< Psalms 137 >

1 When we [had been taken to] Babylonia, [far from Jerusalem], we sat down by the rivers there, and we cried when we thought about [the temple on] Zion [Hill in Jerusalem].
A bakin kogunan Babilon muka zauna muka yi kuka sa’ad da muka tuna da Sihiyona.
2 On the willow trees [alongside the rivers] we hung our harps [because we did not want to play them any more because we were very sad].
A can a kan rassan itatuwa muka rataye garayunmu,
3 The [soldiers] who had captured us [and taken us to Babylonia] told us to sing [for them]; they told us to (entertain them/make them happy), saying, “Sing for us one of the songs [that you previously sang in] Jerusalem!”
gama a can masu kamunmu suka sa mu yi waƙoƙi, masu ba mu azaba suka nema waƙoƙin farin ciki; suka ce, “Ku rera mana ɗaya daga cikin waƙoƙin Sihiyona!”
4 But [we thought], “We [are sad because we have been punished by Yahweh and brought to this] foreign land, so we cannot [RHQ] sing songs about Yahweh while we are here!”
Yaya za mu rera waƙoƙin Ubangiji a baƙuwar ƙasa?
5 If I forget about Jerusalem [APO], Iet my right hand wither [with the result that I will be unable to play my harp]
In na manta da ke, ya Urushalima, bari hannuna na dama manta da iyawarsa.
6 Do not allow me to sing again [MTY], if I forget about Jerusalem, if I do not consider that Jerusalem causes me to be more joyful than anything else does.
Bari harshena yă manne wa rufin bakina in ban tuna da ke ba, in ban so Urushalima farin cikin mafi girma ba.
7 Yahweh, [punish] the people of the Edom people-group for what they did on the day that the army of Babylon captured Jerusalem. Do not forget that they said, “Tear down all the buildings! Destroy them completely! Leave only the foundations!”
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da mutanen Edom suka yi a ranar da Urushalima ta fāɗi. Suka yi ihu suka ce, “A ragargaza ta, A ragargaza ta har tushenta!”
8 And you people of Babylon, you will certainly be destroyed! Those who punish you in return for what you did to us will be happy;
Ya Diyar Babilon, an ƙaddara ke zuwa hallaka, mai farin ciki ne wanda ya sāka miki saboda abin da kika yi mana,
9 they will take your babies and completely smash them on the rocks.
shi da ya ƙwace jariranki ya fyaɗa su a kan duwatsu.

< Psalms 137 >