient vu par où allait l'homme de Dieu, qui venait de Juda.
Mahaifinsu ya tambaye su ya ce, “Wace hanya ce ya bi?” Sai’ya’yansa suka nuna masa hanyar da mutumin Allah daga Yahuda ya bi.
13 Il dit à ses fils: « Sellez-moi l'âne. » Ils sellèrent donc l'âne pour lui, et il monta dessus.
Sai ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Da suka yi wa jakin shimfiɗa, sai ya hau.
14 Il poursuivit l'homme de Dieu, et le trouva assis sous un chêne. Il lui dit: « Es-tu l'homme de Dieu qui est venu de Juda? » Il a dit: « Je le suis. »
Ya bi bayan mutumin Allah. Ya same shi yana zama a ƙarƙashin itace oak, sai ya tambaye shi ya ce, “Kai ne mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda?” Ya amsa, “Ni ne.”
15 Et il lui dit: « Viens à la maison avec moi et mange du pain. »
Saboda haka annabin ya ce masa, “Zo gida tare da ni ka ci abinci.”
16 Il dit: « Je ne retournerai pas avec vous et je n'entrerai pas avec vous. Je ne mangerai pas de pain et ne boirai pas d'eau avec vous dans ce lieu.
Mutumin Allah ya ce, “Ba zan koma tare da kai ba, ko in ci abinci, ko in sha ruwa tare da kai a can ba.
17 Car il m'a été dit par la parole de l'Éternel: Tu ne mangeras pas de pain et tu ne boiras pas d'eau dans ce lieu, et tu ne te retourneras pas pour prendre le chemin par lequel tu es venu. »
An faɗa mini ta wurin maganar Ubangiji, ‘Kada ka ci abinci, ko ka sha ruwa a can, ko ka koma ta hanyar da ka zo.’”
18 Il lui dit: « Moi aussi, je suis prophète comme toi, et un ange m'a parlé par la parole de Yahvé, en disant: « Ramène-le chez toi, dans ta maison, pour qu'il mange du pain et boive de l'eau. » Il lui a menti.
Sai annabin ya amsa, “Ni ma annabi ne, kamar ka. Kuma mala’ika ya ce mini ta wurin kalmar Ubangiji, ‘Dawo da shi zuwa gidanka saboda yă ci abinci, yă kuma sha ruwa.’” (Amma yana masa ƙarya ne.)
19 Il s'en retourna donc avec lui, mangea du pain dans sa maison et but de l'eau.
Sai mutumin Allah ya koma tare da shi ya kuma ci ya sha a gidansa.
20 Comme ils étaient assis à table, la parole de Yahvé vint au prophète qui l'avait ramené
Yayinda suke zaune a teburi, sai maganar Ubangiji ta zo wa tsohon annabin da ya dawo da mutumin Allah.
21 et il cria à l'homme de Dieu venu de Juda: « Yahvé dit: 'Parce que tu as désobéi à la parole de Yahvé et que tu n'as pas observé le commandement que Yahvé ton Dieu t'avait prescrit,
Sai tsohon annabin ya tā da murya wa mutumin Allah wanda ya zo daga Yahuda, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ‘Ka ƙazantar da maganar Ubangiji, ba ka kuma kiyaye umarnin Ubangiji Allahnka ba.
22 mais que tu es revenu, que tu as mangé du pain et bu de l'eau dans le lieu dont il t'avait dit: « Ne mange pas de pain et ne bois pas d'eau », ton corps ne viendra pas au tombeau de tes pères.'"
Ka dawo ka ci abinci, ka kuma sha ruwa a wurin da na faɗa maka kada ka ci, ko ka sha. Saboda haka ba za a binne jikinka a kabarin kakanninka ba.’”
23 Après avoir mangé du pain et après avoir bu, il sella l'âne pour le prophète qu'il avait ramené.
Sa’ad da mutumin Allah ya gama ci da sha, sai annabin da ya dawo da shi ya yi wa jakin mutumin Allah shimfiɗa.
24 Comme il était parti, un lion le rencontra sur le chemin et le tua. Son corps fut jeté sur le chemin, et l'âne se tenait près de lui. Le lion aussi se tenait près du corps.
Yayinda yake kan hanyarsa, sai wani zaki ya sadu da shi ya kashe shi, aka kuma jefar da jikinsa a kan hanya, jakin da zakin suka tsaya kusa da gawar.
25 Voici que des gens passaient par là et voyaient le corps jeté sur le chemin et le lion qui se tenait près du corps; ils vinrent le raconter dans la ville où habitait le vieux prophète.
Waɗansu mutane masu wucewa suka ga an yar da gawar a can, zaki yana tsaye kusa da gawar, sai suka tafi suka ba da labarin a birni inda tsohon annabin nan yake zama.
26 Lorsque le prophète qui l'avait ramené du chemin l'apprit, il dit: « C'est l'homme de Dieu qui a désobéi à la parole de l'Éternel. C'est pourquoi l'Éternel l'a livré au lion, qui l'a déchiqueté et l'a tué, selon la parole que l'Éternel lui avait adressée. »
Sa’ad da annabin da ya dawo da mutumin Allah ya ji, sai ya ce, “Mutumin Allah ne, wanda ya ƙazantar da maganar Ubangiji. Ubangiji ya bashe shi ga zaki, wanda ya yayyage shi ya kuma kashe shi, kamar yadda maganar Ubangiji ta gargaɗe shi.”
27 Il dit à ses fils: « Sellez-moi l'âne », et ils le sellèrent.
Sai annabin ya ce wa’ya’yansa, “Ku yi wa jakina shimfiɗa.” Sai suka yi.
28 Il s'en alla et trouva son corps jeté sur le chemin, et l'âne et le lion debout près du corps. Le lion n'avait pas mangé le corps ni malmené l'âne.
Sai ya fita ya sami an jefar da gawar a hanya, jakin da zakin suna tsaye kusa da shi. Zakin bai ci gawar ko yă yayyage jakin ba.
29 Le prophète prit le corps de l'homme de Dieu, le mit sur l'âne et le ramena. Il se rendit dans la ville du vieux prophète pour le pleurer et l'enterrer.
Saboda haka annabin ya ɗauki gawar mutumin Allah, ya shimfiɗa shi a kan jaki, ya koma da shi cikin birninsa don yă yi makokinsa yă kuma binne shi.
30 Il mit son corps dans son propre sépulcre, et l'on pleura sur lui en disant: « Hélas, mon frère! »
Sai ya kwantar da gawar a kabarinsa, suka yi makoki a kansa, ya kuma ce, “Ayya, abokina!”
31 Après l'avoir enterré, il parla à ses fils en disant: « Quand je serai mort, enterrez-moi dans le tombeau où est enterré l'homme de Dieu. Mettez mes os à côté de ses os.
Bayan an binne shi, sai ya ce wa’ya’yansa, “Sa’ad da na mutu, ku binne ni a kabarin da aka binne mutumin Allah; ku kwantar da ƙasusuwana kusa da ƙasusuwansa.
32 Car ce qu'il a crié par la parole de Yahvé contre l'autel de Béthel et contre toutes les maisons des hauts lieux qui sont dans les villes de Samarie, arrivera certainement. »
Gama annabcin da ya yi ta maganar Ubangiji gāba da bagaden da yake cikin Betel da kuma wuraren sujada a tuddan da suke a biranen Samariya, ba shakka zai cika.”
33 Après cela, Jéroboam ne revint pas de sa mauvaise voie, mais il établit de nouveau des prêtres des hauts lieux parmi tout le peuple. Il consacrait celui qui le voulait, afin qu'il y ait des prêtres des hauts lieux.
Har ma bayan wannan, Yerobowam bai canja daga mugayen hanyoyinsa ba, amma ya ƙara naɗa firistoci domin masujadai da suke kan tuddai daga kowane irin mutane. Duk wanda ya so yă zama firist sai yă naɗa shi don aiki a masujadai da suke kan tuddai.
34 Cette chose devint un péché pour la maison de Jéroboam, au point de l'exterminer et de la faire disparaître de la surface de la terre.
Wannan ne zunubin gidan Yerobowam da ya kai ga fāɗuwarsa da kuma hallakarsa daga fuskar duniya.

< 1 Rois 13 >