< Ezekiel 3 >
1 And he seide to me, Sone of man, ete thou what euer thing thou fyndist, ete thou this volym; and go thou, and speke to the sones of Israel.
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ci abin da yake a gabanka, ka ci wannan littafi; sa’an nan ka tafi ka yi magana wa gidan Isra’ila.”
2 And Y openyde my mouth, and he fedde me with that volym.
Saboda haka na buɗe bakina, ya kuma ba ni littafin in ci.
3 And he seide to me, Sone of man, thi wombe schal ete, and thin entrails schulen be fillid with this volym, which Y yyue to thee. And Y eet it, and it was maad as swete hony in my mouth.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ci wannan littafin da nake ba ka, ka kuma cika cikinka da shi.” Sai na ci shi, ya kuma yi zaki kamar zuma a bakina.
4 And he seide to me, Sone of man, go thou to the hous of Israel, and thou schalt speke my wordis to hem.
Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka tafi gidan Isra’ila ka faɗa kalmomina gare su.
5 For thou schalt not be sent to a puple of hiy word, and of vnknowun langage; thou schalt be sent to the hous of Israel,
Ba ina aikan ka wurin mutanen da suke da baƙon harshe da kuma yare mai wuya ba ne, amma zuwa ga gidan Isra’ila ne,
6 nether to many puplis of hiy word, and of vnknowun langage, of whiche thou maist not here the wordis. And if thou were sent to hem, thei schulden here thee.
ba ga mutane da yawa na baƙon harshe da yare mai wuya, waɗanda ba ka san kalmominsu ba. Tabbatacce da na aike ka wurin irinsu, da sun saurare ka.
7 But the hous of Israel nylen here thee, for thei nylen here me. For al the hous of Israel is of vnschamefast forheed, and of hard herte.
Amma gidan Isra’ila ba sa niyya su saurare ka domin ba sa niyya su saurare ni, gama dukan gidan Isra’ila sun taurare suna kuma kin ji.
8 Lo! Y yaf thi face strongere than the faces of hem, and thi forheed hardere than the forheedis of hem.
Amma zan sa ka zama mai taurinkai da taurin zuciya kamar su.
9 Y yaf thi face as an adamaunt, and as a flynt; drede thou not hem, nether drede thou of the face of hem, for it is an hous terrynge to wraththe.
Zan sa goshinka ya zama da tauri kamar dutse, da tauri fiye da dutsen ƙanƙara ƙarfi. Kada ka ji tsoronsu ko ka firgita ta wurinsu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.”
10 And he seide to me, Sone of man, take in thin herte, and here with thin eeris alle these my wordis, whiche Y speke to thee.
Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ji da kyau ka kuma lura da dukan kalmomin da nake maka magana.
11 And go thou, and entre to the passyng ouer, to the sones of thi puple. And thou schalt speke to hem, and thou schalt seie to hem, The Lord God seith these thingis, if perauenture thei heren, and resten.
Ka tafi yanzu zuwa ga’yan’uwanka waɗanda suke zaman bauta ka yi musu magana. Ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa,’ ko ku ji, ko kada ku ji.”
12 And the spirit took me, and Y herde after me the vois of a greet mouyng. The blessid glorie of the Lord was herd fro his place;
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama, a bayana na ji wata karar babban motsi na cewa, Bari a yabi ɗaukakar Ubangiji a wurin zamansa!
13 and Y herde the vois of wyngis of the beestis smytynge oon an othir, and the vois of wheelis suynge the beestis, and the vois of greet stiryng.
Karar fikafikan rayayyun halittun nan ne suke goge junansu da kuma karar da’irorin nan da suke kusa da su, ƙarar babban motsi.
14 Also the spirit reiside me, and took me. And Y yede forth bittir in the indignacioun of my spirit; for the hond of the Lord was with me, and coumfortide me.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma tafi da ni, na kuwa tafi da ɓacin rai da kuma fushin ruhuna, tare da hannu mai ƙarfi na Ubangiji a bisa na.
15 And Y cam to the passyng ouer, to the heep of newe fruytis, to hem that dwelliden bisidis the flood Chobar. And Y sat where thei saten, and Y dwellide there seuene daies, weilynge, in the myddis of hem.
Na zo wurin masu zaman bautan da suke zama a Tel Abib kusa da Kogin Kebar, A can kuwa, inda suke zama, na zauna a cikinsu kwana bakwai, ina mamaki.
16 Forsothe whanne seuene daies weren passid, the word of the Lord was maad to me, and seide, Sone of man,
A ƙarshen kwana bakwai ɗin maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
17 Y yaf thee `a spiere to the hous of Israel. And thou schalt here of my mouth a word, and thou schalt telle to hem of me.
“Ɗan mutum, na mai da kai mai tsaro don gidan Isra’ila; saboda haka ka ji maganar da zan yi ka kuma yi musu kashedin nan da ya fito daga gare ni.
18 If whanne Y seie to the wickid man, Thou schalt die bi deth, thou tellist not to hym, and spekist not to hym, that he be turned fro his wickid weie, and lyue; thilke wickid man schal die in his wickidnesse, but Y schal seke his blood of thin hond.
In na ce wa mugu, ‘Lalle za ka mutu,’ ba ka kuwa yi masa kashedi ko ka tsawata masa a kan mugayen hanyoyinsa don yă ceci ransa ba, wannan mugun zai mutu saboda zunubinsa, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
19 Forsothe if thou tellist to the wickid man, and he is not conuertid fro his wickidnesse, and fro his wickid weie; sotheli he schal die in his wickidnesse, but thou hast delyuerid thi soule.
Amma in ka yi wa mugun kashedi bai kuwa juya daga mugayen hanyoyinsa ba, zai mutu saboda zunubinsa; amma kai kam za ka kuɓuta.
20 But also if a iust man is turned fro his riytfulnesse, and doith wickidnesse, Y schal sette an hirtyng bifor hym; he schal die, for thou teldist not to hym; he schal die in his synne, and hise riytfulnessis, whiche he dide, schulen not be in mynde, but Y schal seke his blood of thin hond.
“Har yanzu, in mai adalci ya juya daga adalcinsa ya aikata mugunta, na kuma sa abin tuntuɓe a gabansa, zai mutu. Da yake ba ka yi masa kashedi ba, zai mutu saboda zunubinsa. Ba za a tuna da abin adalcin da ya yi ba, zan kuwa nemi hakkin jininsa a hannunka.
21 Forsothe if thou tellist to a iust man, that a iust man do not synne, and he doith not synne, he lyuynge schal lyue, for thou teldist to hym, and thou hast delyuered thi soule.
Amma in ka yi wa mai adalcin kashedi kada yă yi zunubi bai kuwa yi zunubi ba, tabbatacce zai rayu saboda ya ji kashedin, kuma kai kam za ka kuɓuta.”
22 And the hond of the Lord was maad on me, and he seide to me, Rise thou, and go out in to the feeld, and there Y schal speke with thee.
Hannun Ubangiji ya kasance a kaina a can, ya kuma ce mini, “Tashi ka fita zuwa fili, a can kuwa zan yi maka magana.”
23 And Y roos, and yede out in to the feeld. And lo! the glorie of the Lord stood there, as the glorie which Y siy bisidis the flood Chobar; and Y felle doun on my face.
Saboda haka na tashi da tafi fili. Ɗaukakar Ubangiji kuwa ta tsaya a can, kamar ɗaukakar da na gani kusa da Kogin Kebar, sai na fāɗi rubda ciki.
24 And the spirit entride in to me, and settide me on my feet. And he spak to me, and seide to me, Entre thou, and be thou closid in the myddis of thin hous.
Sai Ruhu ya sauko a kaina ya kuma ɗaga ni na tsaya a ƙafafuna. Ya yi mini magana ya ce, “Ka fita, ka rufe kanka a cikin gida.
25 And thou, sone of man, lo! boondis ben youun on thee, and thei schulen bynde thee with tho, and thou schalt not go out in the myddis of hem.
Kuma kai, ɗan mutum, za su ɗaura ka da igiyoyi; za a daure ka yadda ba za ka iya fita a cikin mutane ba.
26 And Y schal make thi tunge to cleue to the roof of thi mouth, and thou schalt be doumbe, and thou schalt not be as a man rebuykinge; for it is an hous terrynge to wraththe.
Zan sa harshenka ya manne wa dasashinka don ka yi shiru ka kuma kāsa tsawata musu, ko da yake su gidan’yan tawaye ne.
27 But whanne Y schal speke to thee, Y schal opene thi mouth, and thou schalt seie to hem, The Lord God seith these thingis, He that herith, here, and he that restith, reste; for it is an hous terrynge to wraththe.
Amma sa’ad da na yi maka magana, zan buɗe bakinka za ka kuwa faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya faɗa.’ Duk mai ji ya ji, kuma duk wanda ya ƙi ji, ya ƙi ji; gama su gida ne na’yan tawaye.