< Acts 16 >
1 He also came to Derbe and to Lystra. At Lystra he found a disciple, Timothy by name--the son of a Christian Jewess, though he had a Greek father.
Bulus ya kai Derbe sa’an nan kuma zuwa Listira, inda wani almajiri mai suna Timoti yake da zama, wanda mahaifiyarsa mutuniyar Yahuda ce kuma mai bi ce, amma mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.
2 Timothy was well spoken of by the brethren at Lystra and Iconium,
’Yan’uwa a Listira da Ikoniyum sun yi magana mai kyau ƙwarai a kansa.
3 and Paul desiring that he should accompany him on his journey, took him and circumcised him on account of the Jews in those parts, for they all knew that his father was a Greek.
Bulus ya so ya ɗauke shi a tafiyar, saboda haka ya yi masa kaciya, domin Yahudawan da suke da zama a wurin, don duk sun san cewa mahaifinsa mutumin Hellenawa ne.
4 As they journeyed on from town to town, they handed to the brethren for their observance the decisions which had been arrived at by the Apostles and Elders in Jerusalem.
Yayinda suke tafiya daga gari zuwa gari, suka dinga ba da shawarwarin da manzanni da dattawa a Urushalima suka zartar domin mutane su kiyaye.
5 So the Churches went on gaining a stronger faith and growing in numbers from day to day.
Saboda haka ikkilisiyoyi suka ginu cikin bangaskiya suka kuma yi girma suka yi ta ƙaruwa kowace rana.
6 Then Paul and his companions passed through Phrygia and Galatia, having been forbidden by the Holy Spirit to proclaim the Message in the province of Asia.
Bulus da abokan tafiyarsa suka zazzaga dukan yankin Firjiya da Galatiya, don Ruhu Mai Tsarki ya hana su yin wa’azi a lardin Asiya.
7 When they reached the frontier of Mysia, they were about to enter Bithynia, but the Spirit of Jesus would not permit this.
Da suka isa kan iyakar Misiya, suka yi ƙoƙari su shiga Bitiniya, amma Ruhun Yesu bai yarda musu ba.
8 So, passing along Mysia, they came to Troas.
Saboda haka suka ratsa Misiya suka zo Toruwas.
9 Here, one night, Paul saw a vision. There was a Macedonian who was standing, entreating him and saying, "Come over into Macedonia and help us."
Da dare Bulus ya ga wahayin wani mutumin Makidoniya yana tsaye yana roƙonsa cewa, “Ka zo Makidoniya ka taimake mu.”
10 So when he had seen the vision, we immediately looked out for an opportunity of passing on into Macedonia, confidently inferring that God had called us to proclaim the Good News to the people there.
Bayan Bulus ya ga wahayin, muka shirya nan take mu tashi zuwa Makidoniya, mun tabbata cewa, Allah ya kira mu mu yi musu wa’azin bishara.
11 Accordingly we put out to sea from Troas, and ran a straight course to Samothrace. The next day we came to Neapolis,
Daga Toruwas muka tashi zuwa teku muka kuma shiga jirgin ruwa muka miƙe kai tsaye zuwa Samotiras, kashegari kuma muka nufi Neyafolis.
12 and thence to Philippi, which is a city in Macedonia, the first in its district, a Roman colony. And there we stayed some little time.
Daga can muka tafi Filibbi, wata babbar alkaryar Roma wadda kuma take babban birni a gundumar Makidoniya. Muka zauna a can kwanaki masu yawa.
13 On the Sabbath we went beyond the city gate to the riverside, where we had reason to believe that there was a place for prayer; and sitting down we talked with the women who had come together.
A Asabbaci, muka fita ƙofar birnin zuwa bakin kogi, inda muke tsammani za mu sami wurin yin addu’a. Muka zauna muka fara yin wa matan da suka taru a can magana.
14 Among our hearers was one named Lydia, a dealer in purple goods. She belonged to the city of Thyateira, and was a worshipper of the true God. The Lord opened her heart, so that she gave attention to what Paul was saying.
Ɗaya daga cikin waɗanda suka saurare mu mace ce mai suna Lidiya, mai sayar da yadunan jan garura masu tsada daga birnin Tiyatira, mai yi wa Allah sujada. Ubangiji ya buɗe zuciyarta har ta karɓi saƙon Bulus.
15 When she and her household had been baptized, she urged us, saying, "If in your judgement I am a believer in the Lord, come and stay at my house." And she made us go there.
Da aka yi mata baftisma tare da iyalin gidanta, sai ta gayyace mu zuwa gidanta. Ta ce, “In kun amince ni mai bi ce cikin Ubangiji, sai ku zo ku sauka a gidana.” Sai ta kuwa rinjaye mu.
16 One day, as we were on our way to the place of prayer, a slave girl met us who claimed to be inspired and was accustomed to bring her owners large profits by telling fortunes.
Wata rana muna tafiya zuwa wurin yin addu’a, sai muka sadu da wata baranya mai ruhun aljani mai duba. Takan samo wa mutanenta kuɗi da yawa, duban da take yi.
17 She kept following close behind Paul and the rest of us, crying aloud, "These men are the bondservants of the Most High God, and are proclaiming to you the way of salvation."
Wannan yarinya kuwa ta bi Bulus da kuma sauranmu, tana ihu tana cewa, “Waɗannan mutane bayin Allah Mafi Ɗaukaka ne, suna sanar da ku hanyar ceto.”
18 This she persisted in for a considerable time, until Paul, wearied out, turned round and said to the spirit, "I command you in the name of Jesus Christ to come out of her." And it came out immediately.
Ta yi ta faɗin haka har kwanaki masu yawa. A ƙarshe Bulus ya damu ƙwarai sai ya juya ya ce wa aljanin, “A cikin sunan Yesu Kiristi na umarce ka, ka rabu da ita!” Nan take aljanin ya rabu da ita.
19 But when her owners saw that their hopes of gain were gone, they seized Paul and Silas and dragged them off to the magistrates in the public square.
Da iyayengijin baranyar suka ga hanyar samun kuɗinsu ta toshe, sai suka kama Bulus da Sila suka ja su zuwa cikin kasuwa don su fuskanci hukuma.
20 Then they brought them before the praetors. "These men," they said, "are creating a great disturbance in our city.
Sai suka kawo su a gaban alƙalai suka ce, “Waɗannan Yahudawa ne, suna kuma birkitar mana da gari,
21 They are Jews, and are teaching customs which we, as Romans, are not permitted to adopt or practise."
ta wurin koyar da al’adun da ba daidai ba ne mu Romawa mu karɓa ko mu aikata.”
22 The crowd, too, joined in the outcry against them, till at length the praetors ordered them to be stripped and beaten with rods;
Sai taron suka fāɗa wa Bulus da Sila gaba ɗaya, alƙalan kuwa suka yi umarni a tuɓe su a kuma yi musu dūka.
23 and, after severely flogging them, they threw them into jail and bade the jailer keep them safely.
Bayan an yi musu bulala sosai, sai aka jefa su cikin kurkuku, aka umarci mai gadin kurkukun yă tsare su da kyau.
24 He, having received an order like that, lodged them in the inner prison, and secured their feet in the stocks.
Da karɓan irin umarnan nan, sai ya sa su can cikin ɗakin kurkuku na ciki-ciki, kuma ya ɗaura ƙafafunsu a turu.
25 About midnight Paul and Silas were praying and singing hymns to God, and the prisoners were listening to them,
Wajen tsakar dare Bulus da Sila suna addu’a suna rera waƙoƙi ga Allah, sauran’yan kurkuku kuwa suna sauraronsu.
26 when suddenly there was such a violent shock of earthquake that the prison shook to its foundations. Instantly the doors all flew open, and the chains fell off from every prisoner.
Ba zato ba tsammani sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa har tushen ginin kurkukun ya jijjiga. Nan da nan sai duk ƙofofin kurkukun suka bubbuɗe, sarƙoƙin kowa kuma suka ɓaɓɓalle.
27 Starting up from sleep and seeing the doors of the jail wide open, the jailer drew his sword and was on the point of killing himself, supposing that the prisoners had escaped.
Mai gadin kurkukun ya farka daga barci, sa’ad da ya ga ƙofofin kurkukun a buɗe, sai ya zāre takobinsa yana shirin kashe kansa domin ya ɗauka’yan kurkukun sun gudu.
28 But Paul shouted loudly to him, saying, "Do yourself no injury: we are all here.
Amma Bulus ya yi ihu ya ce, “Kada ka yi wa kanka lahani! Dukanmu muna nan!”
29 Then, calling for lights, he sprang in and fell trembling at the feet of Paul and Silas;
Mai gadin kurkukun ya kira a kawo fitilu, ya ruga ciki ya fāɗi yana rawan jiki a gaban Bulus da Sila.
30 and, bringing them out of the prison, he exclaimed, "O sirs, what must I do to be saved?"
Sai ya fito da su waje ya kuma tambaye su ya ce, “Ranku yă daɗe, me zan yi domin in sami ceto?”
31 "Believe on the Lord Jesus," they replied, "and both you and your household will be saved."
Suka amsa suka ce, “Ka gaskata da Ubangiji Yesu, za ka sami ceto, kai da iyalinka.”
32 And they told the Lord's Message to him as well as to all who were in his house.
Sa’an nan suka yi masa maganar Ubangiji shi da kuma dukan sauran da suke a gidansa.
33 Then he took them, even at that time of night, washed their wounds, and he and all his household were immediately baptized;
A wannan sa’a na daren, mai gadin kurkukun ya ɗauke su ya wanke musu raunukansu; nan take aka yi masa baftisma da dukan iyalinsa.
34 and bringing the Apostles up into his house, he spread a meal for them, and was filled with gladness, with his whole household, his faith resting on God.
Sai mai gadin kurkukun ya kawo su cikin gidansa ya ba su abinci; ya kuwa cika da murna don yă gaskata da Allah, shi da dukan iyalinsa.
35 In the morning the praetors sent their lictors with the order, "Release those men."
Da gari ya waye, sai alƙalan suka aika ma’aikatansu wajen mai gadin kurkukun da umarni cewa, “Ka saki mutanen nan.”
36 So the jailer brought Paul word, saying, "The praetors have sent orders for you to be released. Now therefore you can go, and proceed on your way in peace."
Sai mai gadin kurkukun ya gaya wa Bulus cewa, “Alƙalai sun ba da umarni a sake ku kai da Sila. Yanzu sai ku tafi. Ku sauka lafiya.”
37 But Paul said to them, "After cruelly beating us in public, without trial, Roman citizens though we are, they have thrown us into prison, and are they now going to send us away privately? No, indeed! Let them come in person and fetch us out."
Amma Bulus ya ce wa ma’aikatan, “Sun yi mana dūka a fili ba tare da shari’a ba, ko da yake mu’yan ƙasar Roma ne, suka kuma jefa mu cikin kurkuku. Yanzu suna so su fitar da mu a ɓoye? A’a! Sai dai su zo da kansu su rako mu waje.”
38 This answer the lictors took back to the praetors, who were alarmed when they were told that Paul and Silas were Roman citizens.
Sai ma’aikatan suka faɗa wa alƙalan wannan, da suka ji cewa Bulus da Sila Romawa ne, sai suka ji tsoro.
39 Accordingly they came and apologized to them; and, bringing them out, asked them to leave the city.
Sai suka zo don su roƙe su, suka yi musu rakiya daga kurkukun, suna roƙonsu su bar birnin.
40 Then Paul and Silas, having come out of the prison, went to Lydia's house; and, after seeing the brethren and encouraging them, they left Philippi.
Bayan Bulus da Sila suka fita daga kurkukun, sai suka tafi gidan Lidiya, inda suka sadu da’yan’uwa suka kuma ƙarfafa su. Sa’an nan suka tafi.