< Luke 1 >

1 Inasmuch as many have undertaken to arrange a narrative of those things which are fully believed among us,
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 even as they were delivered to us by those who were eye-witnesses from the beginning and became ministers of the word,
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 it seemed good to me also, having accurately traced up all things from the first, to write to thee a connected account, most excellent Theophilus,
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 that thou mightst know the exact truth with regard to those things in which thou wast instructed.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 There was in the days of Herod, king of Judaea, a certain priest named Zachariah, of the course of Abijah; and he had a wife of the daughters of Aaron, and her name was Elizabeth.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 And they were both righteous in the sight of God, walking in all the commandments and ordinances of the Lord blameless.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 And they had no child, because Elizabeth was barren, and they were both far advanced in years.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 And it came to pass, that, while he was serving as priest before God in the order of his course,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 according to the custom of the priesthood the lot fell to him to go into the temple of the Lord and burn the incense.
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 And the whole multitude of the people was praying without at the time of the incense.
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 And there appeared to him an angel of the Lord, standing on the right of the altar of incense.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 And Zachariah was troubled at the sight, and fear fell upon him.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 But the angel said to him, Fear not, Zachariah; for thy prayer was heard, and thy wife Elizabeth shall bear thee a son; and thou shalt call his name John.
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 And thou wilt have joy and gladness, and many will rejoice for his birth.
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 For he will be great in the sight of the Lord; and will drink neither wine nor strong drink; and he will be filled with the Holy Spirit from his very birth.
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 And many of the sons of Israel will he turn to the Lord their God.
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 And he will go before his face in the spirit and power of Elijah, to turn the hearts of fathers to children, and the disobedient to the wisdom of the righteous, to make ready for the Lord a prepared people.
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 And Zachariah said to the angel, Whereby shall I know this? for I am an old man, and my wife is far advanced in years.
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 And the angel answering said to him, I am Gabriel, who stand in the presence of God; and I was sent to speak to thee, and to tell thee these glad tidings.
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 And lo! thou shalt be silent, and not able to speak, until the day when these things shall come to pass, because thou didst not believe my words, which will be fulfilled in their season.
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 And the people were looking for Zachariah, and wondering that he remained so long in the temple.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 And on coming out, he was not able to speak to them; and they perceived that he had seen a vision in the temple; and he was beckoning to them, and remained speechless.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 And it came to pass, when the days of his ministration were completed, that he returned to his house.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 And after those days his wife Elizabeth conceived, and hid herself five months, saying,
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 Thus hath the Lord dealt with me in the days wherein he looked on me to take away my reproach among men.
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 And in her sixth month the angel Gabriel was sent from God to a city of Galilee, called Nazareth,
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 to a virgin betrothed to a man whose name was Joseph, of the house of David; and the virgin's name was Mary.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 And the angel came in to her and said, Hail, thou that art highly favored! the Lord is with thee.
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 And she was troubled at the words, and was considering what this salutation could mean.
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 And the angel said to her, Fear not, Mary; for thou hast found favor with God.
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 And lo! thou shalt conceive in thy womb, and hear a son, and shalt call his name Jesus.
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 He shall be great, and shall be called the Son of the Most High; and the Lord God will give to him the throne of David his father;
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 and he shall reign over the house of Jacob for ever; and of his kingdom there shall be no end. (aiōn g165)
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn g165)
34 Then said Mary to the angel, How shall this be, since I know not a man?
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 And the angel answering said to her, The Holy Spirit will come upon thee, and the power of the Most High will overshadow thee; wherefore the holy one that is to be born will be called the Son of God.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 And lo! Elizabeth, thy kinswoman, she also hath conceived a son in her old age; and this is the sixth month with her who is called barren.
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 For nothing will be impossible with God.
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 And Mary said, Lo, the handmaid of the Lord! May it be to me according to thy word. And the angel departed from her.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 And Mary arose and went in those days into the hill-country with haste, into a city of Judah.
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 And she entered the house of Zachariah, and saluted Elizabeth.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 And it came to pass, when Elizabeth heard the salutation of Mary, that the babe leaped in her womb; and Elizabeth was filled with the Holy Spirit,
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 and cried out with a loud voice, and said, Blessed art thou among women; and blessed is the fruit of thy womb!
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 And whence is this to me, that the mother of my Lord should come to me?
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 For lo! as soon as the voice of thy salutation came to my ears, the babe leaped in my womb in exultation.
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 And blessed is she who hath believed that there will be an accomplishment of those things which were told her from the Lord.
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 And Mary said, My soul magnifieth the Lord,
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 and my spirit hath exulted in God my Saviour;
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 for he hath looked upon the low estate of his handmaiden. For lo! from this time all generations will call me blessed;
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 for the Mighty One hath done great things for me; and holy is his name;
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 and his mercy is from generation to generation on them that fear him.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 He hath wrought mightily with his arm; he hath scattered the proud in the device of their heart.
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 He hath cast down princes from thrones, and exalted men of low degree.
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 The hungry he hath filled with good things, and the rich he hath sent away empty.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 He hath given help to Israel his servant, in remembrance of his mercy
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 toward Abraham and his offspring for ever, as he spoke to our fathers. (aiōn g165)
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn g165)
56 And Mary abode with her about three months, and returned to her own house.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 Now Elizabeth's full time came that she should be delivered; and she brought forth a son.
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 And her neighbors and her kinsfolk heard that the Lord had showed great mercy toward her; and they rejoiced with her.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 And it came to pass that on the eighth day they came to circumcise the child; and they were about to call him Zachariah, after the name of his father.
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 And his mother answering said, Not so; but he shall be called John.
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 And they said to her, There is no one of thy kindred that is called by this name.
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 And they made signs to his father, how he would have him named.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 And he asked for a writing-tablet, and wrote, saying, His name is John. And they all marveled.
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 And his mouth was opened immediately, and his tongue was loosed; and he spoke, blessing God.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 And fear came on all that dwelt around them; and all these things were talked of throughout the whole of the hill-country of Judaea.
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 And all that heard them laid them up in their hearts, saying, What then will this child be? For the hand of the Lord was with him.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 And Zachariah his father was filled with the Holy Spirit, and prophesied, saying,
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 Blessed be the Lord, the God of Israel! for he hath visited and redeemed his people,
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 and hath raised up a horn of salvation for us in the house of David his servant, —
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 as he spoke by the mouth of his holy prophets of old, (aiōn g165)
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn g165)
71 salvation from our enemies, and from the hand of all that hate us,
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 to accomplish his mercy toward our fathers, and to remember his holy covenant,
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the oath which he swore to Abraham our father,
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 to grant to us, that being delivered from the hand of our enemies, we might worship him without fear,
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 in holiness and righteousness before him, all our days.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 And thou, child, shalt be called a prophet of the Most High; for thou shalt go in advance before the face of the Lord to prepare his ways,
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 to give knowledge of salvation to his people in the remission of their sins
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 through the tender mercy of our God, whereby the day-spring from on high hath visited us,
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 to give light to those sitting in darkness and the shadow of death, to guide our feet into the way of peace.
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 And the child grew, and waxed strong in spirit; and was in the deserts till the day of his manifestation to Israel.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.

< Luke 1 >