< Genesis 22 >

1 Several years later, God tested Abraham [to find out] whether Abraham [really trusted in him and would obey him]. He called out to Abraham, and Abraham replied, “I’m here.”
Bayan abubuwan nan suka faru, sai Allah ya gwada Ibrahim. Ya ce masa, “Ibrahim!” Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
2 God said, “Your son, Isaac, whom you love very much, is the only son [who is still here with you]. But take him and go together to the Moriah region. Offer him as a sacrifice like a burnt offering, on a hill that I will show you.”
Sai Allah ya ce, “Ka ɗauki ɗanka, makaɗaicin ɗanka Ishaku, wanda kake ƙauna, ka tafi yankin Moriya, ka miƙa shi hadaya ta ƙonawa a can a kan ɗaya daga cikin duwatsun da zan nuna maka.”
3 So Abraham got up early the next morning, put a saddle on his donkey, and took with him two of his servants along with his son, Isaac. He also chopped some wood to kindle a fire for a burnt offering. Then they started traveling to the place God told him about.
Kashegari da sassafe, Ibrahim ya tashi ya ɗaura wa jakinsa sirdi. Ya ɗauki bayinsa biyu, da ɗansa Ishaku. Bayan ya faskare isashen itace saboda hadaya ta ƙonawa sai ya kama hanya zuwa wurin da Allah ya faɗa masa.
4 On the third day of their travels, Abraham looked up and saw in the distance the place where God wanted him to go.
A rana ta uku Ibrahim ya ɗaga ido sai ya ga wurin daga nesa.
5 Abraham said to his servants, “You two stay here with the donkey while the boy and I go over there. We will worship God there, and then we will come back to you.”
Ibrahim ya ce wa bayinsa, “Ku tsaya a nan da jakin, ni da yaron kuwa mu haura can. Za mu yi sujada sa’an nan mu komo wurinku.”
6 Then Abraham took the wood to kindle a fire for the burnt offering and placed it on his son Isaac, for him to carry. Abraham carried in his hand a [pan containing burning coals to start a] fire, and a knife, and the two of them walked along together.
Ibrahim ya ɗauki itace saboda hadaya ta ƙonawa ya ɗora wa ɗansa Ishaku, shi kuwa ya riƙe wuƙa da wutar. Yayinda su biyun suke tafiya,
7 Then Isaac spoke to his father Abraham, saying, “My father!” Abraham replied, “Yes, my son, I’m here!” Isaac said, “Look, we have wood and [coals to light] a fire, but where is the lamb for the burnt offering?”
sai Ishaku ya yi tambaya, ya ce wa mahaifinsa Ibrahim, “Baba?” Ibrahim ya ce masa, “Na’am ɗana!” Ishaku ya ce, “Ga dai wuta, ga kuma itace, amma ina ɗan ragon hadaya ta ƙonawa?”
8 Abraham replied, “My son, God himself will provide the lamb for the burnt offering.” So the two of them continued walking along together.
Ibrahim ya amsa ya ce, “Ɗana, Allah kansa zai tanada ɗan ragon hadayar ƙonawa.” Sai su biyu suka ci gaba da tafiya.
9 They arrived at the place God had told him about. There, Abraham built a stone altar and arranged the wood on top of it. Then he tied his son Isaac, and laid him on the altar on top of the wood.
Sa’ad da suka isa wurin da Allah ya faɗa masa, sai Ibrahim ya gina bagade a can, ya kuma shisshirya itacen a kai. Ya ɗaura ɗansa Ishaku, ya kwantar da shi a kan itacen, a bisa bagaden.
10 Then Abraham took the knife and reached out to kill his son.
Sa’an nan Ibrahim ya miƙa hannunsa ya ɗauki wuƙar don yă yanka ɗansa.
11 But an angel [who was really Yahweh] called to him from heaven and said, “Abraham! Abraham!” Abraham replied, “I’m here!”
Amma mala’ikan Ubangiji ya kira shi daga sama ya ce, “Ibrahim, Ibrahim!” Sai Ibrahim ya amsa ya ce, “Ga ni.”
12 The angel said, “Do not harm the boy or do anything to injure him, because now I know that you respect and obey God. I know that because you have not refused to sacrifice your son, the only son [who is still with you].”
Mala’ikan ya ce, “Kada ka yi wa yaron nan rauni. Kada kuma ka ji masa ciwo. Yanzu na san cewa kana tsoron Allah, gama ba ka hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba.”
13 Then Abraham looked up and saw that a ram was nearby, whose horns had been caught in a (thicket/clump of bushes). So Abraham went over and grabbed the ram [and killed it], and sacrificed it on the altar as a burnt offering, instead of his son.
Ibrahim ya ɗaga ido, ya duba, sai ya ga rago da ƙahoninsa a kafe a wani ɗan kurmi. Sai Ibrahim ya tafi ya kamo ragon ya miƙa shi hadaya ta ƙonawa a maimakon ɗansa.
14 Abraham named that place ‘Yahweh will provide’. And to the present day, people say, “On Yahweh’s mountain, he will provide.”
Ibrahim kuwa ya ba wa wurin suna, Ubangiji Zai Tanada. Gama kamar yadda ake ce har yă zuwa yau, “A bisan dutsen Ubangiji, za a tanada.”
15 The angel [who was really Yahweh] called out to Abraham from heaven a second time.
Mala’ikan Ubangiji ya kira Ibrahim daga sama sau na biyu
16 He said, “I, Yahweh your Lord, am telling you that you did what I told you, and you have not refused to sacrifice your only son [that is with you]. So I say, ‘I solemnly swear, with myself as my witness,
ya ce, “Na rantse da kaina, in ji Ubangiji, domin ka yi wannan, ba ka kuwa hana ni ɗanka, makaɗaicin ɗanka ba,
17 that some day your descendants will be as numerous as the stars in the sky and the grains of sand on the seashore. And your descendants will defeat their enemies and capture their cities [SYN].’
tabbatacce zan albarkace ka, zan kuma sa zuriyarka su yi yawa kamar taurari a sararin sama, kamar kuma yashi a bakin teku. Zuriyarka za su mallaki biranen abokan gābansu,
18 You obeyed me, so by means of your descendants the people of all the nations on the earth will be blessed.”
ta wurin zuriyarka kuma dukan al’umman duniya za su sami albarka, domin ka yi mini biyayya.”
19 Then Abraham and Isaac returned to where his servants were waiting, and they went back home together to Beersheba, and Abraham stayed there.
Sa’an nan Ibrahim ya koma wurin bayinsa, suka kuma kama hanya tare zuwa Beyersheba. Ibrahim kuwa ya yi zamansa a Beyersheba.
20 After these things happened, someone told Abraham, “Your brother Nahor’s wife, Milcah, has also given birth to children. She has eight sons.”
Bayan wani ɗan lokaci, sai aka faɗa wa Ibrahim cewa, “Ga shi, Milka ita ma ta haifa wa Nahor ɗan’uwanka,’ya’ya maza;
21 The oldest son was Uz. The next was Buz. After him was Kemuel, the father of Aram.
ɗan fari shi ne Uz, ɗan’uwansa kuma Buz, Kemuwel (shi ne mahaifin Aram),
22 After Kemuel was Kesad, then Hazo, then Pildash, then Jidlaph, then Bethuel,
Kesed, Hazo, Fildash; Yidlaf, da kuma Betuwel.”
23 who was the father of Rebekah, [who later became Isaac’s wife]. Those were the eight sons of Milcah, wife of Abraham’s brother, Nahor.
Betuwel ya haifi Rebeka. Milka ta haifa wa Nahor ɗan’uwan Ibrahim waɗannan’ya’ya maza takwas.
24 Nahor also had a (concubine/female slave whom he took as a wife), whose name was Beumah. She gave birth to four sons: Tebah, Gaham, Tahash, and Maacah.
Ban da haka ma, ƙwarƙwararsa, mai suna Reyuma, ta haifa masa’ya’ya maza, Teba, Gaham, Tahash da kuma Ma’aka.

< Genesis 22 >