< Acts 22 >

1 "Brethren and fathers," he said, "listen to my defence which I now make before you."
“’Yan’uwa da iyaye, ku saurari kāriyata yanzu.”
2 And on hearing him address them in Hebrew, they kept all the more quiet; and he said,
Da suka ji ya yi musu magana da Arameyik, sai suka yi tsit. Sai Bulus ya ce,
3 "I am a Jew, born at Tarsus in Cilicia, but brought up in this city. I was carefully trained at the feet of Gamaliel in the Law of our forefathers, and, like all of you to-day, was zealous for God.
“Ni mutumin Yahuda ne haifaffen Tarshish na Silisiya, amma a nan birnin ne aka rene ni. Aka horar da ni sosai cikin dokokin kakanninmu a ƙarƙashin Gamaliyel ni ma dā mai himma ne cikin bauta wa Allah kamar yadda kowannenku yake a yau.
4 I persecuted to death this new faith, continually binding both men and women and throwing them into prison;
Na tsananta wa masu bin wannan Hanyar har ga mutuwarsu, ina kama maza da mata ina kuma jefa su cikin kurkuku,
5 as the High Priest also and all the Elders can bear me witness. It was, too, from them that I received letters to the brethren in Damascus, and I was already on my way to Damascus, intending to bring those also who had fled there, in chains to Jerusalem, to be punished.
kamar yadda babban firist da dukan Majalisa za su iya shaida. Na ma karɓi wasiƙu daga gare su zuwa ga’yan’uwansu a Damaskus, na kuma tafi can don in kawo waɗannan mutane a daure zuwa Urushalima don a hukunta su.
6 "But on my way, when I was now not far from Damascus, about noon a sudden blaze of light from Heaven shone round me.
“Wajen tsakar rana da na yi kusa da Damaskus, ba zato ba tsammani sai wani babban haske daga sama ya haskaka kewaye da ni.
7 I fell to the ground and heard a voice say to me, "'Saul, Saul, why are you persecuting Me?'
Sai na fāɗi a ƙasa na kuma ji wata murya ta ce mini, ‘Shawulu! Shawulu! Don me kake tsananta mini?’
8 "'Who art thou, Lord?' I asked. "'I am Jesus, the Nazarene,' He replied, 'whom you are persecuting.'
“Sai na yi tambaya na ce, ‘Wane ne kai, ya Ubangiji?’ “Ya amsa ya ce, ‘Ni ne Yesu Banazare, wanda kake tsanantawa.’
9 "Now the men who were with me, though they saw the light, did not hear the words of Him who spoke to me.
Abokan tafiyata suka ga hasken, amma ba su fahimci muryar mai magana da ni ba.
10 And I asked, "'What am I to do, Lord?' "And the Lord said to me, "'Rise, and go into Damascus. There you shall be told of all that has been appointed for you to do.'
“Sai na yi tambaya, na ce, ‘Me zan yi, ya Ubangiji?’ “Ubangiji ya ce, ‘Tashi, ka tafi cikin Damaskus. A can za a faɗa maka duk abin da aka shirya za ka yi.’
11 "And as I could not see because the light had been so dazzling, those who were with me had to lead me by the arm, and so I came to Damascus.
Abokan tafiyata suka ja ni a hannu zuwa cikin Damaskus, saboda ƙarfin hasken ya makanta ni.
12 "And a certain Ananias, a pious man who obeyed the Law and bore a good character with all the Jews of the city,
“Wani mutumin da ake kira Ananiyas ya zo ya gan ni. Shi mai ibada ne wajen kiyaye dokoki wanda dukan Yahudawan da suke zama a can suna girmama shi ƙwarai.
13 came to me and standing at my side said, "'Brother Saul, recover your sight.' "I instantly regained my sight and looked up at him.
Ya tsaya kusa da ni ya ce, ‘Ɗan’uwa Shawulu, ka sami ganin garinka!’ A daidai lokacin kuwa na iya ganinsa.
14 Then he said, 'The God of our forefathers has appointed you to know His will, and to see the righteous One and hear Him speak.
“Sa’an nan ya ce, ‘Allah na kakanninmu ya zaɓe ka ka san nufinsa ka kuma ga Mai Adalcin nan ka kuma ji kalmomi daga bakinsa.
15 For you shall be a witness for Him, to all men, of what you have seen and heard.
Za ka zama mai shaidarsa ga dukan mutane game da abin da ka gani ka kuma ji.
16 And now why delay? Rise, get yourself baptized, and wash off your sins, calling upon His name.'
Yanzu me kake jira? Ka tashi, a yi maka baftisma, a wanke zunubanka, ta wurin kira bisa ga sunansa.’
17 "After my return to Jerusalem, and while praying in the Temple, I fell into a trance.
“Sa’ad da na dawo Urushalima ina cikin addu’a a haikali, sai na ga wahayi
18 I saw Jesus, and He said to me, "'Make haste and leave Jerusalem quickly, because they will not accept your testimony about Me.'
na ga Ubangiji yana magana. Ya ce mini, ‘Maza! Ka bar Urushalima, gama ba za su yarda da shaidarka game da ni ba.’
19 "'Lord,' I replied, 'they themselves well know how active I was in imprisoning, and in flogging in synagogue after synagogue those who believe in Thee;
“Na amsa na ce, ‘Ubangiji, waɗannan mutane sun san cewa na bi majami’a-majami’a na jefa waɗanda suka gaskata da kai a cikin kurkuku, in kuma yin musu dūka.
20 and when they were shedding the blood of Stephen, Thy witness, I was standing by, fully approving of it, and I held the clothes of those who were killing him.'
Sa’ad da kuma aka zub da jinin Istifanus mashaidinka, na tsaya can ina ba da goyon bayana ina kuma tsaron tufafin masu kisansa.’
21 "'Go,' He replied; 'I will send you as an Apostle to nations far away.'"
“Sa’an nan Ubangiji ya ce mini, ‘Je ka; zan aike ka can nesa a wurin Al’ummai.’”
22 Until they heard this last statement the people listened to Paul, but now with a roar of disapproval they cried out, "Away with such a fellow from the earth! He ought not to be allowed to live."
Taron suka saurari Bulus sai da ya yi wannan magana. Sa’an nan suka ɗaga muryoyinsu suka yi ihu suka ce, “A raba duniya da wannan mutum! Bai cancanci yă rayu ba!”
23 And when they continued their furious shouts, throwing their clothes into the air and flinging dust about,
Da suna ihu suna kaɗa mayafansu suna da tā da ƙura sama,
24 the Tribune ordered him to be brought into the barracks, and be examined by flogging, in order to ascertain the reason why they thus cried out against him.
sai shugaban ƙungiyar sojan ya umarta a kai Bulus a barikin soja. Ya ba da umarni a yi masa bulala a kuma tambaye shi abin da ya sa mutane suke masa ihu haka.
25 But, when they had tied him up with the straps, Paul said to the Captain who stood by, "Does the Law permit you to flog a Roman citizen--and one too who is uncondemned?"
Suna kwantar da shi ke nan domin a yi masa bulala, sai Bulus ya ce wa jarumin da yake tsaye a nan, “Ashe, daidai ne bisa ga doka a yi wa ɗan ƙasar Roma bulala wanda ba a ma tabbatar da laifi a kansa ba?”
26 On hearing this question, the Captain went to report the matter to the Tribune. "What are you intending to do?" he said. "This man is a Roman citizen."
Da jarumin ya ji haka sai ya je wurin shugaban ƙungiyar sojan ya ce masa, “Me kake so yi ne? Wannan mutum ɗan ƙasar Roma ne.”
27 So the Tribune came to Paul and asked him, "Tell me, are you a Roman citizen?" "Yes," he said.
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya je ya tambayi Bulus ya ce, “Faɗa mini, kai ɗan ƙasar Roma ne?” Bulus ya ce, “I.”
28 "I paid a large sum for my citizenship," said the Tribune. "But I was born free," said Paul.
Sai shugaban ƙungiyar sojan ya ce, “Sai da na biya kuɗi mai yawa kafin in zama ɗan ƙasa.” Bulus ya ce, “Ni kuwa an haife ni ɗan ƙasa.”
29 So the men who had been on the point of putting him under torture immediately left him. And the Tribune, too, was frightened when he learnt that Paul was a Roman citizen, for he had had him bound.
Waɗanda dā suke shirin yin masa tambayoyi suka ja da baya nan da nan. Shugaban ƙungiyar sojan kansa ya tsorata da ya fahimci cewa ya sa wa Bulus, ɗan ƙasar Roma sarƙa.
30 The next day, wishing to know exactly what charge was being brought against him by the Jews, the Tribune ordered his chains to be removed; and, having sent word to the High Priests and all the Sanhedrin to assemble, he brought Paul down and made him stand before them.
Kashegari da yake shugaban ƙungiyar sojan ya so yă tabbatar da ainihin abin da ya sa Yahudawa suke zargin Bulus, sai ya sake shi ya kuwa umarci manyan firistoci da dukan Majalisar su taru. Sa’an nan ya kawo Bulus ya sa ya tsaya a gabansu.

< Acts 22 >