< Romans 1 >

1 Paul, a servant of Jesus Christ, a called apostle, separated unto the glad-message of God—
Bulus, bawan Yesu Almasihu, kirayayye ya zama manzo, kuma kebabbe domin bisharar Allah.
2 Which he promised beforehand, through his prophets, in holy scriptures—
Wannan itace bisharar da ya alkawarta tuntuni ta wurin annabawansa ta wurin tsarkakakkun littattafan sa.
3 Concerning his Son, —who came to be of the seed of David, according to flesh,
Game da Dansa ne, haifaffe daga zuriyar Dauda ga zancen jiki.
4 Who was distinguished as the Son of God—by power, according to a Holy Spirit, through means of a resurrection of the dead, —Jesus Christ our Lord;
Ta wurin tashinsa daga mattatu aka aiyana shi ya zama Dan Allah ta wurin ikon Ruhu na tsarkakewa. Yesu Almasihu Ubangijimu.
5 Through whom we have received favour and apostleship, for obedience of faith among all the nations, in behalf of his name,
Ta wurinsa muka karbi alheri da manzanci sabo da biyayyar imani a cikin dukkan al'ummai, domin darajar sunansa.
6 Among whom are, ye also, called of Jesus Christ:
cikin wadannan al'ummai kwa, ku ma an kiraku ku zama na Yesu Almasihu.
7 Unto all that are in Rome, beloved of God, called saints, favour unto you, and peace, from God our Father and Lord Jesus Christ.
Wannan wasika ga dukkanku ne da kuke cikin Roma, kaunatattu na Allah, kirayayyun mutane tsarkakakku. Bari alheri ya kasance tare daku, da salama daga Allah Ubanmu, da kuma Ubangiji Yesu Almasihu.
8 First, indeed, I give thanks unto my God, through Jesus Christ, concerning you all, because your faith is being announced throughout the whole world.
Abu na farko dai ina yi wa Allah na godiya ta wurin Yesu Almasihu domin ku duka, domin kuwa ana labarta bangaskiyarku ko ina a cikin dukkan duniya.
9 For God is, my witness, —unto whom I am rendering divine service in my spirit, in the glad message of his Son, —how incessantly, I am making mention of you
Domin kuwa Allah shi ne shaida ta, wanda nake bautawa a cikin ruhuna a cikin bisharar Dansa, yadda a koyaushe na ke ambaton ku.
10 At all times in my prayers, —making supplication—if, by some means, even now, at any time, I may have a way opened, in the will of God, to come unto you;
A kullum ina roko cikin addu'o'ina domin ta kowanne hali in yi nasarar zuwa gare ku da izinin Allah.
11 For I am longing to see you, that I may impart some spiritual gift unto you, to the end ye may be established, —
Gama ina marmarin ganin ku, domin in baku wata baiwa ta ruhaniya, domin in karfafa ku.
12 That is to say—there may be a mutual encouragement among you, each by the other’s faith, both yours and mine.
Wato ina dokin in sami cikakkiyar karfafawa a cikin ku, ta wurin bangaskiyar junanmu, wato tawa da taku.
13 I do not wish however that ye should be ignorant, brethren, that, many times, have I purposed to come unto you, but have been hindered, until the present, —in order that, some fruit, I might have among you also, even as among the other nations,
Yanzu fa bana so ku rasa sani, yan'uwa, sau da yawa nake yin niyyar zuwa wurinku, amma har yanzu hakan din bata samu ba. Na so yin hakan din ne don in sami 'ya'ya na ruhu a cikinku kamar dai yadda ya ke a sauran Al'ummai.
14 Both to Greeks and to Barbarians, both to wise and to unwise, a debtor, I am:
Ina dauke da nawayar Hellinawa da ta sauran jama'a, masu hikima da marasa hikima.
15 Thus, the eagerness on my part—unto you also who are in Rome, to announce the joyful message.
Don a shirye na ke in sanar da bishara a gare ku, ku da kuke cikin Roma.
16 For I am not ashamed of the joyful message; for it is God’s power unto salvation, to every one that believeth, both to Jew [first] and to Greek;
Don kuwa ni ba na jin kunyar yin bishara, don ita ce ikon Allah don samun ceto ga duk wanda ya gaskata, da farko dai Yahudawa kana kuma Hellinawa,
17 For, a righteousness of God, is therein revealed, —by faith unto faith: even as it is written—But, he that is righteous, by faith, shall live.
Domin a cikin ta adalcin Allah ya bayyana daga bangaskiy zuwa bangaskiya, kamar yadda yake a rubuce, “Mai adalci zai rayu ne tawurin bangaskiya.”
18 For there is being revealed an anger of God from heaven—against all ungodliness and unrighteousness of men who, the truth, in unrighteousness, do hold down; —
Domin fushin Allah ya bayyana ne daga sama gaba da rashin ibada da rashin adalci na yan'adam, wadanda suke danne gaskiya ta wurin rashin adalcin su.
19 Inasmuch as, what may be known of God, is manifest among them, for, God, unto them, hath made it manifest, —
Dalili kuwa abinda yakamata a sani game da Allah a bayyane ya ke a gare su. Domin kuwa Allah ya bayyana masu shi a zahiri.
20 For, the unseen things of him, from a world’s creation, by the things made, being perceived, are clearly seen, even his eternal power and divinity, —to the end they should be without excuse; (aïdios g126)
Domin al'amuransa da ba'a iya gani a bayyane suke tun halittar duniya. A na iya gane su ta wurin halitatattun abubuwa. Wadannan al'amura kuwa sune madawwamin ikonsa da Allahntakarsa. Sakamakon haka, wadannan mutane ba su da hujja. (aïdios g126)
21 Inasmuch as, having come to know God, not, as God, did they glorify him, or give him thanks, but were made fruitless in their reasonings, and darkened was their undiscerning heart,
Dalili kuwa, koda suna jin sun san Allah, amma basu darajanta shi a matsayin Allah ba, ko kuma su nuna masa godiya. Maimakon haka, suka zama wawaye a cikin tunaninsu, zukatansu marasa tunani sun duhunta.
22 Professing to be wise, they were made foolish,
Suna daukar kansu akan masu hikima ne su, amma sai ga su sun zama wawaye.
23 And, exchanged the glory of the incorruptible God, for the likeness of an image of a corruptible man, and of birds and fourfooted beasts and reptiles:
Sun musanya daukakar Allah madawwami da ta kamannin abubuwan da basa dawwama, kamar mutum, da tsuntsaye, da dabbobi masu kafafu hurhudu, da masu jan ciki.
24 Wherefore God gave them up in the covetings of their hearts unto impurity, so as to be dishonouring their bodies among them, —
Saboda haka Allah ya bashe su ga sha'awoyin kazantar zukatansu, su wulakantar da jukunansu a junansu.
25 Who, indeed, exchanged away the truth of God for the falsehood, and rendered worship and service unto the creature rather than unto the Creator, —who is blessed unto the ages. Amen! (aiōn g165)
Sune suka musanya gaskiyar Allah da karya, Kuma suke sujada da bauta ga halittaccen abu, maimakon Mahaliccin, Wanda yake abin yabo har abada. Amin. (aiōn g165)
26 For this cause, God gave them up unto dishonourable passions; for, even their females, exchanged away the natural use into that which is against nature, —
Saboda haka Allah ya bashe su, ga sha'awowin su na lalata da wulakanci, har matansu suka canza ka'idar jima'i da aka saba zuwa madigo mace da mace.
27 In like manner also, even the males, leaving the natural use of the female, flamed out in their eager desire one for another, males with males, the indecency, effecting, —and, the necessary recompence of their error, within themselves, duly receiving; —
Mazajensu ma suka sauya ka'idar jima'i tsakanin mace da miji zuwa namiji da namiji suna yin aikin lalata. Maza su na kwana da maza suna aikata aikin ban kyama, suna kuwa girbe sakamakon aiknsu na ban kyama.
28 And, even as they did not approve to be holding, God, in acknowledgment, God gave them up unto a disapproved mind to be doing the things that are not becoming,
Tunda shike ba su amince da Allah a cikkin al'amuransu ba, Allah ya bashe su ga bataccen hankalinsu, su aikata wadannan munanan abubuwa.
29 Filled with all unrighteousness, wickedness, greed, baseness, full of envy, murder, strife, deceit, evil disposition,
Suna cike da dukkan rashin adalci, mugunta, kyashi, keta, kuma cike da kishi, kisan kai, tarzoma, makirci, da kuma munanan manufafofi.
30 Whisperers, detractors, haters of God, insolent, arrogant, vain boasters, inventors of vices, unto parents unyielding,
Masu gulma da kage, makiyan Allah. Masu tada zaune tsaye, masu taurin kai, da ruba, masu kaga kowadanne miyagun abubuwa, kuma masu kin yin biyayya ga iyayensu.
31 Without discernment, regardless of covenants, without natural affection, unmerciful: —
Masu duhun zuciya; masu cin amana, marasa soyayya, da kuma rashin tausayi.
32 Who, indeed, having acknowledged the righteous sentence of God, —that, they who such things as these do practise, are worthy of death, not only, the same things, are doing, but are even delighting together with them who are practising [them].
Suna sane da tsarin Allah cewa masu yin irin wadannan al'amura sun cancanci hukuncin mutuwa. Ba kuwa yin wadannan abubuwan ka dai suke yi ba, harma goyon bayan masu yinsu suke yi.

< Romans 1 >