< Ezekiel 36 >

1 Forsothe thou, sone of man, profesie on the hillis of Israel; and thou schalt seie, Hillis of Israel, here ye the word of the Lord.
“Ɗan mutum, ka yi annabci wa duwatsun Isra’ila ka ce, ‘Ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji.
2 The Lord God seith these thingis, For that that the enemy seide of you, Wel! euerlastyng hiynessis ben youun to vs in to eritage;
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa abokin gāba yana magana game da ku cewa, “Yauwa! Tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu.”’
3 therefore profesie thou, and seie, The Lord God seith these thingis, For that that ye ben maad desolat, and defoulid bi cumpas, and ben maad in to eritage to othere folkis, and ye stieden on the lippe of tunge, and on the schenschipe of puple;
Saboda haka ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin sun lalace ku suka kuma maishe ku kufai marar amfani a kowane gefe saboda ku zama mallakar sauran al’ummai da kuma abin magana da tsegumi ga mutane,
4 therfor, hillis of Israel, here ye the word of the Lord God. The Lord God seith these thingis to the mounteyns, and litle hillis, to strondis, and to valeis, and to peecis of wallis left, and to citees forsakun, that ben maad bare of puplis, and ben scorned of othere folkis bi cumpas;
saboda haka, ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana faɗa wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, wa kufai da garuruwan da suka zama kango waɗanda aka washe aka wulaƙanta suka zama ganimar sauran al’ummai da suke kewaye da ku,
5 therfore the Lord God seith these thingis, For in the fier of my feruour Y spak of othere folkis, and of al Idumee, that yauen my lond in to eritage to hem silf with ioie `and al herte, and of entent, and castiden out it, to distrie it; therfor profesie thou on the erthe of Israel,
ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa cikin kishina mai ƙuna na yi magana gāba da sauran al’ummai, da kuma gāba da Edom, gama da farin ciki da reni a zukatansu suka mai da ƙasata mallakarsu don su washe wuraren kiwonta.’
6 and thou schalt seie to mounteyns, and litle hillis, to the hiynesse of hillis, and to valeis, The Lord God seith these thingis, For that that ye ben desolat, lo! Y spak in my feruour and in my strong veniaunce. For that that ye suffriden schenschipe of hethene men;
Saboda haka ka yi annabci game da ƙasar Isra’ila ka kuma ce wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al’ummai.
7 therfor the Lord God seith these thingis, Lo! Y reiside myn hond ayens hethene men, that ben in youre cumpas, that thei bere her schenschipe.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa na ɗaga hannuna sama na rantse cewa al’ummai da suke kewaye da ku za su sha ba’a.
8 Forsothe, ye hillis of Israel, brynge forth youre braunchis, and bringe ye fruit to my puple Israel; for it is niy that it come.
“‘Amma ku, ya duwatsun Isra’ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanena Isra’ila, gama ba da daɗewa ba za su komo gida.
9 For lo! Y to you, and Y schal turne to you, and ye schulen be erid, and schulen take seed.
Na damu da ku kuma zan dube ku da tausayi; za ku nome ku kuma shuka,
10 And in you I schal multiplie men, and al the hous of Israel; and citees schulen be enhabitid, and ruynouse thingis schulen be reparelid.
zan kuma riɓaɓɓanya mutane a kanku, dukan gidan Isra’ila ke nan. Za a zauna a birane a kuma sāke gina rusassun wurare.
11 And Y schal fille you with men and beestis, and thei schulen be multiplied, and schulen encreesse; and Y schal make you to dwelle as at the bigynnyng, and Y schal rewarde with more goodis than ye hadden at the bigynnyng; and ye schulen wite, that Y am the Lord.
Zan sa mutane da dabbobi su yi yawa a kanku, za su kuma ba da’ya’ya su kuma yi yawa. Zan zaunar da mutane a kanku kamar dā zan kuma sa ku wadaita fiye da dā. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
12 And Y schal brynge men on you, my puple Israel, and bi eritage thei schulen welde thee, and thou schalt be to hem in to eritage; and thou schalt no more leie to, that thou be with out hem.
Zan sa mutanena Isra’ila su yi tafiya a kanku. Za su mallake ku, za ku kuma zama gādonsu; ba za ku ƙara sa su rasa’ya’yansu ba.
13 The Lord God seith these thingis, For that that thei seien of you, Thou art a deuouresse of men, and stranglist thi folk;
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin mutane suna magana game da ku cewa, “Kun cinye mutane kuka kuma sa al’ummarku ta rasa’ya’yanta,”
14 therfor thou schalt no more ete men, and thou schalt no more sle thi folk, seith the Lord God.
saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ko ku sa al’ummarku ta rasa’ya’ya ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 And Y schal no more make herd in thee the schenschipe of hethene men, and thou schalt no more bere the schenschipe of puplis, and thou schalt no more leese thi folk, seith the Lord God.
Ba zan ƙara bari ku ji maganar banza ta al’ummai ba, ba kuwa za ku ƙara shan ba’ar mutane ko in sa al’ummarku ta fāɗi ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
16 And the word of the Lord was maad to me, and he seide, Thou,
Maganar Ubangiji ta sāke zuwa mini cewa,
17 sone of man, the hous of Israel dwelliden in her lond, and thei defouliden it in her weies, and in her studies; bi the vnclennesse of a womman in rotun blood the weie of hem is maad bifor me.
“Ɗan mutum, sa’ad da mutanen Isra’ila suke zama a ƙasarsu, sun ƙazantar da ita ta wurin halinsu da kuma ayyukansu. Halinsu ya yi kamar rashin tsarkin mace a lokacin al’adarta a gabana.
18 And Y schedde out myn indignacioun on hem, for blood which thei schedden on the lond, and in her idols thei defouliden it.
Saboda haka na husata da su domin sun yi kisankai a ƙasar kuma domin sun ƙazantar da ita da gumakansu.
19 And Y scateride hem among hethene men, and thei weren wyndewid to londis; Y demede hem bi the weies and fyndyngis of hem.
Na warwatsa su cikin al’ummai, suka kuwa warwatsu cikin dukan ƙasashe; na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu.
20 And thei entriden to hethene men, to whiche thei entriden, and defouliden myn hooli name, whanne it was seid of hem, This is the puple of the Lord, and thei yeden out of the lond of hym.
Kuma ko’ina da suka tafi a cikin al’ummai sun ɓata sunana mai tsarki, gama an yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan mutanen Ubangiji ne, duk da haka dole su bar ƙasarsa.’
21 And Y sparide myn hooli name, which the hous of Israel hadde defoulid among hethene men, to whiche thei entriden.
Na damu saboda sunana mai tsarki, wanda gidan Isra’ila ya ɓata a cikin al’ummai inda suka tafi.
22 Therfor thou schalt seie to the hous of Israel, The Lord God seith these thingis, O! ye hous of Israel, not for you Y schal do, but for myn hooli name, which ye defouliden among hethene men, to whiche ye entriden.
“Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba dominku ba ne, ya gidan Isra’ila da nake yin waɗannan abubuwa, amma saboda sunana ne mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al’ummai inda kuka tafi.
23 And Y schal halewe my greet name, which is defoulid among hethene men, whiche ye defouliden in the myddis of hem; that hethene men wite, that Y am the Lord, seith the Lord of oostis, whanne Y schal be halewid in you before hem.
Zan nuna tsarkin girman sunana, wanda aka ɓata a cikin al’umma, sunana da kuka ɓata a cikinsu. Sa’an nan al’ummai za su san cewa ni ne Ubangiji, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinku a idanunsu.
24 For Y schal take awei you fro hethene men, and Y schal gadere you fro alle londis, and Y schal brynge you in to youre lond.
“‘Gama zan fitar da ku daga al’ummai; zan tattara ku daga dukan ƙasashe in komo da ku zuwa ƙasarku.
25 And Y schal schede out clene watir on you, and ye schulen be clensid fro alle youre filthis; and Y schal clense you fro alle youre idols.
Zan yayyafa muku ruwa mai tsabta, zan kuwa tsarkake ku daga dukan ƙazantarku daga kuma dukan gumakanku.
26 And Y schal yyue to you a newe herte, and Y schal sette a newe spirit in the myddis of you; and Y schal do awei an herte of stoon fro youre fleisch, and Y schal yyue to you an herte of fleisch,
Zan ba ku sabuwa zuciya in kuma sa sabon ruhu a cikinku; zan fid da zuciyar dutse in kuma ba ku zuciyar nama.
27 and Y schal sette my spirit in the myddis of you. And Y schal make that ye go in my comaundementis, and kepe and worche my domes.
Zan kuma sa Ruhuna a cikinku in kuma motsa ku ku bi ƙa’idodina ku kuma kiyaye dokokina.
28 And ye schulen dwelle in the lond, whiche Y yaf to youre fadris; and ye schulen be in to a puple to me, and Y schal be in to a God to you.
Za ku zauna a ƙasar da na ba wa kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
29 And Y schal saue you fro alle youre filthis; and Y schal clepe wheete, and Y schal multiplie it, and Y schal not put hungur on you.
Zan cece ku daga dukan rashin tsabtarku. Zan sa hatsi ya yi yalwa ba zan kawo yunwa a kanku ba.
30 And Y schal multiplie the fruyt of tree, and the seedis of the feeld, that ye bere no more the schenschipe of hungur among hethene men.
Zan ƙara’ya’yan itatuwa da amfanin gona, saboda kada ku ƙara shan kunya a cikin al’ummai saboda yunwa.
31 And ye schulen haue mynde on youre worste weies, and on studies not goode; and youre wickidnessis, and youre grete trespassis schulen displese you.
Sa’an nan za ku tuna mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda zunubanku da kuma ayyukanku na banƙyama.
32 Not for you Y schal do, seith the Lord God, be it knowun to you; O! the hous of Israel, be ye schent, and be ye aschamed on youre weies.
Ina so ku san cewa ba na yi wannan saboda ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku ji kunya ku kuma giggita saboda halinku, ya gidan Isra’ila!
33 The Lord God seith these thingis, In the dai in which Y schal clense you fro alle youre wickidnessis, and Y schal make citees to be enhabitid, and Y schal reparele ruynouse thingis,
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na tsarkake ku daga dukan zunubanku, zan sāke zaunar da ku a garuruwanku, a kuma sāke gina kufai.
34 and the desert lond schal be tilid, that was sum tyme desolat, bifor the iyen of ech weiegoere,
Ƙasar da take kango a dā za ku nome ta a maimakon zama kango a idon dukan masu ratsawa a cikinta.
35 thei schulen seie, Thilke lond vntilid is maad as a gardyn of likyng, and citees forsakun and destitute and vndur myned saten maad strong; and hethene men,
Za su ce, “Wannan ƙasar da take kango a dā ta zama kamar lambu Eden; biranen da dā suke kufai, kango da kuma aka lalata, yanzu suna da katanga ana kuma zama a ciki.”
36 whiche euer ben left in youre cumpas, schulen wite, that Y the Lord haue bildid distried thingis, and Y haue plauntid vntilid thingis; Y the Lord spak, and Y dide.
Sa’an nan al’ummai kewaye da ku da suka rage za su san cewa Ni Ubangiji na sāke gina abin da aka lalace na kuma sāke shuka abin da yake kango. Ni Ubangiji na faɗa, kuma zan aikata.’
37 The Lord God seith these thingis, Yit in this thing the hous of Israel schulen fynde me, that Y do to hem; Y schal multiplie hem as the floc of men, as an hooli floc,
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa har yanzu zan ji roƙon gidan Isra’ila in kuma yi musu wannan. Zan sa mutanensu su yi yawa kamar tumaki,
38 as the floc of Jerusalem in the solempnytees therof, so the citees that ben forsakun, schulen be fulle of the flockis of men; and thei schulen wite, that Y am the Lord.
yawansu ya yi kamar garken tumaki don hadaya a Urushalima a ƙayyadaddun lokuta bukukkuwarta. Haka biranen da suke kufai za su cika da ɗumbun mutane. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ezekiel 36 >