< Romans 1 >

1 Poul, the seruaunt of Jhesu Crist, clepid an apostle, departid in to the gospel of God;
Bulus, bawan Kiristi Yesu, kirayaye don yă zama manzo, keɓaɓɓe kuma domin bisharar Allah.
2 which he hadde bihote tofore bi his profetis in holi scripturis of his sone,
Bisharar da Allah ya yi alkawari tuntuni ta bakin annabawansa a cikin Nassosi Masu Tsarki
3 which is maad to hym of the seed of Dauid bi the flesch,
game da Ɗansa. Wanda bisa ga mutuntakarsa, zuriyar Dawuda ne.
4 and he was bifor ordeyned the sone of God in vertu, bi the spirit of halewyng of the ayenrisyng of deed men, of Jhesu Crist oure Lord,
Wanda bisa ga Ruhun tsarki, an shaida shi da iko cewa shi Ɗan Allah ne ta wurin tashinsa daga matattu. Wannan bishara kuwa game da Yesu Kiristi Ubangijinmu ne.
5 bi whom we han resseyued grace and the office of apostle, to obeie to the feith in alle folkis for his name,
Ta wurinsa da kuma saboda sunansa, muka sami alheri muka kuma zama manzanni don mu kira mutane daga cikin dukan Al’ummai zuwa ga biyayyar da take zuwa daga bangaskiya.
6 among whiche ye ben also clepid of Jhesu Crist,
Ku ma kuna cikin waɗanda aka kira ku zama na Yesu Kiristi.
7 to alle that ben at Rome, derlyngis of God, and clepid hooli, grace to you, and pees of God oure fadir, and of the Lord Jhesu Crist.
Wannan wasiƙa ce zuwa ga dukanku da kuke a Roma waɗanda Allah yake ƙauna, waɗanda kuma ya kira domin su zama tsarkaka. Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma daga Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
8 First Y do thankyngis to my God, bi Jhesu Crist, for alle you, for youre feith is schewid in al the world.
Da farko, ina gode wa Allahna ta wurin Yesu Kiristi saboda ku duka, gama ana ba da labarin bangaskiyarku a ko’ina a duniya.
9 For God is a witnesse to me, to whom Y serue in my spirit, in the gospel of his sone,
Allah, wanda nake bauta wa da dukan zuciyata cikin wa’azin bisharar Ɗansa, shi ne shaidata a kan yadda kullum ina tunawa da ku
10 that with outen ceessyng Y make mynde of you euere in my preieris, and biseche, if in ony maner sum tyme Y haue a spedi weie in the wille of God to come to you.
cikin addu’o’ina a kowane lokaci; ina kuma addu’a cewa a ƙarshe in Allah ya yarda hanya za tă buɗe mini in zo wurinku.
11 For Y desire to se you, to parten sumwhat of spiritual grace,
Ina marmarin ganinku don in ba ku wata baiwar ruhaniya, don ku yi ƙarfi
12 that ye be confermyd, that is, to be coumfortid togidere in you, bi feith that is bothe youre and myn togidere.
wato, don ni da ku mu ƙarfafa juna ta wurin bangaskiyarmu.
13 And, britheren, Y nyle, that ye vnknowun, that ofte Y purposide to come to you, and Y am lett to this tyme, that Y haue sum fruyt in you, as in othere folkis.
Ina so ku sani’yan’uwa cewa na yi shirin zuwa wurinku sau da dama (amma aka hana ni yin haka sai yanzu). Na so in zo domin in sami mutane wa Kiristi a cikinku, kamar yadda na yi a cikin sauran Al’ummai.
14 To Grekis and to barberyns, to wise men and to vnwise men,
Ina da hakki ga Hellenawa da waɗanda ba Hellenawa ba, ga masu hikima da kuma marasa azanci.
15 Y am dettour, so that that is in me is redi to preche the gospel also to you that ben at Rome.
Shi ya sa na yi himma sosai in yi muku wa’azin bishara ku ma da kuke a Roma.
16 For Y schame not the gospel, for it is the vertu of God in to heelthe to ech man that bileueth, to the Jew first, and to the Greke.
Ba na jin kunyar bishara, gama ita ikon Allah ne domin ceton kowa da ya gaskata, da farko ga Yahudawa, sa’an nan ga Al’ummai.
17 For the riytwisnesse of God is schewid in it, of feith in to feith,
Gama a cikin bishara an bayyana adalci daga Allah wanda yake ta wurin bangaskiya daga farko zuwa ƙarshe, kamar yadda yake a rubuce cewa, “Mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiya.”
18 as it is writun, For a iust man lyueth of feith. For the wraththe of God is schewid fro heuene on al vnpite and wickidnesse of tho men, that withholden the treuthe of God in vnriytwisnes.
Ana bayyana fushin Allah daga sama a kan dukan rashin sanin Allah da kuma muguntar mutanen da suke danne gaskiya ta wurin muguntarsu,
19 For that thing of God that is knowun, is schewid to hem, for God hath schewid to hem.
gama abin da ana iya sani game da Allah a bayyane yake a gare su, domin Allah ya bayyana musu shi.
20 For the vnuysible thingis of hym, that ben vndurstondun, ben biholdun of the creature of the world, bi tho thingis that ben maad, yhe, and the euerlastynge vertu of hym and the godhed, so that thei mowe not be excusid. (aïdios g126)
Gama tun halittar duniya halayen Allah marar ganuwa, madawwamin ikonsa da kuma allahntakarsa, ana iya ganinsu sarai, ana fahimtarsu ta wurin abubuwan da Allah ya halitta, domin kada mutane su sami wata hujja. (aïdios g126)
21 For whanne thei hadden knowe God, thei glorifieden hym not as God, nether diden thankyngis; but thei vanyschiden in her thouyts, and the vnwise herte of hem was derkid.
Gama ko da yake sun san Allah, ba su ɗaukaka shi a matsayin Allah ko su gode masa ba, sai dai tunaninsu ya zama banza, zukatansu masu wauta kuma suka duhunta.
22 For thei `seiynge that hem silf weren wise, thei weren maad foolis.
Ko da yake sun ɗauka su masu hikima ne, sai suka zama wawaye,
23 And thei chaungiden the glorie of `God vncorruptible in to the licnesse of an ymage of a deedli man, and of briddis, and of foure footid beestis, and of serpentis.
suka kuma yi musayar ɗaukakar Allah marar mutuwa da siffofin da aka ƙera su yi kama da mutum mai mutuwa da tsuntsaye da dabbobi da kuma halittu masu ja da ciki.
24 For which thing God bitook hem in to the desiris of her herte, in to vnclennesse, that thei punysche with wrongis her bodies in hem silf.
Saboda haka Allah ya yashe su ga mugayen sha’awace-sha’awacen zukatansu ga fasikanci don a ƙasƙantar da jikunansu ga yin abin kunya.
25 The whiche chaungiden the treuthe of God in to leesyng, and herieden and serueden a creature rathere than to the creatoure, that is blessid in to worldis of worldis. (aiōn g165)
Sun sauya gaskiyar Allah da ƙarya, suka kuma yi wa abubuwan da aka halitta sujada suna bauta musu a maimakon Mahalicci, wanda ake yabo har abada. Amin. (aiōn g165)
26 Amen. Therfor God bitook hem in to passiouns of schenschipe. For the wymmen of hem chaungiden the kyndli vss in to that vss that is ayens kynde.
Saboda wannan, Allah ya yashe su ga sha’awace-sha’awacensu masu banƙyama. Har matansu suka sauya daga haɗuwar mace da miji wadda ita ce daidai bisa ga halitta zuwa haɗuwa da’yan’uwansu mata wadda ba daidai ba.
27 Also the men forsoken the kyndli vss of womman, and brenneden in her desiris togidere, and men in to men wrouyten filthehed, and resseyueden in to hem silf the meede that bihofte of her errour.
Haka ma maza suka bar al’adar kwana da mata suka tunzura cikin sha’awar kwana da juna, abin da ba daidai ba bisa ga halitta. Maza suka aikata rashin kunya da waɗansu maza, suka jawo wa kansu sakamako daidai da bauɗewarsu.
28 And as thei preueden that thei hadden not God in knowyng, God bitook hem in to a repreuable wit, that thei do tho thingis that ben not couenable; that thei ben fulfillid with al wickidnesse,
Da yake ba su yi tunani cewa ya dace su riƙe sanin Allah da suke da shi ba, sai ya yashe su ga tunanin banza da wofi, su aikata abin da bai kamata a yi ba.
29 malice, fornycacioun, coueitise, weiwardnesse, ful of enuye, mansleyngis, strijf, gile, yuel wille, preuy bacbiteris, detractouris,
Sun cika da kowace irin ƙeta, mugunta, kwaɗayi, da tunanin banza da wofi. Suka kuma cika da kishi, kisankai, faɗa, ruɗu, da kuma riƙo a zuci. Su masu gulma ne,
30 hateful to God, debateris, proude, and hiy ouer mesure, fynderis of yuele thingis, not obeschynge to fadir and modir,
da masu ɓata suna, masu ƙin Allah, masu rashin kunya, masu girman kai, masu rigima; sukan ƙaga hanyoyin yin mugunta; suna rashin biyayya ga iyayensu;
31 vnwise, vnmanerli, withouten loue, withouten boond of pees, with outen merci.
su marasa hankali ne, marasa bangaskiya, marasa ƙauna, marasa tausayi.
32 The whiche whanne thei hadden knowe the riytwisnesse of God, vndirstoden not, that thei that don siche thingis ben worthi the deth, not oneli thei that don tho thingis, but also thei that consenten to the doeris.
Ko da yake sun san dokar adalcin Allah cewa masu aikata irin waɗannan abubuwa sun cancanci mutuwa, duk da haka ba cin gaba da aikata waɗannan abubuwa kaɗai suke yi ba, har ma suna goyon bayan masu yinsu.

< Romans 1 >