< Job 27 >

1 And Job addeth to lift up his simile, and saith: —
Ayuba kuwa ya ci gaba da magana,
2 God liveth! He turned aside my judgment, And the Mighty — He made my soul bitter.
“Na rantse da Allah mai rai, wanda ya danne mini gaskiyata, Maɗaukaki, wanda ya sa nake cikin ɗacin rai.
3 For all the while my breath [is] in me, And the spirit of God in my nostrils.
Muddin ina da rai a cikina kuma numfashin Allah yana cikin hancina,
4 My lips do not speak perverseness, And my tongue doth not utter deceit.
bakina ba zai faɗi mugun abu ba, harshena kuma ba zai yi ƙarya ba.
5 Pollution to me — if I justify you, Till I expire I turn not aside mine integrity from me.
Ba zan taɓa yarda cewa kuna da gaskiya ba; har in mutu, ba zan daina kāre mutuncina ba.
6 On my righteousness I have laid hold, And I do not let it go, My heart doth not reproach me while I live.
Zan ci gaba da adalcina, ba zan fasa ba; lamirina ba zai taɓa yashe ni ba, dukan kwanakin raina.
7 As the wicked is my enemy, And my withstander as the perverse.
“Bari maƙiyana su zama kamar mugaye, masu gāba da ni kuma su zama kamar marasa adalci.
8 For what [is] the hope of the profane, When He doth cut off? When God doth cast off his soul?
Gama wane bege marar tsoron Allah yake da shi, lokacin da aka datse shi, lokacin da Allah ya ɗauke ransa?
9 His cry doth God hear, When distress cometh on him?
Ko Allah yana sauraron kukansa lokacin da ƙunci ya auko masa?
10 On the Mighty doth he delight himself? Call God at all times?
Ko zai sami farin ciki daga Maɗaukaki? Ko zai yi kira ga Allah a kowane lokaci?
11 I shew you by the hand of God, That which [is] with the Mighty I hide not.
“Zan koya muku game da ikon Allah; ba zan ɓoye hanyoyin Maɗaukaki ba.
12 Lo, ye — all of you — have seen, And why [is] this — ye are altogether vain?
Duk kun ga wannan ku da kanku saboda haka me ya sa kuke maganganun nan marasa ma’ana?
13 This [is] the portion of wicked man with God, And the inheritance of terrible ones From the Mighty they receive.
“Ga abin da mugaye za su samu gādon da azzalumi zai samu daga Maɗaukaki.
14 If his sons multiply — for them [is] a sword. And his offspring [are] not satisfied [with] bread.
Kome yawan’ya’yansa, takobi za tă gama da su; zuriyarsa ba za su taɓa samun isashen abinci ba.
15 His remnant in death are buried, And his widows do not weep.
Waɗanda suka tsira annoba za tă kashe su, kuma gwaurayensu ba za su yi kukan mutuwarsu ba.
16 If he heap up as dust silver, And as clay prepare clothing,
Ko da yake ya tara azurfa kamar ƙasa, tufafi kuma kamar tarin ƙasa,
17 He prepareth — and the righteous putteth [it] on, And the silver the innocent doth apportion.
abin da ya tara masu adalci za su sa marasa laifi za su raba azurfarsa.
18 He hath built as a moth his house, And as a booth a watchman hath made.
Gidan da ya gina kamar gidan gizo-gizo, kamar bukkar mai tsaro.
19 Rich he lieth down, and he is not gathered, His eyes he hath opened, and he is not.
Attajiri zai kwanta, amma daga wannan shi ke nan; lokacin da zai buɗe idanunsa, kome ya tafi.
20 Overtake him as waters do terrors, By night stolen him away hath a whirlwind.
Tsoro zai kwashe shi kamar ambaliyar ruwa; Da dare iska za tă tafi da shi.
21 Take him up doth an east wind, and he goeth, And it frighteneth him from his place,
Iskar gabas za tă tafi da shi; shi ke nan ya ƙare; za tă share shi daga wurinsa.
22 And it casteth at him, and doth not spare, From its hand he diligently fleeth.
Za tă murɗe shi ba tausayi, lokacin da yake guje wa ikon iskar.
23 It clappeth at him its hands, And it hisseth at him from his place.
Zai tafa hannu yă yi tsaki yă kawar da shi daga wurinsa.”

< Job 27 >