< Genesis 20 >

1 Abraham left Mamre and moved southwest to the Negev desert and lived in a place named Gerar, between Kadesh and Shur.
Daga Mamre, Ibrahim ya kama hanya ya nufi wajajen Negeb, ya zauna a tsakanin Kadesh da Shur. Ya zauna a Gerar na ɗan lokaci,
2 While he was there, he told people that Sarah was his sister, not his wife. Then King Abimelech of Gerar sent some of his men to Sarah, and they brought her to him to be his wife.
a can ne Ibrahim ya ce game da matarsa Saratu, “Ita’yar’uwata ce.” Sai Abimelek sarkin Gerar ya aiko a kawo masa Saratu.
3 But God appeared to Abimelech in a dream during the night and said to him, “Listen to me! You are going to die because the woman you took is another man’s wife.”
Amma wata rana da dad dare Allah ya zo wa Abimelek a cikin mafarki ya ce masa, “Kai da matacce ɗaya kuke, saboda matar da ka ɗauka. Ita matar aure ce.”
4 But Abimelech had not had sex [EUP] with her, so he said, “God, since the people of my nation and I am innocent; will you kill me?
Abimelek dai bai riga ya kusace ta ba tukuna, saboda haka ya ce, “Ya Ubangiji za ka hallaka al’umma marar laifi?
5 He told me, ‘She is my sister,’ and she also said, ‘He is my brother.’ I did this with pure motives and I [SYN] have not done anything wrong yet.”
Ba shi ne ya ce mini, ‘Ita’yar’uwata ba ce,’ ita ma ba tă ce, ‘Shi ɗan’uwana ba ne’? Na yi haka da kyakkyawan nufi da hannuwa masu tsabta.”
6 God said to him in another dream, “Yes, I know that your motives were pure. That is why I truly prevented you from sinning against me. I did not allow you to have sex [EUP] with her.
Sai Allah ya ce masa a cikin mafarki “I, na san ka yi wannan da kyakkyawan nufi, saboda haka ne na kiyaye ka daga yin mini zunubi. Shi ya sa ban bar ka ka taɓa ta ba.
7 Now, return this man’s wife to her husband, because he is (a prophet/a man who receives messages from me). He will pray for you, and you will (remain alive/not die). But if you do not return her to him, you will certainly die, and all the members of your household will also certainly die.”
Yanzu ka komar da matar mutumin, gama shi annabi ne, zai kuma yi maka addu’a, za ka kuwa rayu. In ba ka komar da ita ba fa, ka sani tabbatacce kai da dukan abin da yake naka za ku mutu.”
8 Early the next morning, Abimelech summoned all his officials, and told them everything that had happened. When they heard that [MTY], his men were very afraid [that God would punish them].
Kashegari da sassafe, sai Abimelek ya tara dukan fadawansa, ya faɗa musu duk abin da ya faru, suka ji tsoro ƙwarai da gaske.
9 Abimelech then summoned Abraham, and said to him, “You should not have done that to us [RHQ]! Did I do something wrong to you, with the result that you are causing me and the people in [MTY] my kingdom to be guilty of committing a great sin [RHQ]? You have done things to me that (should not be done/you should not have done)!”
Sa’an nan Abimelek ya kira Ibrahim ciki ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Ta wace hanya ce na yi maka laifi har da ka kawo irin wannan babban laifi a kaina da kuma masarautata? Ka yi mini abubuwan da bai kamata a yi ba.”
10 Abimelech asked Abraham, “What was your reason for doing this?”
Abimelek ya kuma ce wa Ibrahim, “Me ya sa ka yi wannan?”
11 Abraham replied, “I said that because I thought, ‘They certainly do not respect God in this place. If they don’t respect God, they will not respect relationships with others. [If I say she is my sister, they will try to pay me a bride price] to get her. But if I say she is my wife, they will kill me to get her.’
Ibrahim ya ce, “Na ce a raina, ‘Tabbatacce babu tsoron Allah a wannan wuri, za su kuwa kashe ni saboda matata.’
12 Besides, she really [can be considered] my sister, because she is the daughter of my father, although she is not the daughter of my mother. She is the daughter of another woman, and I married her.
Ban da haka, tabbatacce ita’yar’uwata ce,’yar mahaifina, ko da yake ba daga uwata ba, ta kuma zama matata.
13 Later, when God told me to move away from my father’s household, I said to her, ‘This is the way you can show that you love me: Everywhere we go, say about me, “This is my brother.”’”
Sa’ad da Allah ya sa na tashi daga gidan mahaifina na ce mata, ‘Wannan shi ne yadda za ki nuna mini ƙaunarki. Duk inda muka tafi, ki ce game da ni, “Shi ɗan’uwana ne.”’”
14 So Abimelech brought some sheep and cattle and male and female slaves and gave them to Abraham. And he returned his wife Sarah to him.
Sai Abimelek ya kawo awaki da shanu da bayi maza da mata, ya ba wa Ibrahim, ya kuma komar da Saratu matarsa gare shi.
15 And Abimelech said to him, “Look! All my land is here in front of you. Live in whatever place you like!”
Abimelek ya kuma ce, “Ƙasata tana gabanka, ka zauna a duk inda kake so.”
16 And he said to Sarah, “Look here, I am giving 1,000 pieces of silver to your brother. This is to insure that no one will [bring up this matter again and] say that I have done something wrong. [EUP, IDM]”
Ga Saratu kuwa ya ce, “Ina ba wa ɗan’uwanki shekel dubu na azurfa, shaida ce ta tabbatarwa a idanun dukan waɗanda suke tare da ke, da kuma a gaban kowa cewa ba ki da laifi.”
17 Then Abraham prayed to God, and God healed Abimelech’s wife and his slave girls so that they could become pregnant.
Sai Ibrahim ya yi addu’a ga Allah, Allah kuma ya warkar da Abimelek, da matarsa da bayinsa mata domin su haihu,
18 This was because Yahweh had caused it to be impossible for any of the women in Abimelech’s household to bear children, because Abimelech had taken Abraham’s wife Sarah.
gama Ubangiji ya rufe kowace mahaifa a gidan Abimelek saboda Saratu, matar Ibrahim.

< Genesis 20 >