< Nahum 2 >

1 He has come up [one who] scatters on face your guard [the] fortification watch [the] road strengthen [the] loins make strong strength exceedingly.
Mai hari yana matsowa a kanki, Ninebe. Ki tsare mafaka, ki yi gadin hanya ki sha ɗamara ki tattaro dukan ƙarfinki!
2 For he will restore Yahweh [the] majesty of Jacob like [the] majesty of Israel for they have laid waste to them [those who] lay waste and branches their they have destroyed.
Ubangiji zai maido da darajar Yaƙub, kamar ta Isra’ila, ko da yake masu washewa sun washe su suka kuma lalatar da inabinsu.
3 [the] shield of Warriors his [is] dyed red men of strength [are] clothed in scarlet [are] in fire of iron the chariotry on [the] day prepares he and the cypresses they have been made to quiver.
Garkuwoyin sojojinsa ja wur ne; jarumawansa suna sanye da kaya masu ruwan jan garura. Ƙarafan kekunan yaƙi suna walƙiya a ranar da aka shirya su; ana kaɗa māsu da bantsoro.
4 In the streets they drive madly the chariotry they rush around! in the open places appearance their [are] like torches like lightning flashes they run around.
Kekunan yaƙi sun zabura a tituna, suna kai da kawowa a dandali. Suna walƙiya kamar tocila suna sheƙawa a guje kamar walƙiya.
5 He remembers nobles his they stumble (on journey their *Q(K)*) they hurry wall its and it is prepared the cover.
Ninebe ta tattara rundunarta, duk da haka sun yi ta tuntuɓe a kan hanyarsu. Sun ruga zuwa katangan birnin, sun sanya garkuwar kāriya a inda ya kamata.
6 [the] gates of The rivers they have been opened and the palace it has melted away.
An buɗe ƙofofin rafuffukan sai wurin ya rurrushe.
7 And it has been fixed it was uncovered it was taken away and maidservants its [are] moaning like [the] sound of doves [they are] beating on hearts their.
An umarta cewa birnin za tă tafi bauta, za a kuma yi gaba da su. Bayi’yan mata suna kuka kamar tattabaru suna buga ƙirjinsu.
8 And Nineveh [was] like a pool of water from [the] days of it and they [are] fleeing stop stop and there not [is one who] turns back.
Ninebe tana kama da tafki, wanda ruwanta yana yoyo. Suna kuka suna cewa, “Ku tsaya! Ku tsaya,” amma ba wanda ya waiga.
9 Plunder silver plunder gold and there not [is] an end to the supply abundance from every article of preciousness.
A washe azurfa; a washe zinariya; dukiyarsu ba ta da iyaka, arzikinsu kuma ba ya ƙarewa.
10 Emptiness and emptiness and devastation and heart [is] melting and [are] tottering knees and anguish [is] in all loins and [the] faces of all of them they have gathered a glow.
Ta zama wofi, an washe ta, an tuɓe ta! Zukata sun narke, gwiwoyi suna kaɗuwa, jikuna suna rawa, fuskoki duk sun kwantsare!
11 Where? [is the] dwelling place of lions and [is] pasture it for young lions where it walked lion lioness there cub of lion and there not [was one who] disturbed [them].
Ina kogon zakokin nan yake yanzu, inda suka ciyar da’ya’yansu, inda zaki da zakanya sukan shiga, da’ya’yansu, ba mai damunsu
12 [the] lion [was] tearing For [the] sufficiency of cubs its and [was] strangling for lionesses its and it filled prey hole its and dens its torn flesh.
Zaki ya kashe abin da ya ishe’ya’yansa ya kuma murɗe wuyan dabbobi ya cika wurin zamansa da abin da ya kama ya cika kogwanninsa da abin da ya kashe.
13 Here I [am] against you [the] utterance of Yahweh of hosts and I will burn in smoke chariotry its and young lions your it will consume [the] sword and I will cut off from [the] earth prey your and not it will be heard again [the] voice of messengers your.
“Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ƙone kekunan yaƙinki, takobi kuma zai fafare’ya’yan zakokinki. Ba kuma zan bar miki namun jejin da za ki kashe a duniya ba. Ba kuwa za a ƙara jin muryar’yan saƙonki ba.”

< Nahum 2 >