< Habakkuk 1 >

1 The oracle which he saw Habakkuk the prophet.
Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
2 Until when? O Yahweh have I cried for help and not you will hear I cry out to you violence and not you save.
Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
3 Why? do you make see me wickedness and mischief do you look at? and devastation and violence [are] to before me and it has been strife and contention it arises.
Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
4 There-fore it grows numb [the] law and not it comes forth to perpetuity justice for [the] wicked [is] surrounding the righteous [person] there-fore it comes forth justice perverted.
Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
5 See among the nations and look and be astounded be astonished for a deed [I am] about to do in days your [which] not you will believe if it will be recounted.
“Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
6 For here I [am] about to raise up the Chaldeans the nation bitter and impetuous which goes to [the] expanses of [the] earth to take possession of dwellings [which] not [belong] to it.
Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
7 [is] terrifying And awesome it from itself justice its and dignity its it comes forth.
Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
8 And they are swift more than leopards horses its and they are keen more than wolves of [the] evening and they paw [the] ground warhorses its and horsemen its from a distance they come they fly like an eagle making haste to devour.
Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
9 All of it for violence it comes [the] totality of faces their [is] east-ward and it gathered like sand captive[s].
duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
10 And it kings it derides and rulers [are] laughter to it it at every fortress it laughs and it heaped up earth and it captured it.
Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
11 Then it swept on a wind and it passed on and he is guilty [the one] who strength his [becomes] god his.
Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
12 ¿ Not [are] you from antiquity O Yahweh God my holy [one] my not we will die O Yahweh to judgment you have appointed it and O rock to reprove you have established it.
Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
13 [you are too] pure of Eyes for seeing evil and to look to mischief not you are able why? do you look at treacherous [people] are you silent? when swallows up a wicked [person] a [person] righteous more than him.
Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
14 And you have made humankind like [the] fish of the sea like creeping thing[s] [which] not a ruler [is] over it.
Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
15 All of it with a fish hook he brings up he drags away it in net his and he gathers it in fishing net his there-fore he rejoices and he may be glad.
Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
16 There-fore he sacrifices to net his so he may make smoke to fishing net his for by them [is] fat portion his and food his [is] fat.
Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
17 ¿ There-fore will he empty net his and continually to kill nations not will he spare?
Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?

< Habakkuk 1 >