< Joshua 1 >

1 And it came to pass after the death of Moses, the servant of the Lord, that the Lord spoke unto Joshua the son of Nun, the minister of Moses, saying,
Bayan mutuwar Musa bawan Ubangiji, sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa ɗan Nun, mataimakin Musa,
2 Moses my servant is dead; now therefore arise, pass over this Jordan, thou, and all this people, unto the land which I do give to them, to the children of Israel.
“Bawana Musa ya mutu. Yanzu sai ka tashi tare da mutanen nan duka, ku yi shirin ƙetare kogin Urdun zuwa cikin ƙasar da zan ba su Isra’ilawa.
3 Every place that the sole of your foot shall tread upon, that have I given unto you, as I said unto Moses.
Zan ba ku duk ƙasar da za ku taka, kamar yadda na yi wa Musa alkawari.
4 From the wilderness and this Lebanon even unto the great river, the river Euphrates, all the land of the Hittites, and unto the great sea toward the going down of the sun, shall be your boundary.
Ƙasar da ta kama daga hamada zuwa Lebanon, zuwa babban Kogin, wato, Kogin Yuferites, da dukan ƙasar Hittiyawa zuwa Bahar Rum, wajen yamma.
5 No man shall be able to stand up before thee all the days of thy life; as I was with Moses, so will I be with thee: I will not let thee fail, nor forsake thee.
Ba wanda zai yi tsayayya da kai dukan kwanakin ranka. Yadda na kasance tare da Musa, haka zan kasance tare da kai; ba zan taɓa rabuwa da kai ba; ba zan yashe ka ba.
6 Be strong and of a good courage; for thou shalt divide for an inheritance unto this people the land, which I swore unto their fathers to give to them.
“Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, gama kai za ka bi da mutanen nan har su karɓi ƙasar da na yi wa kakanninsu alkawari zan ba su.
7 Only be thou strong and very courageous, to observe to do according to all the law, which Moses my servant hath commanded thee: turn not from it to the right hand or to the left; in order that thou mayest prosper whithersoever thou goest.
Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro, ka yi lura fa, ka yi biyayya da dokokin da bawana Musa ya ba ka; kada ka kauce ga bin dokokin ko hagu ko dama, domin ka yi nasara a duk, inda za ka je.
8 This book of the law shall not depart out of thy mouth; but thou shalt meditate therein day and night, in order that thou mayest observe to do according to all that is written therein; for then shalt thou make thy way prosperous, and then shalt thou have good success.
Kada ka bar Littafin Dokokin nan yă rabu da bakinka, sai dai ka yi ta tunani game da shi dare da rana, don ka lura, ka yi duk abin da aka rubuta a ciki, ta haka ne za ka yi nasara cikin duk abin da za ka yi.
9 Behold, I have commanded thee, Be strong and of good courage; be not dismayed, neither be thou discouraged; for the Lord thy God is with thee whithersoever thou goest.
Ba ni na umarce ka ba? Ka yi ƙarfin hali ka kuma kasance da rashin tsoro. Kada ka ji tsoro; kada ka karaya, gama Ubangiji Allahnka zai kasance tare da kai duk inda za ka je.”
10 Then Joshua commanded the officers of the people, saying,
Saboda haka sai Yoshuwa ya umarci shugabannin mutane,
11 Pass through the midst of the camp, and command the people, saying, Prepare yourselves provisions; for after only three days more ye shall pass over this Jordan, to go in to possess the land, which the Lord your God giveth you, to possess it.
“Ku ratsa cikin sansani, ku gaya wa mutane, ‘Ku shirya guzurinku. Nan da kwana uku za ku ƙetare Urdun a nan, don ku je ka mallaki ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku ta zama taku.’”
12 And to the Reubenites, and to the Gadites, and to half the tribe of Menasseh, spoke Joshua, saying,
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Ruben, mutanen Gad da kuma rabin mutanen kabilar Manasse,
13 Remember the word which Moses the servant of the Lord commanded you, saying, The Lord your God hath granted you rest, and hath given you this land;
“Ku tuna da umarnin da Musa bawan Ubangiji ya yi muku. ‘Ubangiji Allahnku ya ba ku hutawa, ya kuma ba ku wannan ƙasa.’
14 Your wives, your little ones, and your cattle, shall remain in the land which Moses gave you on this side of the Jordan; but ye shall pass over armed before your brethren, all the mighty men of valor, and help them;
Matanku, da yaranku, da kuma dabbobinku za su kasance a ƙasar da Musa ya ba ku a gabashin Urdun, amma dole mayaƙanku, su yi shirin yaƙi su haye, su yi gaba tare da’yan’uwanku, za ku taimaki’yan’uwanku
15 Until the Lord shall have granted your brethren rest, as he hath done to you, and they also have taken possession of the land which the Lord your God giveth them: then shall ye return unto the land of your possession, and possess it, which Moses the servant of the Lord gave you on this side of the Jordan, toward the rising of the sun.
har sai lokacin da Ubangiji ya ba su hutawa, kamar yadda ya yi muku, kuma har sai su ma sun ƙwace ƙasar da Ubangiji Allahnku ya yi alkawari zai ba su. Bayan haka ne za ku koma ku mallaki ƙasarku, wadda Musa bawan Ubangiji ya ba ku a gabashin Urdun.”
16 And they answered Joshua, saying, All that thou hast commanded us will we do, and whithersoever thou wilt send us will we go.
Sai suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “Duk abin da ka ce mu yi, za mu yi. Duk inda kuma ka aike mu, za mu je.
17 Entirely so as we have hearkened unto Moses, thus will we hearken unto thee: only the Lord thy God be with thee, as he was with Moses.
Kamar yadda muka yi wa Musa biyayya, haka za mu yi maka biyayya. Ubangiji Allahnka ya kasance tare da Musa.
18 Every man that doth rebel against thy order, and will not hearken unto thy words in all that thou mayest command him, shall be put to death: only be strong and of a good courage.
Duk wanda ya yi wa maganarka tawaye, ya ƙi yă yi biyayya da maganarka, ko da umarnin da ka ba shi, za a kashe shi. Ka dai ƙarfafa ka kuma yi ƙarfi hali!”

< Joshua 1 >