< Jude 1 >
1 Jude, a bondservant of Jesus Christ and a brother of James: To those who are in God the Father, enfolded in His love, and kept for Jesus Christ, and called.
Yahuza, bawan Yesu Almasihu kuma dan'uwan Yakubu, zuwa ga kirayayyu, kaunatattu a cikin Allah Uba, kebabbu domin Yesu Kristi:
2 May mercy, peace and love be abundantly granted to you.
bari jinkai da salama da kauna su ribabanya a gare ku.
3 Dear friends, since I am eager to begin a letter to you on the subject of our common salvation, I find myself constrained to write and cheer you on to the vigorous defense of the faith delivered once for all to God's people.
Kaunatattu, ina iyakar kokari in rubuta maku game da ceton mu duka, ya zama dole in gargade ku sosai game da bangaskiya wadda aka mika wa masu bi sau daya tak ba kari.
4 For certain persons have crept in unnoticed--men spoken of in ancient writings as pre-destined to this condemnation--ungodly men, who pervert the grace of our God into an excuse for immorality, and disown Jesus Christ, our only Sovereign and Lord.
Don wasu mutane sun sadado sun shigo da sanda a asirce wadanda an rubuta game da hukuncin su tun da dadewa-mutane marasa imani, wanda suka canza alherin Allah zuwa lalata, kuma sun karyata makadaicin Shugaba da Ubangijinmu, Yesu Almasihu.
5 I desire to remind you--although the whole matter is already familiar to you--that the Lord saved a people out of the land of Egypt, but afterwards destroyed those who had no faith.
Ina so in tunashe ku-ko da shike kun rigaya kun san abin, da cewa Allah ya ceci wasu mutane daga kasar masar, amma daga baya ya hallaka wadanda basu ba da gaskiya ba.
6 And angels--those who did not keep the position originally assigned to them, but deserted their own proper abode--He reserves in everlasting bonds, in darkness, in preparation for the judgement of the great day. (aïdios )
Kuma mala'iku wadanda ba su rike matsayin ikon su ba, amma suka bar wurin zaman su na ainihi-Allah ya tsare su a sarka na har'abada a cikin bakin duhu domin babban ranar shari'a. (aïdios )
7 So also Sodom and Gomorrah--and the neighboring towns in the same manner--having been guilty of gross fornication and having gone astray in pursuit of unnatural vice, are now before us as a specimen of the fire of the Ages in the punishment which they are undergoing. (aiōnios )
Suna nan kamar Saduma da Gwamrata da kuma biranen da ke kewaye da su, wadanda suka ba da kansu ga fasikanci suna bin sha'awoyi wanda ba na dabi'a ba. Aka mai da su abin misalin wadanda suka sha wuta mara matuka. (aiōnios )
8 Yet in just the same way these dreamers also pollute the body, while they set authority at naught and speak evil of dignities.
Haka kuma, wadannan masu mafarkan suna lalatar da jikinsu. Suna raina masu mulki, kuma suna fadar miyagun abubuwa a kan masu daukaka.
9 But Michael the Archangel, when contending with the Devil and arguing with him about the body of Moses, did not dare to pronounce judgement on him in abusive terms, but simply said, "The Lord rebuke you."
Amma ko Mika'ilu babban mala'ika, a lokacin da yake jayyaya da muhawara da shaidan a kan gawar Musa, bai kuskura ya fadi wata kalmar hukunci a kansa ba. Maimakon haka ya ce, “Bari Ubangiji ya tsauta maka!''
10 Yet these men are abusive in matters of which they know nothing, and in things which, like the brutes, they understand instinctively--in all these they corrupt themselves.
Amma waddannan mutane suna kawo batanci game da dukan abin da ba su gane ba. Wadannan mutane masu halin dabbobi ne, suna kwa jawo wa kansu hallaka kenan.
11 Alas for them; for they have followed in the steps of Cain; for the sake of gain they have rushed on headlong in the evil ways of Balaam; and have perished in rebellion like that of Korah!
Kaiton su! Domin sun bi hanyar Kayinu, kuma sun tsunduma cikin kuskuren Bal'amu domin samun riba. Suka hallaka cikin husuma irin ta Kora.
12 These men--sunken rocks! --are those who share the pleasure of your love-feasts, unrestrained by fear while caring only for themselves; clouds without water, driven away by the winds; trees that cast their fruit, barren, doubly dead, uprooted;
Wadannan hatsari ne a boye cikin bukukuwan ku na kauna. Suna shagali ba kunya ba tsoro, suna ciyar da kansu kadai. Su holokon hadari ne marar ruwa, wanda iska ke korar sa. Su itatuwa ne shirim ba yaya, mattatu ribi biyu, tumbukakku tun daga saiwa.
13 wild waves of the sea, foaming out their own shame; wandering stars, for whom is reserved dense darkness of age-long duration. (aiōn )
Su rakuman teku ne masu hauka, suna fahariya cikin kumfar kunyar su. Su kamar taurari ne masu tartsatsi. Wadanda aka tanada wa duhu baki kirin na har abada. (aiōn )
14 It was also about these that Enoch, who belonged to the seventh generation from Adam, prophesied, saying, "The Lord has come, attended by myriads of His people, to execute judgement upon all,
Ahnuhu, mutum na bakwai daga Adamu, ya yi anabci game da su cewa, “Duba, Ubangiji zai zo da tsarkakan sa dubun dubbai.
15 and to convict all the ungodly of all the ungodly deeds which in their ungodliness they have committed, and of all the hard words which they, ungodly sinners as they are, have spoken against Him."
Domin ya zartar da hukunci a kan dukan kowa, ya kuma cakune dukan marasa da'a a cikin dukan ayyukan su na rashin da'a wanda suka aikata a hanyar da bata cancanta ba, da kuma kalmomi masu kaifi da masu zunubi suka fada game da shi.”
16 These men are murmurers, ever bemoaning their lot. Their lives are guided by their evil passions, and their mouths are full of big, boastful words, while they treat individual men with admiring reverence for the sake of the advantage they can gain.
Wadannan masu cecekuce ne, masu gunaguni, wadanda ke bin sha'awar su ta mugunta, masu tinkaho da fahariya, masu bambadanci domin ribar kansu.
17 But as for you, my dearly-loved friends, remember the words that before now were spoken by the Apostles of our Lord Jesus Christ--
Amma ku, kaunatattu, ku tuna da kalmomin da manzannin Yesu Almasihunmu suka gaya maku tun da.
18 how they declared to you, "In the last times there shall be scoffers, obeying only their own ungodly passions."
Sun ce maku, “A cikin kwanaki na karshe, za a samu masu ba'a, wadanda ke bin sha'awoyin su na rashin ibada,”
19 These are those who cause divisions. They are men of the world, wholly unspiritual.
Wadannan mutane masu haddasa tsatsaguwa ne, kuma su yan duniya ne, ba su kuma da Ruhu.
20 But you, my dearly-loved friends, building yourselves up on the basis of your most holy faith and praying in the Holy Spirit,
Amma ku, kaunatattu, ku gina kanku a cikin mafificiyar bangaskiyar ku mai daraja, kuma kuna addu'a a cikin Ruhu Mai Tsarki.
21 must keep yourselves safe in the love of God, waiting for the mercy of our Lord Jesus Christ which will result in the Life of the Ages. (aiōnios )
Ku rike kanku a cikin kaunar Allah, kuna kuma jiran jinkan Ubangijinmu Yesu Almasihu wanda ke kawo rai na har abada. (aiōnios )
22 Some, when they argue with you, you must endeavor to convince;
Ku nuna jinkai ga masu shakku. Ceci wadansu ta wurin fizge su daga wuta.
23 others you must try to save, as brands plucked from the flames; and on others look with pity mingled with fear, while you hate every trace of their sin.
Ga wadansu kuma ku nuna jinkai da rawar jiki, kuyi kyamar koda tufafin jikinsu ma.
24 But to Him who is able to keep you safe from stumbling, and cause you to stand in the presence of His glory free from blemish and full of exultant joy--
Yanzu, zuwa ga wanda yake da iko ya hana ku tuntube, ya kuma sa ku tsaya a gaban madaukakiyar kasancewarsa, marasa abin zargi da kuma murna mai yawa,
25 to the only God our Saviour--through Jesus Christ our Lord, be ascribed glory, majesty, might, and authority, as it was before all time, is now, and shall be to all the Ages! Amen. (aiōn )
zuwa ga Allah makadaici mai ceton mu ta wurin Yesu Almasihu Ubangijinmu, daukaka, da girma, da mulki, da iko su kasance, kamin dukan lokuta, yanzu, da har abada. Amin. (aiōn )