< Acts 8 >

1 Then some men who revered God buried Stephen’s body in a tomb, and they mourned greatly and loudly for him. On that same day [people] started severely persecuting the believers [who were living] in Jerusalem. So most [of the believers] fled [to other places] throughout Judea and Samaria [provinces]. The apostles were the only [believers who remained in Jerusalem].
Bulus ya amince da mutuwarsa. A wannan rana tsanani mai zafi ya fara tasowa akan Iklisiya da take a Urushalima, sai masu bangaskiya duka suka bazu ko ina a cikin garuruwan Yahudiya da Samariya, sai manzannin kadai aka bari.
2
Amintattun mutane suka bizne Istifanus suka yi babban makoki game da shi.
3 While the people were killing Stephen, Saul was there approving of their killing Stephen. So Saul [also] began trying to destroy the group of believers. He entered houses one by one, he dragged away men and women [who believed in Jesus], and then he [arranged for] them to be put in prison.
Amma Shawulu ya yi wa Iklisiya mugunta kwarai, ya dinga shiga gida gida yana jawo mutane maza da mata, kuma yana kulle su cikin kurkuku.
4 The believers who had left Jerusalem went to different places, where they continued preaching the message about Jesus.
Duk da haka masu bangaskiyar nan da suka warwatsu suka tafi suka dinga yada wa'azin maganar.
5 [One of those believers whose name was] Philip went down [from Jerusalem] to a city in Samaria [province]. There he was telling [the people that Jesus is] [MTY] the Messiah.
Filibus ya tafi can Samariya ya yi shelar Almasihu.
6 Many people there heard Philip [speak] and saw the miraculous things that he was doing. So they all (paid close attention to/listened carefully to) his words.
Da taron mutane suka ji kuma suka ga alamun da Filibus yake yi, sai suka mai da hankali dukansu domin su ji abinda yake fadi.
7 For [example, when Philip commanded] evil spirits who controlled many people [that they should come out of them], they came out, while those spirits screamed. Also, many people who were paralyzed and [many others] who were lame were healed.
Domin kazaman ruhohi sun fito daga cikin mutane da yawa da suka saurare shi suna kuka da kururuwa; nakasassun mutane dayawa da guragu suka warke.
8 So [many people] [MTY] in that city greatly rejoiced.
Kuma aka yi farin ciki mai girma a birnin.
9 There was a man in that city whose name was Simon. He had been practicing sorcery for a long time, and he had been amazing the people in Samaria [province by doing that]. He continually claimed that he was a great/important person.
Amma akwai wani mutum a cikin birnin da ake kira Siman, wanda tun farko shi masafi ne da kuma dan dabo, yana yi wa mutanen Samariya abubuwan ban mamaki, yayin da yake kiran kansa wani mai muhimmanci.
10 All the people there, both ordinary and important people, listened to him. [Various ones of] them were saying, “This man works in extremely powerful ways [because] God has caused him to be a great [person].”
Dukan Samariyawa, manya da yara, suna sauraronsa, su kan ce, ''Wannan mutum shine ikon Allahn nan wanda ake kira mai girma.''
11 They continued to listen to him carefully, because for a long time he had astonished them by practicing sorcery.
Suna sauraron sa, domin ya dade yana yi masu abubuwan mamaki da tsafe-tsafensa.
12 But then they believed Philip’s [message] when he preached to them about [how] God desires to rule [MET] [the lives of people who believe in him], and about Jesus being the Messiah [MTY]. Both the men and the women who believed in Jesus were baptized. {[Philip] was baptizing both the men and the women [who had come to believe in Jesus]}.
Amma da suka yi bangaskiya da wa'azin bisharar da Filibus yake yi game da mulkin Allah da sunan Yesu Almasihu, sai aka yi masu Baftisma dukansu maza da mata.
13 Simon himself believed [Philip’s message] and, after he was baptized {after [Philip] baptized him}, he began to constantly accompany Philip. Simon was continually amazed because he often saw [Philip] doing many kinds of miraculous things.
Har shima Siman da kansa ya ba da gaskiya. Bayan an yi masa Baftisma ya cigaba da bin Filibus, da ya ga ana nuna alamu da manyan ayyuka, sai ya yi mamaki.
14 When the apostles in Jerusalem heard that [many people] [PRS] [throughout] Samaria [district] had believed the message from God [about Jesus], they sent Peter and John there.
Da manzannin da ke Urushalima suka ji labarin Samariya ta karbi maganar Allah, sai suka aika masu Bitrus da Yahaya.
15 When Peter and John arrived in Samaria, they prayed for those [new believers] in order that the Holy Spirit’s [power] would come to them.
Da suka iso, suka yi masu addu'a, domin su karbi Ruhu Mai Tsarki.
16 [Peter and John realized that] the Holy Spirit had not yet begun to empower any of them. They had been baptized {[Philip] had baptized them} [because they had believed] in [MTY] the Lord Jesus, [but they did not know about the Holy Spirit].
Domin har wannan lokaci, Ruhu Mai Tsarki bai sauko kan kowannensu ba; an dai yi masu baftisma ne kadai cikin sunan Ubangiji Yesu.
17 [Then Peter and John] placed their hands on [the heads of] each person, and they received the [power of] [MTY] the Holy Spirit.
Sai Bitrus da Yahaya suka dora masu hannuwansu, sai suka karbi Ruhu Mai Tsarki.
18 Simon saw [things that convinced him] that [God] had given the Spirit’s [power to people] as a result of the apostles placing their hands on them. So he offered [to give] money to the apostles,
Sa'adda Siman yaga ana bayar da Ruhu Mai Tsarki ta wurin dorawar hannuwan manzanni, ya basu kudi.
19 saying, “Enable me also to do what [you are doing], so that everyone on whom I place/put my hands may receive the Holy Spirit’s [power].”
Ya ce, “Ku bani wannan iko, ni ma, don duk wanda na dora wa hannu ya karbi Ruhu Mai Tsarki.''
20 But Peter said to him, “May you [(sg)] and your money go to hell, because you [mistakenly] think that you can buy [from us] what God [alone] gives to [people] (questioned)
Amma Bitrus yace masa, ''Azurfarka ta lalace tare da kai, saboda kana tunanin za ka malaki baiwar Ubangiji da kudi.
21 [God] has not authorized you to have any part of this ministry of giving [the Holy Spirit’s power], because he knows that you are not thinking rightly! (OR, because he knows that you are thinking completely wrongly.)
Baka da wani rabo a wannan al'amari, domin zuciyarka ba daidai take da Allah ba.
22 So stop thinking wickedly [like] that, and plead that the Lord, if he is willing, will forgive you [for what] you [wickedly] thought/planned [to do]
Saboda haka ka tuba daga wannan muguntarka, ka kuma yi addu'a ga Ubangiji, domin mai yiwuwa ya gafarta maka game da manufar zuciyarka.
23 [Turn away from your evil ways], because I perceive that you [(sg)] are extremely envious of [us], and you [are] a slave of your [continual desire to do evil! God will certainly punish you severely]!”
Domin na gane kana cikin bacin rai da kuma cikin daurin zunubi.''
24 Then Simon answered, “Pray to the Lord [God] that [he] will not do to me what you just said!”
Siman ya amsa ya ce, ''Kayi addu'a ga Ubangiji domina, kada wani daga cikin abubuwan nan da ka fada ya faru da ni.''
25 After [Peter and John] told [people there] what they knew personally [about the] Lord [Jesus] and declared to them the message about Jesus, they both returned to Jerusalem. [Along the way] they preached the good message [about Jesus to people] in many villages in Samaria [province].
Sa'anda Bitrus da Yahaya suka bada shaida kuma suka fadi maganar Ubangiji, sun koma Urushalima; akan hanya, suka yi wa'azin bishara a kauyukan samariyawa da yawa.
26 [One day] an angel whom the Lord [God] had sent commanded Philip, “Get ready and go south along the road that extends from Jerusalem to Gaza.” [That was] a road in a desert area.
Yanzu kuwa Mala'ikan Ubangiji ya yi wa Filibus magana cewa, ''Tashi ka tafi ta kudu da hanyar da ta yi kasa daga Urushalima zuwa Gaza'' (wannan hanyar yana cikin hamada.)
27 So Philip got ready and went [along that road]. Suddenly he met a man from Ethiopia. He was an important official who took care of all the funds for the queen [of] Ethiopia. [In his language people called their queen] Candace. This man had gone to Jerusalem to worship [God],
Ya kuwa tashi ya tafi. Sai ga wani mutum daga Habasha, baba ne mai babban matsayi a karkashin Kandakatu, sarauniyar Habasha. Shine yake mulkin dukan dukiyarta. Ya zo Urushalima domin ya yi ibada.
28 and he was returning [home] and was seated [riding] in his chariot. [As he was riding], he was reading [out loud from] what the prophet Isaiah [had written] [MTY] [long ago].
Yana komawa zaune cikin karussarsa, kuma yana karanta Littafin annabi Ishaya.
29 [God’s] Spirit told Philip, “Go near to that chariot and keep walking close to [the man who is riding in] it!”
Ruhun ya ce wa Filibus, ''Ka je kusa da karussar nan.''
30 So Philip ran [to the chariot and kept running close to it]. Then he heard the official reading what the prophet Isaiah [had written]. He asked the man, “Do you [(sg)] understand what you are reading?”
Sai Filibus ya gudu ya same shi, kuma ya ji shi yana karanta littafin annabi Ishaya, sai ya ce, ''Ka fahimci abin da kake karantawa?''
31 He answered Philip, “[No!] (I cannot possibly [understand it] if [there is] no one to explain it to me!/How can I [understand it] if [there is] no one to explain it to me?) [RHQ]” Acts 8:31b-35 Then the man said to Philip, “Please come up [and] sit beside me.” [So Philip did that].
Bahabashen ya ce. ''Yaya zan iya, idan ba wani ya bishe ni ba?'' Ya roki Filibus ya shigo cikin karussar ya zauna tare da shi.
32 The part of the Scriptures that the official was reading was this: He will [be silent when] they lead him away to kill him [like when] a sheep [is led away to be killed]. As a young sheep is silent when its wool is being cut off {someone cuts off its wool}, [similarly] he will not protest [MTY] [when people cause him to suffer].
Wannan kuwa shine nassin da Bahabashen yake karantawa, ''An kai shi kamar tunkiya zuwa mayanka; shiru kuma, kamar dan rago a hannun masu sosayarsa, bai bude baki ba.
33 When he will be humiliated by being accused falsely {people will humiliate him [by accusing him falsely]}, [the rulers] (will not consider him innocent/will consider him guilty). No one will possibly be able to tell about his descendants, because he will be killed {people will kill him} without him having [any descendants] on the earth.
Cikin kaskancinsa aka yi masa shari'a da rashin adalci: Wa zai bada tarihin tsararsa? Domin an dauke ransa daga duniya.''
34 The official asked Philip [about these words that he was reading], “Tell me, who was the prophet writing about? [Was he writing] about himself or about someone else?”
Sai baban ya tambayi Filibus, ya ce, ''Na roke ka, gaya mani, game da wa annabin yake magana? Da kansa, ko kuwa wani mutum dabam?''
35 So Philip began [to explain] that Scripture passage. He told him the good message about [MTY] Jesus. [So the official understood and believed in Jesus].
Filibus ya fara magana; akan littafin Ishaya, ya kuwa yi masa wa'azi akan Yesu.
36 While they were traveling along the road, they came to [a place where there was a pond of] water [near the road]. Then the official said [to Philip], “Look, [there is a pond of] water! (I would like you to baptize me, because I do not know of anything that would prevent me from being baptized {prevent [you] from baptizing me.}/Do you know of anything that would prevent me from being baptized {prevent [you] from baptizing me}?) [RHQ]”
Yayin da suke tafiya akan hanya, sai suka iso bakin wani kogi; Baban ya ce, “Duba, ga ruwa anan; me zai hana ayi mani baftisma?”
Filibus ya ce,” Idan ka gaskanta da zuciya daya, ana iya yi maka baftisma.” Sai Bahabashen ya ce, “Na gaskata Yesu Almasihu shine Dan Allah.”
38 So the official told [the driver] to stop the chariot. Then both Philip and the official went down into the [pond of] water, and [Philip] baptized him.
Sai Bahabashen ya umarta a tsai da karussar. Sai suka zo wurin ruwa dukan su biyu, Filibus da baban, Filibus kuwa yayi masa baftisma.
39 When they came up out of the water, suddenly God’s Spirit took Philip away. The official never saw Philip again. But [although he never saw Philip again], the official continued going along the road, very happy [that God had saved him].
Yayin da suka fito daga cikin ruwan, Ruhun Ubangiji ya dauke Filibus; baban bai sake ganin shi ba, sai ya ci gaba da tafiyar sa yana murna.
40 Philip then realized [that the Spirit had miraculously taken him to] Azotus [town]. While he traveled around [in that region], he continued proclaiming the message [about Jesus] in all the towns [between Azotus and Caesarea. And he was still proclaiming] it when he finally arrived in Caesarea [city].
Amma Filibus ya bayyana a Azotus. Ya ratsa wannan yankin yana wa'azin bishara a dukan garuruwan, har sa'anda ya iso Kaisariya.

< Acts 8 >