< Acts 24 >

1 And aftir fyue daies, Ananye, prince of preestis, cam doun with summe eldere men, and Terculle, a feir speker, which wenten to the precident ayens Poul.
Bayan kwana biyar sai Ananiyas babban firist ya tafi Kaisariya tare da waɗansu daga cikin dattawa da kuma wani lauya mai suna Tertullus, suka kawo ƙararsu game da Bulus a gaban gwamna.
2 And whanne Poul was somened, Terculle bigan to accuse hym, and seide, Whanne in myche pees we doon bi thee, and many thingis ben amendid bi thi wisdom, euere more and euery where,
Sa’ad da aka shigo da Bulus, sai Tertullus ya shiga kai ƙararsa a gaban Felis yana cewa, “Mun daɗe muna zaman lafiya a ƙarƙashinka, hangen nesanka kuma ya kawo gyare-gyare a wannan ƙasa.
3 thou best Felix, we han resseyued with al doyng of thankingis.
Ko’ina da kuma a kowace hanya, ya mafifici Felis, mun amince da wannan da godiya marar iyaka.
4 But lest Y tarie thee lengere, Y preie thee, schortly here vs for thi mekenesse.
Amma don kada in ƙara gajiyar da kai, ina roƙonka ka yi haƙuri ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu.
5 We han foundun this wickid man stirynge dissencioun to alle Jewis in al the world, and auctour of dissencioun of the secte of Nazarenus; and he also enforside to defoule the temple;
“Mun tarar da wannan mutum fitinanne ne, yana tā-da-na-zaune-tsaye a tsakanin Yahudawa ko’ina a duniya. Shi shugaban ɗarikar Nazarawa
6 whom also we token, and wolden deme, after oure lawe.
har ma ya yi ƙoƙari ya ƙazantar da haikali; shi ya sa muka kama shi.
7 But Lisias, the trybune, cam with greet strengthe aboue, and delyuerede hym fro oure hoondis;
8 and comaundide hise accuseris to come to thee, of whom thou demynge, maist knowe of alle these thingis, of whiche we accusen hym.
Ta wurin bincika shi da kanka za ka gane gaskiyar game da dukan waɗannan zargin da muke kawo a kansa.”
9 And Jewis putten to, and seiden, that these thingis hadden hem so.
Yahudawa ma suka goyi bayan zargin, suna tabbatar cewa waɗannan abubuwa haka suke.
10 And Poul answeride, whanne the president grauntide hym to seie, Of mony yeeris Y knowe thee, that thou art domesman `to this folk, and Y schal do ynowy for me with good resoun.
Da gwamna ya yi masa alama yă yi magana, sai Bulus ya amsa ya ce, “Na san cewa ka yi shekaru da yawa kana mulki a wannan ƙasa; saboda haka ina farin ciki in kāre kaina.
11 For thou maist knowe, for to me ben not more than twelue daies, sithen Y cam vp to worschipe in Jerusalem;
Da sauƙi za ka iya tabbatar cewa, bai fi kwana goma sha biyu da suka wuce ne na tafi Urushalima, domin yin sujada ba.
12 and nether in the temple thei founden me disputinge with ony man, nether makynge concours of puple, nether in synagogis, nether in citee;
Masu zargina ba su same ni ina gardama da kowa a haikali, ko kuma ina tā da hankalin jama’a a majami’u ko kuwa wani wuri dabam a cikin birni ba.
13 nether thei moun preue to thee, of the whiche thingis thei now accusen me.
Ba kuwa za su iya tabbatar maka ƙarar da suke yi yanzu a kaina ba.
14 But Y knowleche to thee this thing, that aftir the secte which thei seien eresie, so Y serue to God the fadir, `and Y bileue to alle thingis that ben writun in the lawe and profetis; and Y haue hope in God,
Amma na yarda cewa ina bauta wa Allah na kakanninmu a matsayin mai bin Hanyar da suke kira ɗarika. Na gaskata dukan abin da ya amince da Doka da yake kuma a rubuce cikin Annabawa,
15 whiche also thei hem silf abiden, the ayenrisyng `to comynge of iust men and wickid.
ina kuma da irin bege ɗaya ga Allah yadda mutanen nan suke da shi, cewa akwai tashin matattu masu adalci da masu mugunta duka.
16 In this thing Y studie with outen hirtyng, to haue concience to God, and to men euermore.
Saboda haka, ina ƙoƙari kullum in kasance da lamiri mai tsabta a gaban Allah da mutane.
17 But after many yeeris, Y cam to do almes dedis to my folc, and offryngis, and auowis;
“Bayan’yan shekaru da dama da ba na nan, sai na dawo Urushalima don in kawo wa mutanena kyautai saboda matalauta in kuma yi sadaka.
18 in whiche thei founden me purified in the temple, not with company, nether with noise. And thei cauyten me, and thei crieden, and seiden, Take awei oure enemye.
Ni tsarkake ne sa’ad da suka same ni cikin filin haikalin ina yin haka. Babu taro tare da ni, ba kuwa ina tā da hankali ba.
19 And summe Jewis of Asie, whiche it behofte to be now present at thee, and accuse, if thei hadden ony thing ayens me,
Amma akwai waɗansu Yahudawa daga lardin Asiya, waɗanda ya kamata suna a nan a gabanka su kawo ƙara in suna da wani a kaina.
20 ether these hem silf seie, if thei founden in me ony thing of wickidnesse, sithen Y stonde `in the counsel,
Ko kuwa waɗannan da suke a nan su faɗi laifin da suka same ni da shi sa’ad da na tsaya a gaban Majalisa,
21 but oneli of this vois, by which Y criede stondynge among hem, For of the ayenrisyng of deed men Y am demyd this dai of you.
sai ko wannan abu ɗaya kaɗai da na ɗaga murya na faɗi yayinda nake tsaye a gabansu cewa, ‘A game da tashin matattu ake mini shari’a a gabanku yau.’”
22 Sothely Felix delayede hem, and knewe moost certeynli of the weie, and seide, Whanne Lisias, the tribune, schal come doun, Y schal here you.
Sai Felis, wanda yake da cikakken sani game da Hanyar, ya ɗaga sauraron ƙarar. Ya ce, “In Lisiyas shugaban ƙungiyar soja ya iso, zan yanke muku shari’a.”
23 And he comaundide to a centurien to kepe hym, and that he hadde reste, nethir to forbede ony man to mynystre of his owne thingis to him.
Ya yi wa jarumin umarni yă tsare Bulus amma yă ba shi’yanci yă kuma bar abokansa su lura da bukatunsa.
24 And after summe dayes Felix cam, with Drussille his wijf, that was a Jewesse, and clepide Poul, and herde of him the feith that is in Crist Jhesu.
Bayan’yan kwanaki da dama sai Felis ya zo da matarsa Durusilla, mutuniyar Yahuda. Sai ya aika a zo da Bulus ya kuma saurare shi da yake magana game da bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
25 And while he disputide of riytwisnesse, and chastite, and of dom to comynge, Felix was maad tremblinge, and answerde, That perteneth now, go; but in tyme couenable Y schal clepe thee.
Da Bulus ya ci gaba jawabi a kan adalci, kamunkai da kuma hukunci mai zuwa, sai Felis ya tsorata ya ce, “Yanzu kam, ya isa haka! Kana iya tafi. In na sami zarafi, zan kira ka.”
26 Also he hopide, that money schulde be youun to hym of Poul; for which thing eft he clepide hym, and spak with hym.
A wani fanni yana sa rai cewa Bulus zai ba shi toshiyar baki, saboda haka ya yi ta aika a kira masa Bulus yă yi magana da shi.
27 And whanne twei yeeris weren fillid, Felix took a successoure, Porcius Festus; and Felix wolde yyue grace to Jewis, and lefte Poul boundun.
Da shekaru biyu suka wuce, sai Forsiyus Festus, ya gāji Felis, amma domin Felis ya so yă biya wa Yahudawa bukata, sai ya bar Bulus a kurkuku.

< Acts 24 >