< Genesis 23 >

1 Sarah lived a hundred and twenty-seven years. These were the years of the life of Sarah.
Saratu ta yi shekara ɗari da ashirin da bakwai a duniya.
2 Sarah died in Kiriath Arba, that is, Hebron, in the land of Canaan. Abraham mourned and wept for Sarah.
Ta rasu a Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar Kan’ana, Ibrahim kuwa ya tafi ya yi makokin Saratu, yana kuka saboda ita.
3 Then Abraham rose up and went from his dead wife, and spoke to the sons of Heth, saying,
Sai Ibrahim ya tashi daga gefen matarsa da ta mutu, ya yi magana da Hittiyawa. Ya ce,
4 “I am a foreigner among you. Please grant me a property for a burial place among you, so that I may bury my dead.”
“Ni baƙo ne, kuma baƙo a cikinku. Ku sayar mini da wani wuri yă zama wurin binnewa a nan, domin in binne mataccena.”
5 The sons of Heth answered Abraham, saying,
Hittiyawa suka ce wa Ibrahim,
6 “Listen to us, my master. You are a prince of God among us. Bury your dead in the choicest of our tombs. None of us will refuse you his tomb, so that you may bury your dead.”
“Ranka yă daɗe, ka saurare mu. Kai babban yerima ne a cikinmu. Ka binne mataccenka a kabari mafi kyau na kaburburanmu. Babu waninmu da zai hana ka kabarinsa don binne mataccenka.”
7 Abraham arose and bowed down to the people of the land, to the sons of Heth.
Sai Ibrahim ya tashi ya rusuna a gaban mutanen ƙasar, wato, Hittiyawan.
8 He spoke to them, saying, “If you agree that I should bury my dead, then hear me and plead with Ephron son of Zohar, for me.
Ya ce musu, “In kuna so in binne mataccena, sai ku ji ni, ku roƙi Efron ɗan Zohar a madadina
9 Ask him to sell me the cave of Machpelah, which he owns, which is at the end of his field. For the full price let him sell it to me publicly as a property for a burial place.”
domin yă sayar mini da kogon Makfela, wanda yake nasa, wannan da yake a ƙarshen filinsa. Ku ce masa yă sayar mini a cikakken farashi, yă zama mallakata domin makabarta tsakaninku.”
10 Now Ephron was sitting among the sons of Heth, and Ephron the Hittite answered Abraham in the hearing of the sons of Heth, of all those who had come into the gate of his city, saying,
Efron mutumin Hitti yana zaune a cikin mutanensa, sai ya amsa wa Ibrahim a kunnuwan dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birni.
11 “No, my master, hear me. I give you the field, and the cave that is in it. I give it to you in the presence of the sons of my people. I give it to you to bury your dead.”
Ya ce, “A’a, ranka yă daɗe, ka ji ni, na ba ka filin, na kuma ba ka kogon da yake cikinsa. Na ba ka shi a gaban mutanena. Ka binne mataccenka.”
12 Then Abraham bowed himself down before the people of the land.
Ibrahim ya sāke rusuna a gaban mutanen ƙasar
13 He spoke to Ephron in the hearing of the people of the land, saying, “But if you are willing, please hear me. I will pay for the field. Take the money from me, and I will bury my dead there.”
ya ce wa Efron a kunnuwansu, “Ka ji, in ka yarda. Zan biya farashin filin. Ka karɓa daga gare ni don in iya binne mataccena a can.”
14 Ephron answered Abraham, saying,
Efron ya ce wa Ibrahim,
15 “Please, my master, listen to me. A piece of land worth four hundred shekels of silver, what is that between me and you? Bury your dead.”
“Ka saurare ni, ranka yă daɗe; darajan filin ya kai shekel ɗari huɗu na azurfa, amma mene ne wannan a tsakanina da kai? Ka binne mataccenka.”
16 Abraham listened to Ephron and Abraham weighed out to Ephron the amount of silver that he had spoken in the hearing of the sons of Heth, four hundred shekels of silver, according to the standard measurement of the merchants.
Ibrahim ya yarda da sharuɗan Efron, sai ya auna masa farashin da ya faɗa a kunnuwan Hittiyawa, shekel ɗari huɗu na azurfa, bisa ga ma’aunin da’yan kasuwa suke amfani da shi a lokacin.
17 So the field of Ephron, which was in Machpelah, which was next to Mamre, that is, the field, the cave that was in it, and all the trees that were in the field and all around its border, passed
Ta haka filin Efron a Makfela kusa da Mamre, wato, filin da kogon a cikinsa, da kuma dukan itatuwan da suke cikin iyakoki filin, aka
18 to Abraham by purchase in the presence of the sons of Heth, before all those who had come into the gate of his city.
ba wa Ibrahim a matsayin mallakarsa a gaban dukan Hittiyawa waɗanda suka zo ƙofar birnin.
19 After this, Abraham buried Sarah his wife in the cave of the field of Machpelah, which is next to Mamre, that is, Hebron, in the land of Canaan.
Bayan wannan Ibrahim ya binne matarsa Saratu a kogon a filin Makfela kusa da Mamre (wanda yake a Hebron) a ƙasar Kan’ana.
20 So the field and the cave in it passed to Abraham as a property for a burial place from the sons of Heth.
Da filin da kuma kogon da yake cikinsa, Hittiyawa suka tabbatar wa Ibrahim a matsayin makabarta.

< Genesis 23 >