< Genesis 22 >
1 It came about after these things that God tested Abraham. He said to him, “Abraham!” Abraham said, “Here I am.”
Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
2 Then God said, “Take your son, your only son, whom you love, Isaac, and go to the land of Moriah. Offer him there as a burnt offering upon one of the mountains there, which I will tell you about.”
Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
3 So Abraham rose early in the morning, saddled his donkey, and took two of his young men with him, along with Isaac his son. He cut the wood for the burnt offering, then set out on his journey to the place that God had told him about.
Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
4 On the third day Abraham looked up and saw the place afar off.
A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
5 Abraham said to his young men, “Stay here with the donkey, and I and the lad will go over there. We will worship and come again to you.”
Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
6 Then Abraham took the wood for the burnt offering and put it on Isaac his son. He took in his own hand the fire and the knife; and they went both of them together.
Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
7 Isaac spoke to Abraham his father and said, “My father,” and he said, “Here I am, my son.” He said, “See, here is the fire and the wood, but where is the lamb for the burnt offering?”
sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
8 Abraham said, “God himself will provide the lamb for the burnt offering, my son.” So they went on, both of them together.
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
9 When they came to the place that God had told him about, Abraham built an altar there and laid the wood on it. Then he bound Isaac his son, and laid him on the altar, on top of the wood.
Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
10 Abraham reached out with his hand and took up the knife to kill his son.
Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
11 Then the angel of Yahweh called to him from heaven and said, “Abraham, Abraham!” and he said, “Here I am.”
Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
12 He said, “Do not lay your hand upon the lad, nor do anything to harm him, for now I know that you fear God, seeing that you have not withheld your son, your only son, from me.”
Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
13 Abraham looked up and behold, behind him was a ram caught in the bushes by his horns. Abraham went and took the ram and offered him up as a burnt offering instead of his son.
Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
14 So Abraham called that place, “Yahweh will provide,” and it is said to this day, “On the mountain of Yahweh it will be provided.”
Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
15 The angel of Yahweh called to Abraham a second time from heaven
Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
16 and said—this is Yahweh's declaration—by myself I have sworn that because you have done this thing, and have not withheld your son, your only son,
ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
17 I will surely bless you and I will greatly multiply your descendants as the stars of the heavens, and as the sand which is upon the seashore; and your descendants will possess the gate of their enemies.
tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
18 Through your offspring all the nations of the earth will be blessed, because you have obeyed my voice.”
ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
19 So Abraham returned to his young men, and they departed and went together to Beersheba, and he lived at Beersheba.
Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
20 It came about after these things that Abraham was told, “Milkah has borne children, as well, to your brother Nahor.”
Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
21 They were Uz his firstborn, Buz his brother, Kemuel the father of Aram,
ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
22 Kesed, Hazo, Pildash, Jidlaph, and Bethuel.
Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
23 Bethuel became the father of Rebekah. These were the eight children that Milkah bore to Nahor, Abraham's brother.
Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
24 His concubine, whose name was Reumah, also bore Tebah, Gaham, Tahash, and Maacah.
Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.