< Acts 7 >
1 Then the high priest asked Stephen, “Are the things that [these people are saying about you(sg)] true?”
Sai babban firist ya ce, ''Wadannan al'amura gaskiya ne?''
2 Stephen replied, “Fellow Jews and respected leaders, [please] listen to me! The glorious God [whom we(inc) worship] appeared to our ancestor Abraham while he was still [living] in Mesopotamia [region], before he moved to Haran [town].
Sai Istifanus ya amsa ya ce, ''Ya 'yan'uwa da ubanni, ku saurare ni, Allah Madaukaki ya bayyana ga ubanmu Ibrahim tun yana can kasar Mesofotamiya, kafin ma ya zauna a kasar Haran;
3 God said to him, ‘Leave this land where you [(sg)] and your relatives [are living], and go into the land to which I will lead you.’
ya ce masa, 'Ka bar kasarka da danginka, ka tafi kasar da zan nuna maka.'
4 So Abraham left that land, [which was also called] Chaldea, and he arrived in Haran and lived there. After his father died, God told him to move to this land in which you [and I] are now living.”
Sa'annan ya bar kasar Kaldiyawa ya zo ya zauna a Haran; daga can, bayan rasuwar mahaifinsa, sai Allah ya kira shi zuwa wannan kasa da kuke ciki.
5 “[At that time] God did not give Abraham any [land here], not even a small plot of [this] land that would belong to him. God promised that he would [later] give this land to him and his descendants, and that it would [always] belong [to them. However], at that time Abraham did not have any children [who would] ([inherit it/receive it after he died]).”
Amma Allah bai ba shi kasar gado ba tukuna, ko da misalin tafin sawunsa. Amma ya alkawarta - ko da yake bai riga ya haifi da ba tukuna - wanda zai ba shi kasar gado, shi da zuriyarsa, a bayansa.
6 “[Later] God told Abraham, ‘Your descendants will go and live in a foreign country. They [will live there] for 400 years, and [during that time their leaders] will mistreat your descendants and force them to work as slaves.’
Allah ya yi magana da shi kamar haka, cewa zuriyarsa za su yi bakonci a wata kasa wadda ba tasu ba, mutanen wannan kasar kuwa za su gwada masu bakar azaba su kuma bautar da su har shekaru dari hudu.
7 But God [also] said, ‘I will punish the people who make them work as slaves. Then, after that, your descendants will leave [that land] and they will [come and] worship me in this land.’”
'Kuma zan hukunta wannan al'umma da ta bautar da su,' Allah ya ce, 'Bayan haka za su fito daga wannan kasa su bauta mini a wannan wuri.'
8 “Then God commanded Abraham that [every male in his household and all of his male descendants] should be circumcised [to show that they all belonged to God] and that they would obey what he had told Abraham to do. Later Abraham’s son, Isaac, was born, and when Isaac was eight days old, Abraham circumcised him. [Later] Isaac’s son, Jacob, was born, and Isaac [similarly circumcised] him. And Jacob [similarly circumcised] his twelve sons. They are the twelve men [from whom we(inc) Jews have all descended].”
Allah ya ba Ibrahim alkawarin kaciya, sai Ibrahim ya haifi Ishaku ya yi masa kaciya a rana ta takwas; Ishaku ya haifi Yakubu, Yakubu kuma ya haifi ubanni Isra'ila su goma sha biyu.
9 “[You know that] Jacob’s [older] sons became jealous [because their father favored their younger brother] Joseph. So they sold him [to merchants/traders who took him] [MTY] to Egypt. There he became a slave [of an official who lived there]. But God [helped] Joseph.
Wadannan 'yan'uwa suka yi kyashin danuwansu Yusifu suka sayar da shi bauta zuwa Masar. Amma Allah na tare da shi.
10 He protected him whenever people caused him to suffer. He enabled Joseph to be wise; and he caused Pharaoh, the king of Egypt, to think well of Joseph. So Pharaoh appointed him to rule [over] Egypt and to look after all of Pharaoh’s property [MTY].”
Ya kuwa cece shi daga dukan sharin da yan uwansa suka kulla masa, Allah kuwa ya ba shi tagomashi da hikima a gaban Fir'auna, sarkin Masar. Fir'auna kuwa ya mai da shi mai mulki a dukan kasar Masar da kuma dukan mallakarsa.
11 “[While Joseph was doing that work], there was a time (when there was very little food/of famine) throughout Egypt and also throughout Canaan. People did not have enough food to eat. People were suffering. [At that time] Jacob and his sons [in Canaan] also could not find [enough] food.
Sai aka yi babbar yunwa a dukan kasar Masar da ta Kan'ana, iyayenmu suka sha wuya saboda rashin abinci.
12 When Jacob heard [people report that] there was grain/food [that people could buy] in Egypt, he sent Joseph’s older brothers [to go there to buy grain. They went and bought grain from Joseph, but they did not recognize him. Then they returned home].
Amma lokacin da Yakubu ya ji akwai hatsi a kasar Masar, sai ya aiki ubannimu a karo na farko.
13 When Joseph’s brothers went to Egypt the second time, [they again bought grain from Joseph]. But this time [he] told them who he was. [And] people told Pharaoh that Joseph’s people were Hebrews [and that those men who had come from Canaan were his brothers].
Da suka je a karo na biyu, sai Yusifu ya bayyana kansa ga yanuwansa; a wannan lokaci ne Fir'auna ya gane da yanuwan Yusufu.
14 Then after Joseph sent [his brothers back home, they] told their father Jacob [that Joseph wanted] him and his entire family to come [to Egypt. At that time] ([Jacob’s family consisted of] 75 people/there were 75 people in Jacob’s family) [SYN].
Yusufu ya aiki yanuwansa su kawo Yakubu ubansu da dukan mallakarsu da iyalansu zuwa Masar, Dukansu mutane saba'in da biyar ne.
15 [So when] Jacob [heard that, he and all his family] went to [live in] Egypt.” Acts 7:15b-16 “[Later on], Jacob died [there], and our [other] ancestors, [his sons, also died there].
Yakubu ya tafi ya zauna a Masar; shi da zuriyarsa har mutuwar su.
16 [But] the bodies [of Jacob and Joseph] were brought {[they] brought the bodies [of Jacob and Joseph]} [back to our land], and [Jacob’s body] was buried {they buried [Jacob’s body]} [in the tomb that Abraham had bought, and they buried Joseph’s body] in Shechem in the ground that [Jacob] had bought from Hamor’s sons.”
Aka dauke su zuwa Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya da kudin azurfa daga hannun yayan Hamor a Shekem.
17 “Our ancestors had become very numerous when it was almost time for [God to rescue them] from Egypt, [as] he had promised Abraham that he would do.
Yayin da alkawarin Allah ya kusato wanda Allah ya fada wa Ibrahim, mutanen suka karu suka hayayyafa kwarai a Masar,
18 Another king had begun to rule in Egypt. He did not know that Joseph, [long before that time, had greatly helped the people of Egypt] [MTY].
Sai a ka yi wani sarki a Masar wanda bai san Yusifu ba,
19 That king cruelly tried to get rid of our ancestors. He oppressed them and caused them to suffer greatly. He [even commanded] them to leave their baby [boys] outside [their homes] so that they would die.”
Wannan sarki ya yaudari kakkaninmu ya yi masu mugunta kwarai da gaske, har ma ya kai ga suna barin jariransu cikin hasari don su ceci rayukansu.
20 “During that time Moses was born, and he was a very beautiful [LIT] [child]. So his parents [secretly] cared for him in their house for three months.
A wannan lokaci ne aka haifi Musa, kuma kyakkyawan yaro ne sai aka yi renon sa tsawon wata uku a gidan mahaifinsa a asirce.
21 Then they had to put him outside [the house, but] Pharaoh’s daughter [found him and] adopted him and cared for him as [though he were] her own son.
Yayin da aka jefar da shi, sai diyar Fir'auna ta dauke shi ta rene shi kamar danta.
22 Moses was taught {[The Egyptian teachers] taught Moses} many kinds of wise things [HYP] that the people in Egypt knew, and [when he grew up], he spoke powerfully and did things powerfully.”
Aka ilimantar da Musa da dukan ilimi irin na Masar; kuma ya shahara cikin fasahar magana da kuma ayyukansa.
23 “[One day] when Moses was about 40 years old, he decided that he would [go and] see his fellow Israelis. [So he went to the place where they worked].
Amma lokacin da yakai shekara arba'in, sai ya yi niyyar ya ziyarci 'yan'uwansa, Isra'ilawa.
24 He saw an Egyptian beating one of the Israelis. So he went over to help [MTY] the Israeli man who was being hurt/beat {whom [the Egyptian] was hurting/beating}, and he (got revenge on/paid back) the Israeli man by killing the Egyptian [who was hurting/beating him].
Sai ya ga wani na cin zalin Ba Isra'ile, Musa kuwa ya taimaki wanda ake kwara ta wurin murkushe Bamasaren:
25 Moses was thinking that his fellow Israelis would understand that God had sent him to free them [from being slaves]. But they did not understand that.
zaton Musa 'yan'uwansa za su fahimci taimakon Allah ne ya zo masu amma ina! Basu gane ba.
26 The next day, Moses saw two Israeli men fighting [each other]. He tried to make them stop fighting by saying to them, ‘Men, you two are fellow [Israelis! So] (stop hurting each other!/why are you hurting each other?) [RHQ]’
Washegari ya ga wasu Isra'ilawa na fada da junansu; ya yi kokari ya raba su; sai ya ce masu, 'Malamai, ku 'yan'uwan juna ne; don me kuke fada da junanku?'
27 But the man who was injuring the other man pushed Moses away and said to him, ‘(No one appointed you [(sg)] to rule and judge us [(exc)]!/Do you [(sg)] think someone appointed you [(sg)] to rule and judge us [(exc)]?) [RHQ]
Amma shi wanda ake kwarar makwabcinsa ya ture Musa a gefe guda, ya ce, 'Wa ya nada ka shugaba ko alkali akanmu?
28 Do you want to kill me as you killed the Egyptian yesterday?’
Kana so ka kashe ni ne, kamar yadda ka kashe Bamasaren nan jiya?'
29 When Moses heard that, [he thought to himself, ‘Obviously, people know what I have done, and someone will kill me.’ He was afraid, so] he fled [from Egypt] to Midian land. He lived there [for some years]. He [got married, and he and his wife] had two sons.”
Da jin haka sai Musa ya gudu, zuwa kasar Midinawa, a matsayin dan gudun hijira. Anan ya haifi ''ya'ya biyu maza.
30 “[One day] 40 years later, [the Lord God appeared as] an angel to Moses. He appeared in a bush that was burning in the desert near Sinai Mountain.
Bayan da shekaru arba'in suka wuce, sai mala'ika ya bayyana gare shi a jeji, kusa da dutsen Sinai, a cikin harshen wuta a cikin jeji.
31 When Moses saw that, he was greatly surprised, [because the bush was not burning up]. As he went over to look more closely, he heard the Lord [God] say [to him],
Sa'adda Musa ya ga wutar, mamaki ya kama shi; sai ya maso kusa don ya kara dubawa, sai ya ji muryar Ubangiji na cewa,
32 ‘I [am] the God [whom] your ancestors [worshipped]. I [am] the God that Abraham, Isaac and Jacob [worship].’ Moses [was so afraid that he] began to shake. He was afraid to look [at the bush any longer].
'Nine Allah na ubanninka, Ibrahim, da na Ishaku, da na Yakubu.' Musa ya razana har ma bai sake daga kai ya duba ba.
33 Then the Lord [God] said to him, ‘Take your sandals off [to show that you(sg) revere me]. Because I [am here], the place where you are standing is holy/sacred.
Ubangiji ya ce masa, 'Tube takalminka, domin in da kake tsaye wuri mai tsarki ne.
34 I have surely seen how the people of Egypt are continually causing my people to suffer. I have heard my people when they groan [because those people continually oppress them]. So I have come down to rescue them [from Egypt]. Now get ready, because I am going to send you [back] to Egypt [to do that].’”
Ba shakka na ga wahalar da mutane na ke sha a Masar, kuma na ji nishinsu, don haka na zo in cece su, yanzu fa sai ka zo, in aike ka zuwa Masar.'
35 “This Moses [is the one who had tried to help our Israeli people, but] whom they rejected [by saying], ‘No one [RHQ] appointed you to rule and judge [us!’] Moses [is the one whom] God [himself] sent to rule them and to free them [from being slaves. He is the one whom] an angel in the bush [commanded to do that].
Wannan fa shine Musan da suka ki, harma da cewa, 'Wanene ya nada ka alkali ko shugaba a kanmu?' Shine kuma wanda Allah ya aiko masu a matsayin shugaba da kuma mai ceto. Allah ya aiko shi ta hannun mala'ikan da ya gani a daji.
36 Moses [is the one who] led our ancestors out [from Egypt]. He did many kinds of miracles in Egypt, at the Red Sea, and during the 40 years [that the Israelite people lived] in the desert.
Bayan alamu da al'ajibai iri-iri a Masar da kuma Baharmaliya, Musa ya fito da su daga Masar da kuma cikin jeji, a lokacin da suka yi tafiya shekara arbain.
37 This Moses is the one who said to the Israelite people, ‘God will appoint a prophet for you from among your own people. [He will speak words from God], just like I [speak his words to you].’
Wannan shine Musan da ya cewa Isra'ilawa, 'Ubangiji zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin Yan'uwan ku.'
38 This man [Moses] was [our people’s leader] when they gathered together in the desert. It is Moses to whom [God sent] the angel on Sinai Mountain to [give him our laws], and [he was the one who told] our [other] ancestors [what the angel had said]. He was the one who received [from God] words that tell us how to live [eternally, and Moses] passed [them] on to us.”
Wannan shine mutumin da ke tare da mutane a jeji. Karkashin jagorancin mala'ikan da ya yi magana da shi a dutsen Sinai. Wannan ne mutumin da ke tare da ubannen mu, wannan shi ne mutumin da ya ba mu maganar Allah mai rai.
39 “[However], our ancestors did not want to obey [Moses]. Instead, [while he was still on the mountain], they rejected him [as their leader] and decided that they wanted to return to Egypt.
Wannan shine mutumin da ubannenmu suka ki su yi masa biyayya; su ka fitar da shi daga cikinsu, suka kudurta a zuciyarsu za su koma masar.
40 So they told [his older brother] Aaron, ‘Make idols for us who will be our gods to lead us [back to Egypt]! As for that fellow Moses who led us out of Egypt we [(exc)] do not know what has happened to him!’
A lokacin ne suka cewa Haruna, 'ya yi masu allolin da za su jagorance su zuwa masar. Domin kuwa ga zancen Musan nan da ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.'
41 So, they made [out of gold] an image [that looked like] a calf. Then they sacrificed [animals and offered other things] to [honor] that idol, and they sang and danced to honor the idol that they themselves had made.
Sai suka kera dan maraki suka kawo wa gunkin hadaya, suka yi murna da abin da hannayensu suka kera.
42 So God rejected them. He abandoned them to worship the sun, moon and stars in the sky. This agrees with the words that one of the prophets wrote that God said, You Israelite [people] [MTY], when you [repeatedly] killed animals and offered them as sacrifices during those 40 years [that you were] in the desert, (you [most certainly] were not offering them to me!/what makes you think that you were offering them to me?) [RHQ]
Allah ya bashe su su bauta wa tauraran sama, kamar yadda yake a rubuce cikin littattafafan annabawa, 'Kun mika mani hadayu na yankakkun dabbobi a jeji ne a shekaru arba'in din nan ya ku Isra'ilawa?'
43 [On the contrary], you carried [with you from place to place] the tent [that contained the idol] representing [the god] Molech [that you worshipped]. You also [carried with you] the image of the star [called] Rephan. [Those] were idols that you had made, [and you] worshipped [them instead of me]. So I will [cause you to] be taken away {[people to] take you} [from your own country. You will be taken] {[They will take you]} [far from your homes to regions] even farther than Babylon [Country].”
Kun yarda da haikalin Molek da kuma tauraron allahn nan Rafem, da kuma siffofin nan da kuka kera don ku yi masu sujada; don haka zan kai ku bauta har gaba da Babila.'
44 “While our ancestors were in the desert, they worshipped God at the tent that showed [that he was there with them]. They had made the tent exactly like God had commanded Moses [to make it. It was] exactly like the model that Moses had seen [when he was up on the mountain].
Kakkaninmu suna da alfarwa ta sujada domin shaida a cikin jeji, kamar yadda Allah ya umarta yayin da ya yi magana da Musa, cewa ya yi shi bisa ga salon da aka nuna mashi.
45 [Later on], other ancestors of ours carried that tent with them when Joshua led them [into this land]. That was during the time that they took this land for themselves, when God forced the people [who previously lived here] to leave. So the Israelis were able to possess this land. [The tent remained in this land and was still here] when [King] David ruled.
Wannan shine Alfarwar da kakkaninmu suka zo da shi, a lokacin Joshuwa. Wannan ya faru ne yayin da suka mallaki wannan kasa ta al'ummai da Allah ya kora a gaban kakkaninmu. Haka abin yake har ya zuwa zamanin Dauda,
46 David pleased God, and he asked God to let him build a house where [he and] all of our Israeli people could worship God.
wanda ya sami tagomashi a wurin Allah; don ya gina masujada domin Allah na Yakubu.
47 But [instead, God let David’s son] Solomon build a house [where people could worship] God.”
Amma Sulaimanu ne ya gina Gidan Allah.
48 “However, [we(inc) know that] God is greater than everything, and he does not live in [houses that] people [SYN] have made. It is like the prophet [Isaiah] wrote. He wrote [these words that God had spoken: ]
Sai dai Madaukaki ba yakan zauna a gidan da hannaye suka gina ba, kamar yadda annabin ya ce,
49 Heaven is (my throne/the place from which I rule the entire universe), and the earth is (my footstool/[merely like] a stool on which I may rest my feet). I myself [SYN] have made everything [both in heaven and on the earth]. So you [human beings], ([you] really cannot build a house that would be [adequate] for me!/do you think you can build a house that would be [appropriate] for me?) [RHQ] You cannot [RHQ] make a place good enough for me [to live in]!”
'Sama kursiyina ce, duniya kuwa wurin ajjiye sawayena ne. To wane irin gida za ku gina mani? inji Ubangiji: ko kuwa ina ne wurin da zan huta?
Ko ba hannayena ne suka yi dukan wadannan ba?'
51 “You people are extremely stubborn [MET], not wanting to obey God or listen [MTY] [to him!] You are exactly like your ancestors! You always resist the Holy Spirit [as they did]!
Ku mutane masu taurin kai masu zuciya mara kaciya da kunnuwa marasa ji, kullum kuna gaba da Ruhu Mai Tsarki, kuna aikata abin da kakkaninku suka aikata.
52 Your ancestors caused [RHQ] every prophet to suffer, [including Moses]. They even killed those who long ago announced [that the Messiah] would come, the one who always did what pleased God. [And the Messiah has come! He is the one whom] you [recently] turned over [to his enemies] and [insisted that] they kill him!
Wane annabi ne kakkaninku ba su tsanantawa ba? Sun kashe annabawan da suka rigayi zuwan Mai Adalcin nan, kuma kun zama wadanda suka kasance masu bashe shi da masu kashe shi,
53 You [are the people] who have received God’s laws. [Those were laws] that God caused angels to give [to our ancestors]. However, [incredibly], you have not obeyed them!”
kune mutanen da kuka karbi shari'a wadda mala'iku suka bayar, amma ba ku kiyaye ta ba”.
54 When the Jewish Council members [and others there] heard all that [Stephen said], they became very angry. They were grinding their teeth [together because they were so angry] at him!
Yayin da majalisar suka ji wannan, sai ransu ya baci kwarai, har suna cizon hakoransu don gaba da Istifanus.
55 But the Holy Spirit completely controlled Stephen. He looked up into heaven and saw a dazzling light from God, and [he saw] Jesus standing at God’s right side.
Amma shi, cike da Ruhu Mai Tsarki, sai ya daga idonsa sama, ya ga daukakar Allah; ya kuma hango Yesu na tsaye a hannun daman Allah.
56 “Look,” he said, “I see heaven open, and I [see] the one who came from heaven standing at God’s right side!”
Istifanus ya ce, “Duba, ina ganin sama ta bude, ga Dan Mutum na tsaye a hannun dama na Allah.”
57 [When the Jewish Council members and others heard that], they shouted loudly. They put their hands over their ears [so that they could not hear Stephen, and immediately] they all rushed at him.
Amma yan majalisar suka daga murya da karfi, suka yi ihu, suka kuma toshe kunnuwansu, gaba dayansu suka afka masa;
58 They dragged him outside the city [of Jerusalem] and started to throw stones at him. The people who were accusing him [took off] their outer garments [in order to throw stones more easily, and] they put their clothes [on the ground] next to a young man whose name was Saul, [so that he could guard them].
suka fitar da shi bayan gari, suka jejjefe shi da duwatsu, don shaida sai suka tube manyan rigunansu suka ajiye a gaban wani matashi da ake ce da shi Shawulu.
59 While they continued to throw stones at Stephen, Stephen prayed, “Lord Jesus, receive my spirit!”
Lokacin da suke kan jifan Istifanus, ya dinga kira yana cewa, ''Ya Ubangiji Yesu, ka karbi ruhu na.”
60 Then Stephen fell on his knees and cried out, “Lord, do not punish them (OR, forgive them) [LIT] for this sin!” After he had said that, he died.
Ya durkusa ya daga murya da karfi, ya ce, “Ya Ubangiji, kada ka rike wannan zunubi a kansu.” Yayin da ya fadi wannan, sai ya yi barci.