< Ezekiel 18 >
1 And the word of the Lord was maad to me,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 and he seide, What is it, that ye turnen a parable among you in to this prouerbe, in the lond of Israel, and seien, Fadris eeten a bittir grape, and the teeth of sones ben an egge, ether astonyed?
“Me ku mutane kuke nufi da faɗar wannan karin magana a kan ƙasar Isra’ila cewa, “‘Ubanni sun ci’ya’yan inabi masu tsami, haƙoran’ya’ya kuwa sun mutu’?
3 Y lyue, seith the Lord God, this parable schal no more be in to a prouerbe to you in Israel.
“Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, ba za ku ƙara faɗar wannan karin magana a Isra’ila ba.
4 Lo! alle soulis ben myne; as the soule of the fadir, so and the soule of the sone is myn. Thilke soule that doith synne, schal die.
Gama kowane mai rai nawa ne, mahaifi da ɗa, duk nawa ne. Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu.
5 And if a man is iust, and doith doom and riytfulnesse,
“A ce akwai mai adalci wanda yake aikata abin da yake daidai da kuma gaskiya;
6 etith not in hillis, and reisith not hise iyen to the idols of the hous of Israel; and defoulith not the wijf of his neiybore, and neiyeth not to a womman defoulid with vncleene blood;
ba ya cin abinci a duwatsun tsafi ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Ba ya ƙazantar da matar maƙwabcinsa ko ya kwana da mace lokacin al’adarta ba.
7 and makith not a man sori, yeldith the wed to the dettour, rauyschith no thing bi violence, yyueth his breed to the hungri, and hilith a nakid man with a cloth;
Ba ya cin zalin wani, amma yakan mayar wa wanda ya ba shi jingina abin da ya jinginar masa. Ba ya yi fashi amma yakan ba wa mayunwata abinci ya kuma tanada wa marasa tufafi riga.
8 leeneth not to vsure, and takith not more; turneth awei his hond fro wickidnesse, and makith trewe dom bitwixe man and man;
Ba ya ba da bashi da ruwa ko ya karɓa ƙarin riba. Yakan janye hannunsa daga aikata mugunta yakan kuma yi shari’a cikin gaskiya tsakanin mutum da mutum.
9 and goith in my comaundementis, and kepith my domes, that he do treuthe; this is a iust man, he schal lyue in lijf, seith the Lord God.
Yana bin ƙa’idodina yana kuma kiyaye dokokina da aminci. Wannan mutumin adali ne; tabbatacce zai rayu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
10 That if he gendrith a sone, a theef, shedinge out blood,
“A ce yana da ɗa wanda yana kisa ko yana yin ɗaya daga cikin waɗannan abubuwa
11 and doith oon of thes thingis, and sotheli not doing alle these thingis, but etinge in hillis, and defoulynge the wijf of his neiybore;
(ko da yake mahaifin bai yi ko ɗaya daga cikinsu ba). “Yakan ci abinci a duwatsun tsafi. Yakan ƙazantar da matar maƙwabci.
12 makynge soreuful a nedy man and pore, rauyschynge raueyns, not yeldinge a wed, reisynge hise iyen to idols, doynge abhomynacioun; yiuynge to vsure, and takynge more;
Yakan ci zalin matalauta da mabukata. Yakan yi fashi. Ba ya mayar da abin da aka jinginar masa. Ya dogara ga gumaka. Yana aikata ayyukan banƙyama.
13 whether he schal lyue? he schal not lyue; whanne he hath do alle these abhomynable thingis, he schal die bi deth, his blood schal be in hym.
Yakan ba da bashi da ruwa ya kuma karɓi riba mai yawa. Irin wannan mutum zai rayu? Ba zai rayu ba! Domin ya aikata dukan waɗannan abubuwa masu banƙyama, tabbatacce za a kashe shi, kuma hakkin jininsa zai zauna a kansa.
14 That if he gendrith a sone, which seeth alle the synnes of his fadir, whiche he dide, and dredith, and doith noon lijk tho;
“Amma a ce wannan ɗa yana da ɗa wanda ya ga dukan zunuban da mahaifinsa yake aikata, kuma ko da yake ya gan su, bai yi ko ɗaya daga cikin irin abubuwan nan ba, wato,
15 etith not on hillis, and reisith not hise iyen to the idols of the hous of Israel; and defoulith not the wijf of his neiybore,
“Bai ci abinci a duwatsun tsafi ba ko ya dogara ga gumakan gidan Isra’ila. Bai ƙazantar da matar maƙwabcinsa ba.
16 and makith not sori a man, witholdith not a wed, and rauyschith not raueyn, yyueth his breed to the hungri, and hilith the nakid with a cloth;
Bai ci zalin wani ko ya karɓi jingina ba. Ba ya fashi amma yakan ba da abincinsa ga mayunwata ya tanada tufafi wa marasa tufafi.
17 turneth a wei his hond fro the wrong of a pore man, takith not vsure and ouerhabundaunce, `that is, no thing more than he lente, and doith my domes, and goith in my comaundementis; this sone schal not die in the wickidnesse of his fadir, but he schal lyue in lijf.
Yakan janye hannunsa daga zunubi ba ya kuma ba da bashi da ruwa ko karɓan riba da yawa. Yakan kiyaye dokokina ya kuma bi ƙa’idodina. Ba zai mutu saboda zunubin mahaifinsa ba; tabbatacce zai rayu.
18 For his fadir made fals caleng, and dide violence to his brother, and wrouyte yuel in the myddis of his puple, lo! he is deed in his wickidnesse.
Amma mahaifinsa zai mutu saboda zunubinsa, domin ya yi ƙwace, ya yi wa ɗan’uwansa fashi ya kuma yi abin da ba daidai ba a cikin mutanensa.
19 And ye seien, Whi berith not the sone the wickidnesse of the fadir? That is to seie, for the sone wrouyte doom and riytfulnesse, he kepte alle my comaundementis, and dide tho, he schal lyue in lijf.
“Duk da haka kukan yi tambaya, ‘Me ya sa ɗan ba zai sami rabo a laifin mahaifinsa ba?’ Da yake ɗan ya yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina, tabbatacce zai rayu.
20 Thilke soule that doith synne, schal die; the sone schal not bere the wickidnesse of the fadir, and the fadir schal not bere the wickednesse of the sone; the riytfulnesse of a iust man schal be on hym, and the wickidnesse of a wickid man schal be on hym.
Mutumin da ya yi zunubi shi zai mutu. Ɗa ba zai sami rabo a laifin mahaifi ba, mahaifi ba zai sami rabo a laifi ɗa ba. Adalcin adali zai zama nasa, muguntar mugu za tă koma kansa.
21 Forsothe if a wickid man doith penaunce of alle hise synnes whiche he wrouyte, and kepith alle myn heestis, and doith dom and riytfulnesse, he schal lyue bi lijf, and schal not die.
“Amma in mugun mutum ya juya daga dukan zunubin da ya aikata ya kuma kiyaye dukan ƙa’idodina ya kuwa yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
22 Y schal not haue mynde of alle his wickidnessis whiche he wrouyte; he schal lyue in his riytfulnesse which he wrouyte.
Babu laifin da ya yi da za a tuna da su. Saboda abubuwan adalcin da ya aikata, zai rayu.
23 Whether the deth of the wickid man is of my wille, seith the Lord God, and not that he be conuertid fro his weies, and lyue?
Ina jin daɗin mutuwar mugu ne? In ji Ubangiji Mai Iko Duka. A maimako, ban fi jin daɗi sa’ad da suka juyo daga hanyoyinsu suka rayu ba?
24 Forsothe if a iust man turneth awey hym silf fro his riytfulnesse, and doith wickidnesse bi alle hise abhomynaciouns, which a wickid man is wont to worche, whether he schal lyue? Alle hise riytfulnessis whiche he dide, schulen not be had in mynde; in his trespassyng bi which he trespasside, and in his synne which he synnede, he schal die in tho.
“Amma in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya yi zunubi ya kuma aikata abubuwa masu banƙyamar da mugun mutum ke aikatawa, zai rayu? Babu abubuwan adalcin da ya aikata da za a tuna da su. Saboda rashin amincinsa da kuma saboda zunubai da ya yi, zai mutu.
25 And ye seiden, The weie of the Lord is not euene. Therfor, the hous of Israel, here ye, whether my weie is not euene, and not more youre weies ben schrewid?
“Duk da haka kun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Ka ji, ya gidan Isra’ila. Hanyata ba daidai ba ce?
26 For whanne a riytful man turneth awei hym silf fro his riytfulnesse, and doith wickidnesse, he schal die in it, he schal die in the vnriytwisnesse which he wrouyte.
In mai adalci ya juye daga adalcinsa ya yi zunubi, zai mutu saboda wannan; saboda zunubin da ya yi, zai mutu.
27 And whanne a wickid man turneth awei him silf fro his wickidnesse which he wrouyte, and doith dom and riytfulnesse, he schal quykene his soule.
Amma in mugun mutum ya juye daga muguntarsa ya kuma yi abin da yake daidai da kuma gaskiya, zai ceci ransa.
28 For he biholdinge and turnynge awei hym silf fro alle hise wickidnessis which he wrouyte, schal lyue in lijf, and schal not die.
Domin ya lura da dukan laifofin da ya yi ya kuma juye daga gare su, tabbatacce zai rayu; ba zai mutu ba.
29 And the sones of Israel seien, The weie of the Lord is not euene. Whether my weies ben not euene, ye hous of Israel, and not more youre weies ben schrewid?
Duk da haka mutanen Isra’ila sun ce, ‘Hanyar Ubangiji ba daidai ba ce.’ Hanyoyina ba daidai ba ne, ya gidan Isra’ila? Ba hanyoyinku ne ba daidai ba?
30 Therfor, thou hous of Israel, Y schal deme ech man bi hise weies, seith the Lord God. Turne ye togidere, and do ye penaunce for alle youre wickidnessis, and wickidnesse schal not be to you in to falling.
“Saboda haka, ya gidan Isra’ila, zan hukunta ku, kowa bisa ga hanyarsa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba! Ku juye daga dukan laifofinku; sa’an nan zunubi ba zai zama sanadin fāɗuwarku ba.
31 Caste awei fro you alle youre trespassingis, bi whiche ye trespassiden, and make ye a newe herte and a newe spirit to you, and whi schulen ye die, the hous of Israel?
Ku raba kanku da dukan laifofin da kuka yi, ku sami sabuwar zuciya da sabon ruhu. Don me za ku mutu, ya gidan Isra’ila?
32 For Y nyle the deeth of hym that dieth, seith the Lord God; turne ye ayen, and lyue ye.
Gama ba na jin daɗin mutuwar wani, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku tuba don ku rayu!