< Daniel 10 >

1 In the thridde yeer of the rewme of Sirus, kyng of Perseis, a word was schewid to Danyel, Balthasar bi name; and a trewe word, and greet strengthe, and he vndurstood the word; for whi vndurstondyng is nedeful in visioun.
A shekara ta uku ta Sairus sarkin Farisa, sai aka ba wa Daniyel (wanda ake kira Belteshazar) wahayi. Saƙon kuwa gaskiya ce wadda take tattare da babban yaƙi. Fahimtar saƙon ya zo masa a cikin wahayi.
2 In tho daies Y, Danyel, mourenyde bi the daies of thre woukis;
A wannan lokaci ni Daniyel na yi makoki har na sati uku.
3 Y eet not desirable breed, and fleisch, and wyn entride not into my mouth, but nethir Y was anoynted with oynement, til the daies of thre woukis weren fillid.
Ban ci abinci mai kyau ba; ba nama ko ruwa inabin da ya shiga bakina; kuma ba na amfani da man shafawa gaba ɗaya har sai da sati nan uku suka wuce.
4 Forsothe in the foure and twentithe dai of the firste monethe, Y was bisidis the greet flood, which is Tigris.
A rana ta ashirin da huɗu ga watan farko, a sa’ad da nake tsaye a bakin babban kogi, Tigris,
5 And Y reiside myn iyen, and Y siy, and lo! o man was clothid with lynun clothis, and hise reynes weren gird with schynynge gold;
na ɗaga kaina na duba sai ga wani mutum tsaye sanye da rigar lilin, ya yi ɗamara da zinariya zalla daga Ufaz kewaye da ƙugunsa.
6 and his bodi was as crisolitus, and his face was as the licnesse of leit, and hise iyen weren as a brennynge laumpe, and hise armes and tho thingis that weren bynethe til to the feet weren as the licnesse of bras beynge whijt, and the vois of hise wordis was as the vois of multitude.
Jikinsa kamar lu’ulu’u yake, fuskarsa kuma kamar walƙiya, idanunsa kamar harshen wuta, hannuwansa da ƙafafunsa kamar gogaggiyar tagulla, muryarsa kuma kamar amon babban taron jama’a.
7 Forsothe Y, Danyel, aloone siy the visioun; certis the men that weren with me, sien not, but ful greet ferdfulnesse felle yn on hem, and thei fledden in to an hid place.
Ni, Daniyel, kaɗai ne na ga wahayin; mutanen da suke tare da ni ba su gani ba, amma wata irin babbar razana ta auko musu har suka gudu suka ɓuya.
8 But Y was left aloone, and Y siy this greet visioun, and strengthe dwellide not in me; but also my licnesse was chaungid in me, and Y was stark, and Y hadde not in me ony thing of strengthis.
Sai aka bar ni ni kaɗai, ina juyayi wannan babban wahayi, ba ni da sauran ƙarfi, fuskata ta yamutse kuma ba ni da sauran ƙarfi.
9 And Y herde the vois of hise wordis, and Y herde, and lay astonyed on my face, and my face cleuyde to the erthe.
Sai na ji yana magana, da ina sauraronsa, sai na shiga barci mai nauyi, na kuwa fāɗi rubda ciki.
10 And lo! an hond touchide me, and reiside me on my knees, and on the toes of my feet.
Sai hannu ya taɓa ni ya sa makyarkyata a hannuna da ƙafafuna.
11 And he seide to me, Thou, Danyel, a man of desiris, vndurstonde the wordis whiche Y speke to thee, and stonde in thi degree; for now Y am sent to thee. And whanne he hadde seid this word to me, Y stood quakynge.
Sai ya ce, “Daniyel, kai ne wanda ake ƙauna sosai, ka yi lura da kyau game da kalmomin da zan yi maka magana a kansu, ka tashi yanzu, gama an aiko ni a gare ka.” Sa’ad da ya faɗa mini haka, sai na tashi a tsaye ina rawan jiki.
12 And he seide to me, Danyel, nyle thou drede, for fro the firste dai in which thou settidist thin herte to vndurstonde, that thou schuldist turmente thee in the siyt of thi God, thi wordis weren herd, and Y cam for thi wordis.
Sai ya ci gaba da cewa, “Kada ka ji tsoro, Daniyel. Gama tun daga ran da ka fara sa zuciya ga neman ganewa, ka kuma ƙasƙantar da kanka a gaban Allahnka, an ji addu’arka, amsar addu’arka ce ta kawo ni.
13 Forsothe the prince of the rewme of Perseis ayenstood me oon and twenti daies, and lo! Myyhel, oon of the firste princes, cam in to myn help, and Y dwellide stille there bisidis the kyng of Perseis.
Amma mai mulkin masarautar Farisa ya tsare ni har kwana ashirin da ɗaya. Sai da Mika’ilu, ɗaya daga cikin manya shugabanni, ya zo ya taimake ni, saboda an tsare ni a can tare da sarkin Farisa.
14 Forsothe Y am comun to teche thee, what thingis schulen come to thi puple in the laste daies; for yit the visioun is delaied in to daies.
Yanzu na zo domin in bayyana maka abin da zai faru da mutanenka nan gaba, gama wahayin ya shafi lokacin da bai riga ya zo ba ne.”
15 And whanne he spak to me bi siche wordis, Y castide doun my cheer to erthe, and was stille.
Yayinda yake faɗin mini haka, sai na sunkuyar da kaina ƙasa shiru, ba magana.
16 And lo! as the licnesse of sone of man touchide my lippis; and Y openyde my mouth, and spak, and seide to hym that stood bifore me, My Lord, in thi siyt my ioynctis ben vnknit, and no thing of strengthis dwellide in me.
Sai wani wanda ya yi kama da mutum ya taɓa leɓunana, na kuma buɗe bakina sai na fara magana. Na ce wa wannan da yake tsaye a gabana, “Na cika da azaba saboda wannan wahayi, ranka yă daɗe, ina kuma neman taimako.
17 And hou schal the seruaunt of my Lord mow speke with my Lord? no thing of strengthis dwellide in me, but also my breeth is closyde bitwixe.
Yaya ni bawanka zan iya magana da kai, ranka yă daɗe? Ƙarfina ya ƙare kuma ina numfashi da ƙyar.”
18 Therfor eft as the siyt of a man touchide me, and coumfortide me,
Har yanzu wannan wanda yana kama da mutum ya taɓa ni ya kuma ba ni ƙarfi.
19 and seide, Man of desiris, nyle thou drede; pees be to thee, be thou coumfortid, and be thou strong. And whanne he spak with me, Y wexide strong and seide, My Lord, speke thou, for thou hast coumfortid me.
Ya kuma ce, “Kada ka ji tsoro, ya kai mutumin da ake fahariya, salama a gare ka! Ka ƙarfafa yanzu; ka yi ƙarfin hali.” Sa’ad da ya yi magana da ni, sai na samu ƙarfi na ce, “Ka yi magana ranka yă daɗe, tun da yake ka sa na sami ƙarfi.”
20 And he seide, Whether thou woost not, whi Y cam to thee? And now Y schal turne ayen, to fiyte ayens the prince of Perseis. For whanne Y yede out, the prince of Grekis apperide comynge.
Sai ya ce mini, “Ka san abin da ya kawo ni gare ka? Ba da jimawa ba zan koma in yi yaƙi da mai mulkin Farisa, kuma idan na tafi, mai mulkin Hellenawa zai taso;
21 Netheles Y schal telle to thee that, that is expressid in the scripture of treuthe; and noon is myn helpere in alle these thingis, no but Myyhel, youre prynce.
amma da farko zan faɗa maka abin da aka rubuta a cikin Littafin Gaskiya (Babu wanda ya taimake ni yaƙi da waɗannan sai dai Mika’ilu, sarkinku.

< Daniel 10 >