< Psalms 105 >

1 Alleluya. Knouleche ye to the Lord, and inwardli clepe ye his name; telle ye hise werkis among hethen men.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
2 Synge ye to hym, and seie ye salm to him, and telle ye alle hise merueylis;
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan abubuwan mamakin da ya aikata.
3 be ye preisid in his hooli name. The herte of men sekynge the Lord be glad;
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki; bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
4 seke ye the Lord, and be ye confermed; seke ye euere his face.
Ku sa rai ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
5 Haue ye mynde on hise merueilis, whiche he dide; on his grete wondris, and domes of his mouth.
Ku tuna da abubuwan mamakin da ya yi, mu’ujizansa, da kuma hukunce-hukuncen da ya zartar,
6 The seed of Abraham, his seruaunt; the sones of Jacob, his chosun man.
Ya ku zuriyar Ibrahim bawansa, Ya ku’ya’yan Yaƙub, zaɓaɓɓensa.
7 He is oure Lord God; hise domes ben in al the erthe.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; kuma hukunce-hukuncensa suna a cikin dukan duniya.
8 He was myndeful of his testament in to the world; of the word which he comaundide in to a thousynde generaciouns.
Yana tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
9 Which he disposide to Abraham; and of his ooth to Isaac.
alkawarin da ya yi da Ibrahim, rantsuwar da ya yi wa Ishaku.
10 And he ordeynede it to Jacob in to a comaundement; and to Israel in to euerlastinge testament.
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub a matsayin ƙa’ida, Isra’ila a matsayin madawwamin alkawari,
11 And he seide, I shal yiue to thee the lond of Canaan; the cord of youre eritage.
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana a matsayin rabo za ka yi gādo.”
12 Whanne thei weren in a litil noumbre; and the comelingis of hem weren ful fewe.
Sa’ad da suke kima kawai, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
13 And thei passiden fro folk in to folk; and fro a rewme in to another puple.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga masarauta zuwa wata.
14 He lefte not a man to anoye hem; and he chastiside kyngis for hem.
Bai bar kowa yă danne su ba; saboda su, ya tsawata wa sarakuna,
15 Nile ye touche my cristis; and nyle ye do wickidli among my prophetis.
“Kada ku taɓa shafaffena; kada ku yi wa annabawa lahani.”
16 And God clepide hungir on erthe; and he wastide al the stidefastnesse of breed.
Ya sauko da yunwa a kan ƙasa ya kuma lalace dukan tanadinsu na abinci;
17 He sente a man bifore hem; Joseph was seeld in to a seruaunt.
ya kuma aiki mutum a gabansu, Yusuf, da aka sayar a matsayin bawa.
18 Thei maden lowe hise feet in stockis, irun passide by his soule; til the word of him cam.
Suka raunana ƙafafunsa da sarƙa aka sa wuyansa cikin ƙarafa,
19 The speche of the Lord enflawmede him;
sai abin da ya rigafaɗi ya cika sai da maganar Ubangiji ta tabbatar da shi mai gaskiya.
20 the king sente and vnbond hym; the prince of puplis sente and delyuerede him.
Sarki ya aika aka kuma sake shi, mai mulkin mutane ya’yantar da shi.
21 He ordeynede him the lord of his hous; and the prince of al his possessioun.
Ya mai da shi shugaban gidansa, mai mulki a bisa dukan abin da ya mallaka,
22 That he schulde lerne hise princis as him silf; and that he schulde teche hise elde men prudence.
don yă umarci sarakunansa yadda ya ga dama yă kuma koya wa dattawa hikima.
23 And Israel entride in to Egipt; and Jacob was a comeling in the lond of Cham.
Sa’an nan Isra’ila ya shiga Masar; Yaƙub ya yi zama kamar baƙo a ƙasar Ham.
24 And God encreesside his puple greetli; and made hym stidefast on hise enemyes.
Ubangiji ya mai da mutanensa suka yi ta haihuwa; ya sa suka yi yawa suka fi ƙarfin maƙiyansu,
25 He turnede the herte of hem, that thei hatiden his puple; and diden gile ayens hise seruauntis.
waɗanda ya juya zukatansu su ƙi mutanensa don su haɗa baki a kan bayinsa.
26 He sent Moises, his seruaunt; thilke Aaron, whom he chees.
Ya aiki Musa bawansa, da Haruna, wanda ya zaɓa.
27 He puttide in hem the wordis of hise myraclis; and of hise grete wondris in the lond of Cham.
Suka yi mu’ujizansa a cikinsu, abubuwan mamakinsa a cikin ƙasar Ham.
28 He sente derknessis, and made derk; and he made not bitter hise wordis.
Ya aiko da duhu ya kuma sa ƙasar tă yi duhu, ba domin sun yi tawaye a kan maganarsa ba?
29 He turnede the watris of hem in to blood; and he killide the fischis of hem.
Ya mai da ruwaye suka zama jini, ya sa kifayensu suka mutu.
30 And the lond of hem yaf paddoks; in the priue places of the kyngis of hem.
Ƙasarsu ta yi ta fid da kwaɗi, waɗanda suka haura cikin ɗakunan kwana na masu mulkinsu.
31 God seide, and a fleische flie cam; and gnattis in alle the coostis of hem.
Ya yi magana, sai tarin ƙudaje suka fito, cinnaku kuma ko’ina a ƙasar.
32 He settide her reynes hail; fier brennynge in the lond of hem.
Ya mai da ruwan samansu ya zama ƙanƙara, da walƙiya ko’ina a ƙasarsu;
33 And he smoot the vynes of hem, and the fige trees of hem; and al to-brak the tree of the coostis of hem.
ya lalace inabinsu da itatuwan ɓaurensu ya ragargaza itatuwan ƙasarsu.
34 He seide, and a locuste cam; and a bruk of which was noon noumbre.
Ya yi magana, sai fāri ɗango suka fito, fāran da ba su ƙidayuwa;
35 And it eet al the hey in the lond of hem; and it eet al the fruyt of the lond of hem.
suka cinye kowane abu mai ruwan kore a cikin ƙasarsu, suka cinye amfanin gonarsu
36 And he killide ech the firste gendrid thing in the lond of hem; the firste fruitis of alle the trauel of hem.
Sa’an nan ya karkashe dukan’yan fari a cikin ƙasarsu, nunan fari na dukan mazantakarsu.
37 And he ledde out hem with siluer and gold; and noon was sijk in the lynagis of hem.
Ya fitar da Isra’ila, ɗauke da azurfa da zinariya, kuma daga cikin kabilansu babu wani da ya kāsa.
38 Egipt was glad in the goyng forth of hem; for the drede of hem lai on Egipcians.
Masar ta yi murna sa’ad da suka tafi, saboda tsoron Isra’ila ya fāɗo musu.
39 He spredde abrood a cloude, in to the hiling of hem; and fier, that it schynede to hem bi nyyt.
Ya shimfiɗa girgije kamar mayafi, da kuma wuta don ta ba su haske da dare.
40 Thei axiden, and a curlew cam; and he fillide hem with the breed of heuene.
Suka roƙa, ya kuwa ba su makware ya kuma ƙosar da su da abinci daga sama.
41 He brak a stoon, and watris flowiden; floodis yeden forth in the drye place.
Ya buɗe dutse, sai ruwa ya ɓulɓulo, kamar kogi ya gudu zuwa cikin hamada.
42 For he was myndeful of his hooli word; which he hadde to Abraham, his child.
Ya tuna da alkawarinsa mai tsarki da ya ba wa bawansa Ibrahim.
43 And he ledde out his puple in ful out ioiyng; and hise chosun men in gladnesse.
Ya fitar da mutanensa da farin ciki, zaɓaɓɓunsa da sowa ta farin ciki;
44 And he yaf to hem the cuntreis of hethen men; and thei hadden in possessioun the trauels of puplis.
ya ba su ƙasashen al’ummai, suka kuma sami gādon abin da waɗansu sun sha wahala a kai,
45 That thei kepe hise iustifiyngis; and seke his lawe.
don su kiyaye farillansa su kuma kiyaye dokokinsa. Yabo ga Ubangiji.

< Psalms 105 >