< Psalms 114 >
1 Alleluya. In the goyng out of Israel fro Egipt; of the hous of Jacob fro the hethene puple.
Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
2 Judee was maad the halewyng of hym; Israel the power of hym.
Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
3 The see siy, and fledde; Jordan was turned abac.
Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
4 Munteyns ful out ioyeden as rammes; and litle hillis as the lambren of scheep.
duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
5 Thou see, what was to thee, for thou fleddist; and thou, Jordan, for thou were turned abak?
Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
6 Munteyns, ye maden ful out ioye as rammes; and litle hillis, as the lambren of scheep.
ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
7 The erthe was moued fro the face of `the Lord; fro the face of God of Jacob.
Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
8 Which turnede a stoon in to pondis of watris; and an hard rooch in to wellis of watris.
wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.