< Hebrews 1 >

1 In many parts and many ways, God, having spoken long ago to the fathers by the prophets,
A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri,
2 in these last days speaks to us in [His] Son, whom He appointed heir of all things, through whom He also made the ages; (aiōn g165)
amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. (aiōn g165)
3 who being the brightness of the glory, and the impress of His subsistence, bearing up also all things by the saying of His might—having made a cleansing of our sins through Himself, sat down at the right hand of the Greatness in the highest,
Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama.
4 having become so much better than the messengers, as He inherited a more excellent name than them.
Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.
5 For to which of the messengers did He ever say, “You are My Son—today I have begotten You?” And again, “I will be to Him for a Father, and He will be to Me for a Son?”
Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa, “Kai Ɗana ne; yau na zama Uba a gare ka”? Ko kuwa, “Zan zama Ubansa, shi kuma zai zama Ɗana”?
6 And when again He may bring the firstborn into the world, He says, “And let them worship Him—all messengers of God”;
Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce, “Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”
7 and to the messengers, indeed, He says, “The [One] who is making His messengers spirits, and His ministers a flame of fire”;
Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce, “Ya mai da mala’ikunsa iska, bayinsa kuma harsunan wuta.”
8 but to the Son: “Your throne, O God, [is] throughout the age of the age; The scepter of righteousness [is the] scepter of Your kingdom; (aiōn g165)
Amma game da Ɗan ya ce, “Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin, adalci kuma zai zama sandan mulkinka. (aiōn g165)
9 You loved righteousness, and hated lawlessness; Because of this He anointed You—God, Your God—With oil of gladness above Your partners”;
Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta; saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka, ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”
10 and, “You, LORD, founded the earth at the beginning, And the heavens are a work of Your hands.
Ya kuma ce, “Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya, sammai kuma aikin hannuwanka ne.
11 These will perish, but You remain, And all will become old as a garment,
Su za su hallaka, amma kai kana nan; dukansu za su tsufa kamar riga.
12 And You will roll them together as a mantle, and they will be changed, But You are the same, and Your years will not fail.”
Za ka naɗe su kamar mayafi, kamar riga za su sauya. Amma kai ba za ka canja ba, shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”
13 And to which of the messengers did He ever say, “Sit at My right hand, Until I may make Your enemies Your footstool?”
Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa, “Zauna a hannun damana, sai na sa abokan gābanka su zama matashin sawunka”?
14 Are they not all spirits of service—being sent forth for ministry because of those about to inherit salvation?
Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?

< Hebrews 1 >