< Acts 7 >

1 And the High-priest said—Are these things, so?
Sai babban firist ya ce, ''Wadannan al'amura gaskiya ne?''
2 And, he, said—Brethren and fathers, hearken! The God of Glory, appeared unto our father Abraham, while he was in Mesopotamia, before he dwelt in Haran, —
Sai Istifanus ya amsa ya ce, ''Ya 'yan'uwa da ubanni, ku saurare ni, Allah Madaukaki ya bayyana ga ubanmu Ibrahim tun yana can kasar Mesofotamiya, kafin ma ya zauna a kasar Haran;
3 And said unto him—Get thee forth, out of thy land, and from among thy kindred, and come unto the land which, unto thee, I will point out.
ya ce masa, 'Ka bar kasarka da danginka, ka tafi kasar da zan nuna maka.'
4 Then, coming forth out of the land of the Chaldeans, he dwelt in Haran; and, from thence, when his father was dead, he removed him into this land, in which, ye, now dwell;
Sa'annan ya bar kasar Kaldiyawa ya zo ya zauna a Haran; daga can, bayan rasuwar mahaifinsa, sai Allah ya kira shi zuwa wannan kasa da kuke ciki.
5 And gave him no inheritance therein, not even a place to set his foot on; and yet promised to give it unto him in possession, and unto his seed after him, when as yet he had not a child.
Amma Allah bai ba shi kasar gado ba tukuna, ko da misalin tafin sawunsa. Amma ya alkawarta - ko da yake bai riga ya haifi da ba tukuna - wanda zai ba shi kasar gado, shi da zuriyarsa, a bayansa.
6 But God, spake thus—His seed shall be a sojourner in a foreign land, and they will bring it into bondage, and ill-treat it four-hundred years;
Allah ya yi magana da shi kamar haka, cewa zuriyarsa za su yi bakonci a wata kasa wadda ba tasu ba, mutanen wannan kasar kuwa za su gwada masu bakar azaba su kuma bautar da su har shekaru dari hudu.
7 And, the nation unto which they shall be in bondage, will, I, judge—said God; and, after these things, shall they come forth, and render divine service unto me, in this place.
'Kuma zan hukunta wannan al'umma da ta bautar da su,' Allah ya ce, 'Bayan haka za su fito daga wannan kasa su bauta mini a wannan wuri.'
8 And he gave unto him a covenant of circumcision; and, thus, he begat Isaac, and circumcised him on the eighth day, and Isaac, Jacob, and Jacob, the twelve patriarchs.
Allah ya ba Ibrahim alkawarin kaciya, sai Ibrahim ya haifi Ishaku ya yi masa kaciya a rana ta takwas; Ishaku ya haifi Yakubu, Yakubu kuma ya haifi ubanni Isra'ila su goma sha biyu.
9 And, the patriarchs, being jealous of Joseph, gave him up into Egypt; and, God, was, with him,
Wadannan 'yan'uwa suka yi kyashin danuwansu Yusifu suka sayar da shi bauta zuwa Masar. Amma Allah na tare da shi.
10 And rescued him out of all his tribulations, and gave him favour and wisdom before Pharaoh king of Egypt; and he appointed him governor over Egypt and all his house.
Ya kuwa cece shi daga dukan sharin da yan uwansa suka kulla masa, Allah kuwa ya ba shi tagomashi da hikima a gaban Fir'auna, sarkin Masar. Fir'auna kuwa ya mai da shi mai mulki a dukan kasar Masar da kuma dukan mallakarsa.
11 And there came a famine upon all Egypt and Canaan, and great tribulation, and our fathers could not find pasture.
Sai aka yi babbar yunwa a dukan kasar Masar da ta Kan'ana, iyayenmu suka sha wuya saboda rashin abinci.
12 But Jacob, hearing there was corn in Egypt, sent off our fathers, first;
Amma lokacin da Yakubu ya ji akwai hatsi a kasar Masar, sai ya aiki ubannimu a karo na farko.
13 And, the second time, Joseph was made known unto his brethren, and, the race of Joseph was made, manifest, unto Pharaoh.
Da suka je a karo na biyu, sai Yusifu ya bayyana kansa ga yanuwansa; a wannan lokaci ne Fir'auna ya gane da yanuwan Yusufu.
14 And Joseph, sending forth, called for Jacob his father, and all the kindred, consisting of seventy-five souls;
Yusufu ya aiki yanuwansa su kawo Yakubu ubansu da dukan mallakarsu da iyalansu zuwa Masar, Dukansu mutane saba'in da biyar ne.
15 And Jacob went down [into Egypt]. And he died, he, and our fathers;
Yakubu ya tafi ya zauna a Masar; shi da zuriyarsa har mutuwar su.
16 And were brought over into Shechem, and laid in the tomb which Abraham had purchased, for a price of silver, of the sons of Hamor in Shechem.
Aka dauke su zuwa Shekem aka binne su a kabarin da Ibrahim ya saya da kudin azurfa daga hannun yayan Hamor a Shekem.
17 Now, just as the time of the promise was drawing near wherewith God had agreed with Abraham, the people grew, and were multiplied in Egypt, —
Yayin da alkawarin Allah ya kusato wanda Allah ya fada wa Ibrahim, mutanen suka karu suka hayayyafa kwarai a Masar,
18 Until there arose another sort of king over Egypt, who had not known Joseph.
Sai a ka yi wani sarki a Masar wanda bai san Yusifu ba,
19 The same, dealing craftily with our race, ill-treated our fathers, so as to cause their babes to be exposed, to the end they might not be suffered to live.
Wannan sarki ya yaudari kakkaninmu ya yi masu mugunta kwarai da gaske, har ma ya kai ga suna barin jariransu cikin hasari don su ceci rayukansu.
20 In which season, Moses, was born, and was exceeding goodly, —who was nourished up three months in the house of his father;
A wannan lokaci ne aka haifi Musa, kuma kyakkyawan yaro ne sai aka yi renon sa tsawon wata uku a gidan mahaifinsa a asirce.
21 But, when he was exposed, the daughter of Pharaoh rescued him, and nourished him for herself, as a son.
Yayin da aka jefar da shi, sai diyar Fir'auna ta dauke shi ta rene shi kamar danta.
22 And, so Moses was trained in all the wisdom of the Egyptians, and was mighty in his words and works.
Aka ilimantar da Musa da dukan ilimi irin na Masar; kuma ya shahara cikin fasahar magana da kuma ayyukansa.
23 And, when there was being fulfilled unto him a period of forty years, it came up on his heart to look after his brethren the sons of Israel;
Amma lokacin da yakai shekara arba'in, sai ya yi niyyar ya ziyarci 'yan'uwansa, Isra'ilawa.
24 And, seeing one being wronged, he defended him, and avenged him that was getting worn out, smiting the Egyptian.
Sai ya ga wani na cin zalin Ba Isra'ile, Musa kuwa ya taimaki wanda ake kwara ta wurin murkushe Bamasaren:
25 But he supposed his brethren would understand that, God, through his hand, would give them deliverance; whereas they understood not.
zaton Musa 'yan'uwansa za su fahimci taimakon Allah ne ya zo masu amma ina! Basu gane ba.
26 On the following day also, he appeared unto them, as they were contending, and would have reconciled them in peace, saying—Men! ye are, brothers! Wherefore wrong ye one another?
Washegari ya ga wasu Isra'ilawa na fada da junansu; ya yi kokari ya raba su; sai ya ce masu, 'Malamai, ku 'yan'uwan juna ne; don me kuke fada da junanku?'
27 But, he that was wronging his neighbour, thrust him away, saying—Who hath appointed, thee, to be ruler and judge over us?
Amma shi wanda ake kwarar makwabcinsa ya ture Musa a gefe guda, ya ce, 'Wa ya nada ka shugaba ko alkali akanmu?
28 Art, thou, wishing, to kill me, in the same way thou didst kill, yesterday, the Egyptian?
Kana so ka kashe ni ne, kamar yadda ka kashe Bamasaren nan jiya?'
29 And Moses fled at this saying, and became a sojourner in the land of Midian, where he begat two sons.
Da jin haka sai Musa ya gudu, zuwa kasar Midinawa, a matsayin dan gudun hijira. Anan ya haifi ''ya'ya biyu maza.
30 And, when forty years were fulfilled, there appeared unto him, in the desert of Mount Sinai, a messenger, in a flame of fire, in a bush.
Bayan da shekaru arba'in suka wuce, sai mala'ika ya bayyana gare shi a jeji, kusa da dutsen Sinai, a cikin harshen wuta a cikin jeji.
31 And, Moses, seeing it, marvelled at the sight; and, as he was going near to observe, there came a voice of the Lord—
Sa'adda Musa ya ga wutar, mamaki ya kama shi; sai ya maso kusa don ya kara dubawa, sai ya ji muryar Ubangiji na cewa,
32 I, am the God of thy fathers, The God of Abraham and Isaac and Jacob. And Moses becoming, terrified, durst not observe.
'Nine Allah na ubanninka, Ibrahim, da na Ishaku, da na Yakubu.' Musa ya razana har ma bai sake daga kai ya duba ba.
33 And the Lord said unto him—Loose the sandals of thy feet; for, the place whereon thou art standing, is, hallowed ground.
Ubangiji ya ce masa, 'Tube takalminka, domin in da kake tsaye wuri mai tsarki ne.
34 I have, indeed seen, the ill-treatment of my people that is in Egypt, and, unto their groaning, have I hearkened, and have come down to rescue them. Now, therefore, come! I will send thee into Egypt.
Ba shakka na ga wahalar da mutane na ke sha a Masar, kuma na ji nishinsu, don haka na zo in cece su, yanzu fa sai ka zo, in aike ka zuwa Masar.'
35 The same Moses whom they had refused, saying—Who hath appointed thee to be ruler and judge? the same, both as ruler and redeemer, did God send, by the hand of the messenger who had appeared unto him in the bush:
Wannan fa shine Musan da suka ki, harma da cewa, 'Wanene ya nada ka alkali ko shugaba a kanmu?' Shine kuma wanda Allah ya aiko masu a matsayin shugaba da kuma mai ceto. Allah ya aiko shi ta hannun mala'ikan da ya gani a daji.
36 The same, led them forth, doing wonders and signs in Egypt, and in the Red Sea, and in the desert, forty years:
Bayan alamu da al'ajibai iri-iri a Masar da kuma Baharmaliya, Musa ya fito da su daga Masar da kuma cikin jeji, a lokacin da suka yi tafiya shekara arbain.
37 The same, is the Moses that said unto the sons of Israel—A prophet, unto you, will God raise up, from among your brethren, like unto me:
Wannan shine Musan da ya cewa Isra'ilawa, 'Ubangiji zai tayar maku da wani annabi kamar ni daga cikin Yan'uwan ku.'
38 The same, is he that came to be in the assembly in the desert, with the messenger who was speaking with him in Mount Sinai, and with our fathers, he who welcomed living utterances, to give unto us:
Wannan shine mutumin da ke tare da mutane a jeji. Karkashin jagorancin mala'ikan da ya yi magana da shi a dutsen Sinai. Wannan ne mutumin da ke tare da ubannen mu, wannan shi ne mutumin da ya ba mu maganar Allah mai rai.
39 Unto whom, our fathers would not become obedient, but thrust him away, and turned in their hearts unto Egypt,
Wannan shine mutumin da ubannenmu suka ki su yi masa biyayya; su ka fitar da shi daga cikinsu, suka kudurta a zuciyarsu za su koma masar.
40 Saying unto Aaron—Make as gods who shall go before us; for, as for this Moses who brought us forth out of Egypt, we know not what hath befallen him!
A lokacin ne suka cewa Haruna, 'ya yi masu allolin da za su jagorance su zuwa masar. Domin kuwa ga zancen Musan nan da ya fito da mu daga Masar, ba mu san abin da ya faru da shi ba.'
41 And so they fell to calf-making in those days, and offered sacrifice unto the idol, and rejoiced in the works of their hands.
Sai suka kera dan maraki suka kawo wa gunkin hadaya, suka yi murna da abin da hannayensu suka kera.
42 But God, turned, and delivered them up to be doing divine service unto the host of heaven, —just as it is written in a book of the prophets—Victims and sacrifices did ye offer unto me, forty years in the desert, O house of Israel?
Allah ya bashe su su bauta wa tauraran sama, kamar yadda yake a rubuce cikin littattafafan annabawa, 'Kun mika mani hadayu na yankakkun dabbobi a jeji ne a shekaru arba'in din nan ya ku Isra'ilawa?'
43 Nay! but ye took with you the tent of Moloch, and the star of the god Rephan, —the forms which ye made to bow down unto them: therefore will I carry you away beyond Babylon.
Kun yarda da haikalin Molek da kuma tauraron allahn nan Rafem, da kuma siffofin nan da kuka kera don ku yi masu sujada; don haka zan kai ku bauta har gaba da Babila.'
44 The tent of witness, was with our fathers in the desert, according as he who was speaking unto Moses, gave instructions, to make it, according to the model which he had seen.
Kakkaninmu suna da alfarwa ta sujada domin shaida a cikin jeji, kamar yadda Allah ya umarta yayin da ya yi magana da Musa, cewa ya yi shi bisa ga salon da aka nuna mashi.
45 Which our fathers succeeding to, also brought in, with Joshua, when taking possession of the nations, which God put out from before our fathers until the days of David;
Wannan shine Alfarwar da kakkaninmu suka zo da shi, a lokacin Joshuwa. Wannan ya faru ne yayin da suka mallaki wannan kasa ta al'ummai da Allah ya kora a gaban kakkaninmu. Haka abin yake har ya zuwa zamanin Dauda,
46 Who found favour before God, and asked to find a habitation for the God of Jacob.
wanda ya sami tagomashi a wurin Allah; don ya gina masujada domin Allah na Yakubu.
47 But, Solomon, built him a house.
Amma Sulaimanu ne ya gina Gidan Allah.
48 Although indeed, the Most High, not in hand-made places, dwelleth; just as, the prophet, saith—
Sai dai Madaukaki ba yakan zauna a gidan da hannaye suka gina ba, kamar yadda annabin ya ce,
49 Heaven is my thrown, and, the earth, is my footstool: What manner of house, will ye build me, saith the Lord, —Or what shall be the place of my resting?
'Sama kursiyina ce, duniya kuwa wurin ajjiye sawayena ne. To wane irin gida za ku gina mani? inji Ubangiji: ko kuwa ina ne wurin da zan huta?
50 Hath not, my hand, made all these things?
Ko ba hannayena ne suka yi dukan wadannan ba?'
51 Ye stiff-necked and uncircumcised in hearts and in ears, ye, always, against the Holy Spirit, do strive! As your fathers, ye also:
Ku mutane masu taurin kai masu zuciya mara kaciya da kunnuwa marasa ji, kullum kuna gaba da Ruhu Mai Tsarki, kuna aikata abin da kakkaninku suka aikata.
52 Which of the prophets, did not your fathers persecute? Yea they slew them who declared beforehand concerning the coming of the Righteous One—of whom, now, ye, have become, betrayers and murderers!
Wane annabi ne kakkaninku ba su tsanantawa ba? Sun kashe annabawan da suka rigayi zuwan Mai Adalcin nan, kuma kun zama wadanda suka kasance masu bashe shi da masu kashe shi,
53 Who, indeed, received the law through ranks of messengers, —and guarded it not.
kune mutanen da kuka karbi shari'a wadda mala'iku suka bayar, amma ba ku kiyaye ta ba”.
54 And, while they were hearing these things, they were being pierced in their hearts, and began gnashing their teeth against him.
Yayin da majalisar suka ji wannan, sai ransu ya baci kwarai, har suna cizon hakoransu don gaba da Istifanus.
55 But he, being already full of Holy Spirit, looking steadfastly into heaven, saw the glory of God, and Jesus standing on the right hand of God;
Amma shi, cike da Ruhu Mai Tsarki, sai ya daga idonsa sama, ya ga daukakar Allah; ya kuma hango Yesu na tsaye a hannun daman Allah.
56 And said—Lo! I see the heavens opened, and the Son of Man, standing, on the right hand of God.
Istifanus ya ce, “Duba, ina ganin sama ta bude, ga Dan Mutum na tsaye a hannun dama na Allah.”
57 And, crying out with a loud voice, they held their ears, and rushed with one accord upon him;
Amma yan majalisar suka daga murya da karfi, suka yi ihu, suka kuma toshe kunnuwansu, gaba dayansu suka afka masa;
58 And, thrusting him forth outside the city, proceeded to stone him. And, the witnesses, laid their garments at the feet of a young man named Saul.
suka fitar da shi bayan gari, suka jejjefe shi da duwatsu, don shaida sai suka tube manyan rigunansu suka ajiye a gaban wani matashi da ake ce da shi Shawulu.
59 And they stoned Stephen, as he was invoking and saying—Lord Jesus! give welcome unto my spirit.
Lokacin da suke kan jifan Istifanus, ya dinga kira yana cewa, ''Ya Ubangiji Yesu, ka karbi ruhu na.”
60 And, kneeling down, he cried out with a loud voice—Lord! do not charge against them, this sin. And, having said this, he fell asleep.
Ya durkusa ya daga murya da karfi, ya ce, “Ya Ubangiji, kada ka rike wannan zunubi a kansu.” Yayin da ya fadi wannan, sai ya yi barci.

< Acts 7 >