< Hebrews 2 >
1 Because of this it is more abundantly necessary to take heed to the things heard, lest we may drift away,
Dole mu ƙara mai da hankali sosai ga abubuwan da muka ji, don kada mu kauce.
2 for if the word being spoken through messengers became steadfast, and every transgression and disobedience received a just repayment,
Gama in saƙon da aka faɗi ta bakin mala’iku ya zama tabbatacce, kuma kowane ƙeta umarni da rashin biyayya suka karɓi sakamakonsu da ya dace,
3 how will we escape, having neglected such great salvation? Which having received [that] spoken through the LORD [from] the beginning, was confirmed to us by those having heard,
yaya za mu tsira in muka ƙyale irin wannan babban ceto? Wannan ceto, wanda Ubangiji ne ya fara sanar, aka kuma tabbatar mana ta bakin waɗanda suka ji shi.
4 God also bearing joint-witness both with signs and wonders, and manifold powers, and distributions of the Holy Spirit, according to His will.
Allah shi ma ya shaida ta wurin alamu, abubuwan banmamaki da mu’ujizai iri-iri, da kuma baye-bayen Ruhu Mai Tsarki da aka rarraba bisa ga nufinsa.
5 For He did not subject the coming world to messengers, concerning which we speak,
Ba ga mala’iku ba ne ya sa su yi mulkin duniya mai zuwa, wanda muke magana a kai ba.
6 and one in a certain place testified fully, saying, “What is man, that You are mindful of him, Or a son of man, that You look after him?
Amma akwai wani wurin da wani ya shaida cewa, “Mene ne mutum, da kake tuna da shi, ɗan mutum da kake kula da shi?
7 You made him [a] little less than messengers, You crowned him with glory and honor, And set him over the works of Your hands,
Ka sa shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku; ka naɗa shi da ɗaukaka da girma,
8 You put all things in subjection under his feet,” for in the subjecting to Him all things, He left nothing to Him unsubjected, but now we do not yet see all things subjected to Him,
ka kuma sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa.” Ta wurin sa kome a ƙarƙashinsa, Allah bai bar wani abu da bai sa a ƙarƙashinsa ba. Duk da haka a yanzu ba mu ga kowane abu a ƙarƙashinsa ba.
9 and we see Him who was made [a] little less than messengers—Jesus—because of the suffering of death, having been crowned with glory and honor, that by the grace of God He might taste of death for everyone.
Sai dai muna ganin Yesu, wanda aka mai da shi ƙasa kaɗan da darajar mala’iku, yanzu kuwa an naɗa shi da ɗaukaka da girma domin yă sha wahalar mutuwa, domin ta wurin alherin Allah yă ɗanɗana mutuwa saboda kowa.
10 For it was fitting to Him, because of whom [are] all things, and through whom [are] all things, bringing many sons to glory, to make the author of their salvation perfect through sufferings,
Ta wurin kawo’ya’ya masu yawa zuwa ga ɗaukaka, ya dace cewa Allah, wanda dominsa da kuma ta wurinsa ne kome yake kasancewa, ya sa tushen cetonsu yă zama cikakke ta wurin shan wahala.
11 for both He who is sanctifying and those sanctified [are] all of one, for which cause He is not ashamed to call them brothers,
Da shi wanda yake tsarkake mutane da kuma su waɗanda ake tsarkakewa duk’yan iyali ɗaya ne. Saboda haka Yesu ba ya kunyan kiransu’yan’uwansa.
12 saying, “I will declare Your Name to My brothers, In the midst of an assembly I will sing praise to You”; and again, “I will be trusting on Him”;
Ya ce, “Zan sanar da sunanka ga’yan’uwana; a gaban jama’a zan rera yabonka.”
13 and again, “Behold, I and the children that God gave to Me.”
Har wa yau ya ce, “Zan dogara gare shi.” Ya kuma ce, “Ga ni, da’ya’yan da Allah ya ba ni.”
14 Seeing, then, the children have partaken of flesh and blood, He Himself also took part of the same in like manner, that through death He might destroy him having the power of death—that is, the Devil—
Da yake’ya’yan suna da nama da jini, shi ma sai ya ɗauki kamanninsu na mutum domin ta wurin mutuwarsa yă hallaka wanda yake riƙe da ikon mutuwa, wato, Iblis
15 and might deliver those, whoever, with fear of death, throughout all their life, were subjects of bondage,
ya kuma’yantar da waɗanda dukan rayuwarsu tsoron mutuwa ya riƙe su cikin bauta.
16 for doubtless, He does not lay hold of messengers, but He lays hold of [the] seed of Abraham,
Gama tabbatacce ba mala’iku ne ya taimaka ba, sai dai zuriyar Ibrahim.
17 for this reason it seemed necessary to Him to be made like the brothers in all things, that He might become a kind and faithful Chief Priest in the things related to God, to make propitiation for the sins of the people,
Saboda wannan dole a mai da shi kamar’yan’uwansa ta kowace hanya, domin yă zama babban firist mai aminci da mai jinƙai cikin hidima ga Allah, yă kuma miƙa hadayar sulhu saboda zunuban mutane.
18 for in that He suffered, Himself being tempted, He is able to help those who are tempted.
Domin shi kansa ya sha wahala sa’ad da aka gwada shi, yana iya taimakon waɗanda ake yi wa gwaji.