< 1 Rois 12 >

1 Roboam se rendit à Sichem, car tout Israël était venu à Sichem pour le faire roi.
Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ila sun je can don su naɗa shi sarki.
2 Lorsque Jéroboam, fils de Nebath, en eut connaissance (car il était encore en Égypte, où il s'était enfui de la présence du roi Salomon, et Jéroboam vivait en Égypte;
Sa’ad da Yerobowam ɗan Nebat ya ji labari (gama har yanzu yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon), sai ya dawo daga Masar.
3 et on l'envoya chercher), Jéroboam et toute l'assemblée d'Israël vinrent et parlèrent à Roboam, en disant:
Saboda haka mutane suka aika Yerobowam yă zo, sai shi da dukan taron Isra’ila suka tafi wurin Rehobowam, suka ce masa,
4 « Ton père a rendu notre joug difficile. Maintenant donc, allège le dur service de ton père et le lourd joug qu'il nous a imposé, et nous te servirons. »
“Mahaifinka ya sa mana kaya mai nauyin gaske, amma yanzu ka sassauta wannan aiki mai zafi, da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
5 Il leur dit: « Partez pour trois jours, puis revenez vers moi. » Alors les gens sont partis.
Rehobowam ya amsa, “Ku tafi, bayan kwana uku, ku dawo.” Sai mutane suka watse.
6 Le roi Roboam consulta les vieillards qui s'étaient présentés devant Salomon, son père, de son vivant, et dit: « Quel conseil me donnez-vous pour répondre à ces gens? »
Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawa waɗanda suka yi wa mahaifinsa Solomon, hidima a kwanakinsa. Ya ce, “Wace shawara ce za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
7 Ils répondirent: « Si tu veux être aujourd'hui le serviteur de ce peuple, si tu le sers et si tu lui réponds par de bonnes paroles, alors ils seront tes serviteurs pour toujours. »
Suka amsa, “In a yau za ka zama bawan waɗannan mutane, ka kuma yi musu hidima, ka ba su amsa mai kyau, kullum za su kasance bayinka.”
8 Mais il abandonna le conseil des vieillards qu'ils lui avaient donné, et tint conseil avec les jeunes gens qui avaient grandi avec lui, et qui se tenaient devant lui.
Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawan suka ba shi, sai ya nemi shawarar matasa waɗanda suka yi girma tare, waɗanda kuma suke masa hidima.
9 Il leur dit: « Quel conseil donnez-vous, pour que nous répondions à ces gens qui m'ont parlé en disant: « Allègez le joug que votre père a mis sur nous? »".
Ya tambaye su, “Mece ce shawararku? Yaya za mu amsa wa waɗannan mutane masu cewa, ‘Ka sassauta nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
10 Les jeunes gens qui avaient grandi avec lui lui dirent: « Dis à ces gens qui t'ont parlé en disant: « Ton père a rendu notre joug lourd, mais allège-le pour nous », dis-leur: « Mon petit doigt est plus gros que la taille de mon père.
Matasan, waɗanda suka yi girma tare da shi, suka amsa, “Faɗa wa waɗannan mutanen da suka ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sassauta kayanka.’ Ka ce musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun tsohona kauri.
11 Mon père vous a chargé d'un joug lourd, mais moi, je vais ajouter à votre joug. Mon père vous a châtiés avec des fouets, mais moi, je vous châtierai avec des scorpions.'"
Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.’”
12 Jéroboam et tout le peuple se présentèrent à Roboam le troisième jour, comme le roi le leur avait demandé, en disant: « Revenez me voir le troisième jour. »
Bayan kwana uku, Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam yadda sarki ya faɗa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
13 Le roi répondit durement au peuple, abandonna le conseil des vieillards qu'ils lui avaient donné,
Sai Sarki ya amsa wa mutane da zafi. Yana ƙin shawarar da dattawa suka ba shi.
14 et leur parla selon le conseil des jeunes gens, en disant: « Mon père a rendu votre joug pesant, mais moi, j'ajouterai à votre joug. Mon père vous a châtiés avec des fouets, mais moi je vous châtierai avec des scorpions. »
Ya bi shawarar matasa, ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.”
15 Et le roi n'écouta pas le peuple, car c'était une chose provoquée par l'Éternel, afin d'affermir sa parole, que l'Éternel avait dite par Achija de Silo à Jéroboam, fils de Nebath.
Saboda haka sarki bai saurare mutane ba, gama wannan abin da ya faru daga wurin Ubangiji ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi wa Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya, mutumin Shilo.
16 Lorsque tout Israël vit que le roi ne les écoutait pas, le peuple prit la parole et dit au roi: « Quelle part avons-nous en David? Nous n'avons pas d'héritage dans le fils de Jessé. À tes tentes, Israël! Occupe-toi maintenant de ta propre maison, David. » Et Israël s'en alla vers ses tentes.
Da dukan Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, “Ina ruwanmu da Dawuda! Ai! Ba mu da gādo wurin ɗan Yesse. Ya Isra’ila, kowa yă koma tentinsa! Dawuda, sai ka lura da gidanka!” Saboda haka Isra’ilawa suka watse zuwa gida.
17 Mais quant aux enfants d'Israël qui habitaient dans les villes de Juda, Roboam régnait sur eux.
Amma ga Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da mulki a kansu.
18 Alors le roi Roboam envoya Adoram, qui était à la tête des hommes soumis au travail forcé, et tout Israël le lapida à mort. Le roi Roboam se hâta de monter sur son char, pour fuir à Jérusalem.
Sarki Rehobowam ya aiki Adoniram wanda yake shugaban aikin gandu, amma Isra’ila suka jajjefe shi da dutse har ya mutu. Sarki Rehobowam, ya sullale ya hau keken yaƙinsa ya tsere zuwa Urushalima.
19 Ainsi Israël s'est rebellé contre la maison de David jusqu'à ce jour.
Tun daga wannan ranar ne mutanen Isra’ila suka shiga gāba da gidan Dawuda har wa yau.
20 Lorsque tout Israël apprit que Jéroboam était de retour, ils l'envoyèrent appeler à l'assemblée et l'établirent roi sur tout Israël. Il n'y eut personne qui suivit la maison de David, sauf la tribu de Juda seulement.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ji Yerobowam ya dawo, sai suka aika, suka kira shi zuwa taro, suka kuma naɗa shi sarki bisa dukan Isra’ila. Kabila Yahuda kaɗai ta kasance mai biyayya ga gidan Dawuda.
21 Lorsque Roboam fut arrivé à Jérusalem, il rassembla toute la maison de Juda et la tribu de Benjamin, cent quatre-vingt mille hommes d'élite qui étaient des guerriers, pour combattre la maison d'Israël, afin de ramener la royauté à Roboam, fils de Salomon.
Da Rehobowam ya isa Urushalima, ya tattara dukan gidan Yahuda da kabilar Benyamin, ya sami sun kai mayaƙa dubu da tamanin. Sai aka shirya don su yaƙi gidan Isra’ila, su kuma mayar da masarautar wa Rehobowam ɗan Solomon.
22 Mais la parole de Dieu fut adressée à Shemaya, homme de Dieu, en ces termes:
Amma waɗannan kalmomin Allah suka zo wa Shemahiya, mutumin Allah, cewa,
23 « Parle à Roboam, fils de Salomon, roi de Juda, à toute la maison de Juda et de Benjamin, et au reste du peuple, et dis-lui:
“Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon, sarkin Yahuda, ka faɗa wa dukan gidan Yahuda da Benyamin, da kuma dukan sauran mutane,
24 « Yahvé dit: Vous ne monterez pas et vous ne combattrez pas contre vos frères, les enfants d'Israël. Chacun retournera dans sa maison, car cette chose vient de moi. »" Ils écoutèrent donc la parole de Yahvé, s'en retournèrent et poursuivirent leur chemin, selon la parole de Yahvé.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku, Isra’ilawa. Ku koma gida, kowannenku, gama wannan aikina ne.”’” Saboda haka suka yi biyayya da maganar Ubangiji, suka sāke watse zuwa gida, yadda Ubangiji ya umarta.
25 Jéroboam bâtit Sichem dans la montagne d'Ephraïm, et il y habita; puis il sortit de là et bâtit Penuel.
Sai Yerobowam ya ƙara gina Shekem a ƙasar tudu ta Efraim, ya zauna a can. Daga can ya tafi ya gina Fenuwel.
26 Jéroboam disait en son cœur: « Maintenant le royaume va revenir à la maison de David.
Yerobowam ya yi tunani a ransa ya ce, “Mai yiwuwa mulkin yă koma gidan Dawuda.
27 Si ce peuple monte pour offrir des sacrifices dans la maison de l'Éternel à Jérusalem, le cœur de ce peuple se tournera de nouveau vers son seigneur, vers Roboam, roi de Juda; il me tuera et reviendra à Roboam, roi de Juda. »
In waɗannan mutane sun riƙa haurawa don su miƙa hadayu a haikalin Ubangiji a Urushalima. Za su sāke nuna biyayya ga mai girma, Rehobowam, sarkin Yahuda. Za su kashe ni su kuma koma ga Sarki Rehobowam.”
28 Le roi tint conseil et fit deux veaux d'or, et il leur dit: « C'est trop pour vous de monter à Jérusalem. Regardez et contemplez vos dieux, Israël, qui vous ont fait monter du pays d'Égypte! »
Bayan ya nemi shawara, sai sarki ya yi siffofin’yan maruƙa biyu na zinariya. Ya ce wa mutane, “Kun daɗe kuna haurawa zuwa can Urushalima. Ga allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga ƙasar Masar.”
29 Il plaça l'un à Béthel, et l'autre à Dan.
Sai ya kafa ɗaya a Betel, ɗaya kuma a Dan.
30 Cela devint un péché, car le peuple alla jusqu'à Dan pour se prosterner devant celui qui était là.
Wannan ya zama zunubi, gama mutane suna tafiya yin wa wannan da yake a Betel sujada, su kuma je har Dan don su yi wa ɗayan sujada.
31 Il fit des maisons de hauts lieux et établit des prêtres parmi tout le peuple, qui n'étaient pas des fils de Lévi.
Yerobowam ya gina masujadai da suke kan tuddai, ya kuma naɗa firistoci barkatai daga cikin mutanen da ba na zuriyar Lawi ba.
32 Jéroboam institua une fête au huitième mois, le quinzième jour du mois, comme la fête qui a lieu en Juda, et il monta à l'autel. Il le fit à Béthel, en sacrifiant aux veaux qu'il avait faits, et il plaça à Béthel les prêtres des hauts lieux qu'il avait faits.
Ya kafa biki a rana ta goma sha biyar ta watan takwas, kamar bikin da ake yi a Yahuda, ya kuma miƙa hadayu a bisa bagade. Ya yi haka a Betel, yana miƙa wa siffofin maruƙan da ya yi hadayu. A Betel kuma ya naɗa firistoci a wuraren tudun da ya yi.
33 Il monta à l'autel qu'il avait fait à Béthel, le quinzième jour du huitième mois, au mois qu'il avait choisi de son propre cœur; il donna une fête aux enfants d'Israël, et il monta à l'autel pour brûler des parfums.
A rana ta goma sha biyar ta watan takwas, watan da ya zaɓa, ya miƙa hadayu a bisa bagaden da ya gina a Betel. Saboda haka ya kafa biki don Isra’ilawa, ya kuma haura zuwa bagade don yă miƙa hadayu.

< 1 Rois 12 >