< 1 Chroniques 26 >

1 Pour les divisions des portiers: parmi les Koréites, Meschélémia, fils de Koré, d'entre les fils d'Asaph.
Ɓangarorin Matsaran Ƙofofi su ne, Daga Korayawa, Meshelemiya ɗan Kore, ɗaya daga cikin’ya’yan Asaf maza.
2 Meschélémia eut des fils: Zacharie, premier-né, Jediaël, deuxième, Zebadia, troisième, Jathniel, quatrième,
Meshelemiya yana da’ya’ya maza. Zakariya ɗan fari, Yediyayel na biyu, Zebadiya na uku, Yatniyel na huɗu,
3 Elam, cinquième, Jehohanan, sixième, et Eliehœnaï, septième.
Elam na biyar, Yehohanan na shida da Eliyehoyenai na bakwai.
4 Obed-Edom eut des fils: Schemaeja, le premier-né, Jehozabad, le deuxième, Joach, le troisième, Sacar, le quatrième, Nethanel, le cinquième,
Obed-Edom shi ma yana da’ya’ya maza. Shemahiya ɗan fari, Yehozabad na biyu, Yowa na uku, Sakar na huɗu Netanel na biyar,
5 Ammiel, le sixième, Issachar, le septième, et Peullethai, le huitième; car Dieu l'a béni.
Ammiyel na shida, Issakar na bakwai da Feyuletai na takwas. (Gama Allah ya albarkace Obed-Edom.)
6 Des fils naquirent aussi à Schemaeja, son fils, qui régnèrent sur la maison de leur père; car ils étaient des hommes vaillants.
Ɗan Obed-Edom, wato, Shemahiya shi ma yana da’ya’ya maza, waɗanda suke shugabanni a cikin iyalin mahaifinsu, gama su jarumawa ne ƙwarai.
7 Fils de Schemaeja: Othni, Rephaël, Obed et Elzabad, dont les parents étaient des hommes vaillants, Elihu et Semachia.
’Ya’yan Shemahiya maza su ne, Otni, Rafayel, Obed da Elzabad; danginsa Elihu da Shemahiya su ma jarumawa ne.
8 Tous ceux-là étaient des fils d'Obed-Edom, avec leurs fils et leurs frères, des hommes vaillants pour le service: soixante-deux d'Obed-Edom.
Ɗaukan waɗannan zuriyar Obed-Edom ne; su da’ya’yansu maza da danginsu, jarumawa ne masu ƙarfin yin aiki. Zuriyar Obed-Edom, mutum 62 ne duka.
9 Meshelemia avait des fils et des frères, dix-huit hommes vaillants.
Meshelemiya yana da’ya’ya maza da kuma’yan’uwa, waɗanda jarumawa ne, su 18 ne duka.
10 Hosa, des fils de Merari, avait aussi des fils: Shimri, le chef (car, bien qu'il ne fût pas le premier-né, son père l'avait établi chef),
Hosa dangin Merari yana da’ya’ya maza. Shimri na fari (ko da yake ba shi ne ɗan fari ba, mahaifinsa ya sa shi na fari),
11 Hilkija, le second, Tebalia, le troisième, et Zacharie, le quatrième. Tous les fils et frères de Hosah étaient au nombre de treize.
Hilkiya ne na biyu, Tabaliya ne na uku sai kuma Zakariya na huɗu.’Ya’ya da dangin Hosa su 13 ne duka.
12 Voici les divisions des portiers, des chefs, qui avaient des fonctions comme leurs frères, pour faire le service dans la maison de l'Éternel.
Waɗannan ɓangarori na matsaran ƙofofi, ta wurin manyansu, suna da ayyukan yin hidima a haikalin Ubangiji, kamar yadda danginsu suke da shi.
13 Ils tirèrent au sort, pour chaque porte, les petits et les grands, selon les maisons de leurs pères.
Aka jefa ƙuri’u don kowace ƙofa bisa ga iyalansu, ƙarami da babba.
14 Le lot de l'est échut à Shemiah. On tira au sort pour Zacharie, son fils, conseiller avisé, et son lot sortit au nord.
Ƙuri’a don Ƙofar Gabas ta fāɗo a kan Shelemiya. Sai aka jefa ƙuri’u don ɗansa Zakariya, mai ba da shawara mai ma’ana, sai ƙuri’a ta ƙofar arewa ta fāɗo a kansa.
15 A Obed-Edom, au sud; et à ses fils, l'entrepôt.
Ƙuri’a don Ƙofar Kudu ta fāɗo a kan Obed-Edom, ƙuri’a don ɗakin ajiya kuwa ta fāɗo a kan’ya’yansa maza.
16 A Shuppim et à Hosa, à l'occident, près de la porte de Schallécheth, sur la chaussée qui monte, sentinelle en face de sentinelle.
Ƙuri’u don Ƙofar Yamma da kuma Ƙofar Shalleket a hanyar bisa suka fāɗo a kan Shuffim da Hosa. Aikin tsaro bisa ga mai tsaro.
17 A l'est, il y avait six Lévites, au nord quatre par jour, au sud quatre par jour, et pour le magasin deux et deux.
Akwai Lawiyawa shida da suke tsaron ƙofar gabas, huɗu a ƙofar kudu, huɗu kuma a ƙofar arewa, biyu-biyu suke tsaron ɗakunan ajiya.
18 Pour Parbar, à l'ouest, quatre à la chaussée, et deux à Parbar.
Game da filin waje ta yamma kuwa, akwai masu tsaro huɗu a hanya da kuma biyu a filin kansa.
19 Telles étaient les divisions des portiers, des fils des Koréites et des fils de Merari.
Waɗannan su ne ɓangarori na matsaran ƙofofi waɗanda suke zuriyar Kora da Merari.
20 Parmi les Lévites, Achija était responsable des trésors de la maison de Dieu et des trésors des objets consacrés.
’Yan’uwansu Lawiyawa kuwa su ne suke lura da ma’ajin gidan Allah da kuma baitulmali don kayayyakin da aka keɓe.
21 Les fils de Ladan, les fils des Gershonites appartenant à Ladan, les chefs de famille appartenant à Ladan, le Gershonite: Jehieli.
Ladan ɗan Gershon ne, kuma kaka ga iyalai masu yawa, har ma da iyalin ɗansa Yehiyeli,
22 Fils de Jehieli: Zetham et Joël, son frère, sur les trésors de la maison de Yahvé.
’ya’yan Yehiyeli maza su ne, Zetam da ɗan’uwansa Yowel. Su ne suke kula da ma’ajin haikalin Ubangiji.
23 Des Amramites, des Jitseharites, des Hébronites, des Uzzielites:
Daga zuriyar Amram, Izhar, mutanen Hebron da kuma Uzziyel, su ma aka ba su aiki.
24 Shebuel, fils de Gershom, fils de Moïse, était chef des trésors.
Shebuwel ɗan Gershom, daga zuriyar Musa, shi ne babban jami’i mai lura da baitulmali.
25 Ses frères: d'Éliézer, Rehabia, son fils, et Jeshaiah, son fils, et Joram, son fils, et Zichri, son fils, et Shelomoth, son fils.
Danginsa na wajen Eliyezer su ne, Rehabiya, Yeshahiya, Yoram, Zikri da Shelomit.
26 Ce Shelomoth et ses frères étaient responsables de tous les trésors des objets consacrés, que le roi David, les chefs de famille, les chefs de milliers et de centaines, et les chefs de l'armée avaient consacrés.
Shelomit da danginsa su ne suke lura da dukan baitulmali don kayayyakin da Sarki Dawuda ya keɓe, ta wajen kawunan iyalai waɗanda suke shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, da kuma wajen sauran shugabannin mayaƙa.
27 Ils consacrèrent une partie du butin gagné dans les batailles pour réparer la maison de Yahvé.
Sun keɓe waɗansu ganimar da aka kwaso a yaƙi don gyaran haikalin Ubangiji.
28 Tout ce que Samuel le voyant, Saül, fils de Kish, Abner, fils de Ner, et Joab, fils de Tseruja, avaient consacré, quiconque avait consacré quelque chose, était sous la main de Shelomoth et de ses frères.
Shelomit da’yan’uwansa suka lura da dukan abubuwan da annabi Sama’ila da Shawulu ɗan Kish, da Abner ɗan Ner, da Yowab ɗan Zeruhiya suka keɓe.
29 D'entre les Jizharites, Chenania et ses fils furent chargés des affaires extérieures d'Israël, comme officiers et comme juges.
Daga mutanen Izhar, Kenaniya da’ya’yansa maza su aka sa a ayyukan da ba na haikali ba, su suka zama manya da kuma alƙalai a bisa Isra’ila.
30 Parmi les Hébronites, Haschabia et ses frères, mille sept cents hommes vaillants, avaient la surveillance d'Israël au-delà du Jourdain, à l'ouest, pour toutes les affaires de l'Éternel et pour le service du roi.
Daga zuriyar Hebron, Hashabiya da danginsa, su jarumawa dubu ɗaya da ɗari bakwai ne, su suke lura da Isra’ila yamma da Urdun don dukan aikin Ubangiji da kuma hidimar sarki.
31 Parmi les Hébronites, Jerijah était le chef des Hébronites, selon leurs générations par maisons de pères. On les rechercha la quarantième année du règne de David, et l'on trouva parmi eux des hommes vaillants à Jazer de Galaad.
Game da zuriyar Hebron kuwa, Yeriya ne babba bisa ga tarihin zuriyar iyalansu. A shekara ta arba’in ta sarautar Dawuda, sai aka yi binciken tarihi, aka tarar jarumawa cikin zuriyar Hebron suna zama a Yazer cikin Gileyad ne.
32 Ses parents, hommes vaillants, étaient au nombre de deux mille sept cents, chefs de famille, que le roi David établit comme surveillants des Rubénites, des Gadites et de la demi-tribu des Manassites, pour tout ce qui concernait Dieu et les affaires du roi.
Yeriya yana da’yan’uwa guda dubu biyu da ɗari bakwai, jarumawa da kuma kawunan iyalai, sai Sarki Dawuda ya sa su lura da mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse game da kome da ya shafi Allah da kuma al’amuran sarki.

< 1 Chroniques 26 >