< Mark 1 >

1 The beginning of the gospel of Jesus Christ;
Wannan itace farkon bisharar Yesu Almasihu, Dan Allah.
2 as it is written in Isaiah the prophet: “Lo! I send my messenger before thy face, who shall prepare thy way;”
kamar yadda aka rubuta cikin littafin annabi Ishaya. Duba, ina aika manzona, a gabanka, wanda zai shirya maka hanya.
3 “The voice of one crying in the wilderness, Prepare the way of the Lord, make straight his paths!”
Akwai murya mai kira a jeji, tana cewa ka shirya hanyar Ubangiji. ka daidaita ta.
4 John the Baptizer appeared in the wilderness, preaching a baptism of repentance for the remission of sins.
Yahaya ya zo, yana baptisma acikin jeji yana wa'azin tuba, domin gafarar zunubai.
5 And there went out to him all the country of Judaea, and all they of Jerusalem and were baptized by him in the river Jordan, confessing their sins.
Dukan kasar Yahudiya da mutanen Urshalima suka zo wurin sa, a ka kuma yi masu baptisma a kogin urdun. suna furta zunubansu.
6 And John was clothed with camel's hair, and with a leathern girdle about his loins, and he ate locusts and wild honey.
Yahaya yana saye da tufa ta gashin rakumi, yana kuma da damara ta fata a kugunsa, abincinsa fara ce da zuma.
7 And he preached, saying, There cometh after me one mightier than I, the latchet of whose sandals I am not worthy to stoop down and loose.
Yana wa'azi, ya ce “akwai mai zuwa a bayana wanda ya ke da iko fiye da ni. wanda ko maballin takalminsa ban isa in kwance ba.
8 I have baptized you with water; but he will baptize you in the Holy Spirit.
Ni ina yi maku baptisma da ruwa, amma mai zuwa a bayana zai yi maku baptisma da Ruhu Mai Tsarki''.
9 And it came to pass that in those days Jesus came from Nazareth of Galilee, and was baptized by John in the Jordan.
Sai ya kasance a kwanakin nan Yesu ya zo daga Nazarat ta Galili, sai Yahaya ya yi masa baptisma a kogin urdun.
10 And immediately on coming up out of the water, he saw the heavens parted, and the Spirit descending as a dove upon him.
Sa'adda Yesu ya fito daga ruwan, sai sama ta bude, sai Ruhu ya sauko a bisansa da kamanin kurciya.
11 And there was a voice from the heavens, “Thou art my beloved Son; with thee I am well pleased.”
Sai wata murya ta zo daga sama, tana cewa, “Kai kaunataccen Dana ne. zuciyata ta na murna da kai kwarai''.
12 And immediately the Spirit driveth him forth into the wilderness.
Sai Ruhu ya iza shi zuwa jeji.
13 And he was in the wilderness forty days, tempted by Satan, and was with the wild beasts; and the angels ministered to him.
Yana a jeji kwana arba'in, Shaidan yana jarabtar sa. Yana cikin jeji da dabobi, sai malaiku su ka yi masa hidima.
14 But after John was put in prison, Jesus came into Galilee, preaching the glad tidings of God,
Bayan da aka kama Yahaya, Yesu ya shiga kasar Galili yana wa'azin bisharar Allah.
15 [[saying, ]] The time is fulfilled, and the kingdom of God is at hand; repent, and believe the glad tidings.
Yana cewa, “Lokaci ya yi, gama mulkin Allah ya kusato. Ku tuba ku bada gaskiya ga bishara”.
16 And as he was passing along by the lake of Galilee, he saw Simon and Andrew the brother of Simon dragging a net in the lake; for they were fishers.
Sa'adda ya ke wucewa a gefen takun Galili, sai ya ga Saminu da Andarawus, dan'uwansa suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
17 And Jesus said to them, Come after me, and I will cause you to become fishers of men.
Yesu ya ce masu ku zo, ku biyo ni, ni kuwa sai in maisheku masuntan mutane”.
18 And immediately they left their nets, and followed him.
Nan da nan suka bar tarun su, suka bi shi.
19 And going on a little farther, he saw James the son of Zebedee, and John his brother, who also were in the boat mending the nets;
Sa'adda Yesu ya yi tafiya kadan, sai ya ga Yakubu dan Zabadi da Yahaya dan'uwansa; suna gyaran tarunsu a jirgin ruwa.
20 and immediately he called them. And leaving their father Zebedee in the boat with the hired men, they went after him.
Sai ya kira su, su kuwa suka bar mahaifinsu Zabadi a jirgin ruwan da ma'aikatansu, sai su ka bi shi.
21 And they enter Capernaum; and immediately on the sabbath he was teaching in the synagogue.
Da su ka shigo cikin kafanahum, a ranar asabar, Yesu ya shiga majami'a ya koya masu.
22 And they were astonished at his teaching; for he taught them as having authority, and not as the scribes.
Su ka yi mamakin koyarwarsa, domin ya na koya masu da iko ba kamar marubuta ba.
23 And immediately there was in their synagogue a man with an unclean spirit, and he cried out,
A nan cikin majami'a akwai wani mutum mai kazamin ruhu, sai ya yi ihu da karfi.
24 saying, What have we to do with thee, Jesus of Nazareth? Thou hast come to destroy us; we know who thou art, the Holy One of God.
Yana cewa Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo ne domin ka halakar da mu? Na san wanene kai. Kai ne Mai Tsarki na Allah”.
25 And Jesus rebuked him, [[saying, ]] Be silent, and come out of him.
Sai Yesu ya tsauta wa kazamin ruhun ya ce, “Ka yi shiru ka fita daga cikinsa”.
26 And the unclean spirit convulsing him, and crying out with a loud voice, came out of him.
Bayan da kazamin ruhun ya buga shi kasa, sai kazamin ruhun ya yi ihu sa'annan ya fita daga jikinsa.
27 And they were all amazed, so that they questioned each other, saying, What is this? New teaching with authority; even the unclean spirits doth he command, and they obey him!
Sai dukan mutanen su ka yi mamaki kwarai, suna tambayar junansu menene wannan? wace sabuwar koyarwa ce da iko haka? har yana umartar kazaman ruhohi suna kuwa yi masa biyayya!”
28 And immediately his fame spread abroad everywhere through the whole surrounding country of Galilee.
Nan da nan labarinsa ya bazu ko'ina a dukkan kewayen kasar Galili.
29 And having come out of the synagogue, they immediately entered the house of Simon and Andrew, with James and John.
Bayan da suka bar majami'a, sai su ka shiga gidan Saminu da Andarawus, suna kuma tare da Yakubu da Yahaya.
30 And Simon's wife's mother lay sick of a fever; and they immediately speak to him about her.
Surikar Saminu tana kwance ba lafiya tana fama da zazzabi. Sai suka gaya wa Yesu game da ita.
31 And he went to her, and took her by the hand, and raised her up; and the fever left her, and she waited on them.
Sai ya zo, ya kama hannunta, ya daga ta, sai zazzabin ya sake ta, ta fara yi masu hidima.
32 And in the evening, when the sun had set, they brought to him all that were sick, and those who were possessed by demons;
Da yamman nan, bayan da rana ta fadi, sai su ka kawo masa dukan marasa lafiya da masu fama da aljanu.
33 and the whole city was assembled at the door.
Dukan mutanen garin su ka taru a bakin kofa.
34 And he healed many that were sick with various diseases, and cast out many demons; and he suffered not the demons to speak, because they knew him.
ya warkar da masu ciwo da yawa da masu chututtuka iri-iri, ya kuma fitar da bakaken aljanu, amma bai yarda aljanun su yi magana ba domin sun san shi.
35 And rising early, long before day, he went out, and withdrew into a desert place, and there prayed.
Ya tashi da sassafe, tun da sauran dare, ya tafi wurin da ba kowa, a can ya yi add'ua.
36 And Simon and those with him went in search of him,
Saminu da wandanda suke tare da shi suka neme shi.
37 and found him. And they say to him, All people are in search of thee.
Suka sa me shi, sai su ka ce masa, “kowa yana nemanka”.
38 And he saith to them, Let us go elsewhere into the neighboring towns, that I may preach there also; for, for this I came forth.
Ya ce, bari mu tafi wani wuri, zuwa wadansu garuruwan da ke kewaye, Saboda in yi wa'azi a can kuma. Wannan shi yasa na zo nan''.
39 And he went, preaching in their synagogues throughout all Galilee, and casting out the demons.
Ya tafi dukan kasar Galili, yana wa'azi a majimi'un su yana kuma fitar da aljanu.
40 And there cometh a leper to him beseeching him, and kneeling down, saying to him, If thou wilt, thou canst cleanse me.
Wani kuturu ya zo wurinsa. Yana rokonsa, ya durkusa. Ya ce masa, “in ka yarda kana iya warkar da ni.
41 And Jesus, moved with compassion, put forth his hand, and touched him, and saith, I will; be thou cleansed.
Sai ya yi juyayi, Yesu ya mi ka hannun sa ya ta ba shi ya na ce masa “Na yarda. Ka sarkaka”.
42 And immediately the leprosy left him, and he was cleansed.
Nan da nan kuturtar ta barshi, ya kuma sa mu tsarkakewa.
43 And sternly charging him, he immediately sent him away,
Yesu ya yi masa gargadi sosai, ya salame shi.
44 saying to him, See that thou say nothing to any one; but go, show thyself to the priest, and offer for thy cleansing what Moses commanded, for a testimony to them.
Ya ce masa “ka tabbata fa kada ka gayawa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, sai ka je ka yi hadaya domin tsarkakewa kamar yadda Musa ya umurta, domin shaida.
45 But he went away, and began to publish it constantly, and to spread the matter abroad, so that Jesus could no more enter a city openly, but was without in desert places; and they came to him from every quarter.
Amma da ya fita sai ya fara gaya wa kowa, ya baza maganar a ko'ina, har Yesu bai iya tafiya a sake a garin ba. Ya tafi ya tsaya a wuraren da ba kowa, mutane kuwa su ka zo wurinsa daga ko'ina.

< Mark 1 >