< Revelation 20 >

1 Then I saw an angel coming down from Heaven, having the key of the bottomless pit, and upon his arm he carried a great chain. (Abyssos g12)
Sai na ga mala'ika na saukowa daga sama. Yana da makullin rami marar iyaka, yana kuma da babar sarka a hannunsa. (Abyssos g12)
2 He laid hold of the Dragon--the ancient serpent--who is the Devil and the Adversary, and bound him for a thousand years, and hurled him into the bottomless pit.
Sai ya dauki tsohon macijin, wanda shine iblis, ko shaidan, ya daure shi shekaru dubu.
3 He closed the entrance and put a seal upon him in order that he might be unable to lead the nations astray any more until the thousand years were at an end. Afterwards he is to be set at liberty for a short time. (Abyssos g12)
Ya jefa shi cikin rami marar iyaka, ya rufe shi ya kuma sa hatimi a bisansa. Hakan ya faru ne domin kada ya kara yaudarar al'ummai har sai bayan shekaru dubu. Bayan wannan, dole a sake shi na dan lokaci. (Abyssos g12)
4 And I saw thrones, and some who were seated on them, to whom judgment was entrusted. And I saw the souls of those who had been beheaded on account of the testimony that they had borne to Jesus and on account of God's Message, and also the souls of those who had not worshipped the Wild Beast or his statue, nor received his mark on their foreheads or on their hands; and they came to Life and were kings with Christ for a thousand years.
Sa'annan na ga kursiyoyi. Wadanda ke zaune a bisansu sune wadanda aka ba ikon hukunci. Na kuma ga rayukan wadanda aka fille wa kai saboda shaidar Yesu da maganar Allah. Ba su yi wa dabban sujada ba ko siffarsa, suka ki su karbi alamar a goshinsu ko a hannu. Sun sake rayuwa, suka yi mulki tare da Kristi shekaru dubu.
5 No one else who was dead rose to Life until the thousand years were at an end. This is the First Resurrection.
Sauran matattun basu sake dawowa da rai ba har sai da shekaru dubu din suka cika. Wannan shine tashin matattu na fari.
6 Blessed and holy are those who share in the First Resurrection. The Second Death has no power over them, but they shall be priests to God and to Christ, and shall be kings with Christ for the thousand years.
Mai albarka ne mai tsarki ne kuma wanda yake da rabo cikin tashin matattu na fari! Mutuwa ta biyu ba ta da iko akan wadannan. Za su zama firistocin Allah da na Almasihu za su kuma yi mulki tare da shi shekaru dubu.
7 But when the thousand years are at an end, the Adversary will be released from his imprisonment,
Sa'adda shekaru dubu suka zo ga karshe, za a saki shaidan daga kurkukunsa.
8 and will go out to lead astray the nations in all the four corners of the earth, Gog and Magog, and assemble them for war, and they are like the sands on the seashore in number.
Za ya fito domin ya yaudari al'ummai da ke kursuyoyi hudu na duniya, Gog da Magog ya tattara su domin yaki. Yawan su zai zama kamar yashin teku.
9 And they went up over the whole breadth of the earth and surrounded the encampment of God's people and the beloved city. But fire came down from Heaven and consumed them;
Suka bazu a fuskar duniya suka kuma kewaye sansanin masu ba da gaskiya, kaunataccen birni. Amma wuta ta sauko daga sama ta lankwame su.
10 and the Devil, who had been leading them astray, was thrown into the Lake of fire and sulphur where the Wild Beast and the false Prophet were, and day and night they will suffer torture until the Ages of the Ages. (aiōn g165, Limnē Pyr g3041 g4442)
Shaidan, wanda ya yaudare su, aka jefa shi cikin korama ta farin wuta mai ci, inda aka jefa dabban da makaryacin annabin. Za su sha azaba dare da rana har abada abadin. (aiōn g165, Limnē Pyr g3041 g4442)
11 Then I saw a great white throne and One who was seated on it, from whose presence earth and sky fled away, and no place was found for them.
Sai na ga babban kursiyi da wanda ke zaune a kansa. Duniya da sama suka guje wa fuskarsa, amma babu wurin da za su tafi.
12 And I saw the dead, the great and the small, standing in front of the throne. And books were opened; and so was another book--namely, the Book of Life; and the dead were judged by the things recorded in the books in accordance with what their conduct had been.
Na ga matattu manya da kanana- suna tsaye gaban kursiyin, aka bude litattafai. Sai aka bude wani littafi - Littafin rai. Aka yi wa matattu shari'a bisa ga abinda aka rubuta cikin litattafan, gwargwadon ayyukansu.
13 Then the sea yielded up the dead who were in it, Death and Hades yielded up the dead who were in them, and each man was judged in accordance with what his conduct had been. (Hadēs g86)
Teku ta ba da matattun dake cikinta. Mutuwa da hades suka ba da matattun da ke cikinsu, aka yi masu shari'a gwargwadon abin da suka yi. (Hadēs g86)
14 Then Death and Hades were thrown into the Lake of fire; this is the Second Death--the Lake of fire. (Hadēs g86, Limnē Pyr g3041 g4442)
Aka jefa mutuwa da hades cikin tafkin wuta. Wannan shine mutuwa ta biyu - tafkin wuta. (Hadēs g86, Limnē Pyr g3041 g4442)
15 And if any one's name was not found recorded in the Book of Life he was thrown into the Lake of fire. (Limnē Pyr g3041 g4442)
Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce cikin littafin rai ba, aka jefar da shi cikin tafkin wuta. (Limnē Pyr g3041 g4442)

< Revelation 20 >