< Deuteronomy 34 >

1 And Moses went up from the plains of Moab unto the mount of Nebo, to the top of Pisgah, that is before Jericho; and the Lord showed him all the land [from] Gil'ad unto Dan,
Sai Musa ya hau Dutsen Nebo daga filayen Mowab, zuwa ƙwanƙolin Fisga, wanda yake ƙetare Yeriko. A can Ubangiji ya nuna masa dukan ƙasar, daga Gileyad zuwa Dan,
2 And all Naphtali, and the land of Ephraim, and Menasseh, and all the land of Judah, unto the western sea.
da ta dukan Naftali, da yankin Efraim da na Manasse, dukan ƙasar Yahuda har zuwa Bahar Rum,
3 And the south, and the plain, the valley of Jericho, the city of palm-trees, unto Zoar.
da Negeb da dukan yankin Kwarin Yeriko, Birnin Dabino, har zuwa Zowar.
4 And the Lord said unto him, This is the land which I swore unto Abraham, unto Isaac, and unto Jacob, saying, Unto thy seed will I give it: I have let thee see it with thy eyes, but thither shalt thou not go over.
Sa’an nan Ubangiji ya ce masa, “Wannan ce ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa wa Ibrahim, Ishaku da Yaƙub, sa’ad da na ce, ‘Zan ba da ita ga zuriyarku.’ Na bar ka ka gani da idanunka, amma ba za ka haye zuwa cikinta ba.”
5 And Moses the servant of the Lord died there in the land of Moab, according to the order of the Lord.
Nan fa, a ƙasar Mowab Musa bawan Ubangiji ya mutu, yadda Ubangiji ya faɗa.
6 And he buried him in the valley in the land of Moab, opposite Beth-peor; but no man knoweth of his sepulchre unto this day.
Aka binne shi a Mowab, a kwarin kusa da Bet-Feyor, amma har wa yau babu wanda ya san inda kabarinsa yake.
7 And Moses was a hundred and twenty years old when he died; his eye was not dimmed, and his natural force had not abated.
Musa yana da shekara ɗari da ashirin sa’ad da ya mutu, duk da haka idanunsa ba su dushe ba, ƙarfinsa kuwa bai ragu ba.
8 And the children of Israel wept for Moses in the plains of Moab thirty days; and then were ended the days of weeping and mourning for Moses.
Isra’ilawa suka yi makoki domin Musa a filayen Mowab kwana talatin, sai da lokacin kuka, da na makoki suka ƙare.
9 And Joshua the son of Nun was full of the spirit of wisdom; for Moses had laid his hands upon him; and the children of Israel hearkened unto him, and did, as the Lord had commanded Moses.
To, Yoshuwa ɗan Nun ya cika da ruhun hikima, gama Musa ya ɗibiya hannuwansa a kansa. Saboda haka Isra’ilawa suka saurare shi, suka kuma aikata abin da Ubangiji ya umarci Musa.
10 And there arose not a prophet since then in Israel like unto Moses, whom the Lord knew face to face,
Tun daga nan ba a sāke yin wani annabi a Isra’ila kamar Musa ba, wanda Ubangiji ya san shi fuska da fuska,
11 In respect to all the signs and the wonders, which the Lord had sent him to do in the land of Egypt to Pharaoh, and to all his servants, and to all his land,
wanda kuma ya yi dukan waɗannan alamu banmamaki da al’ajaban da Ubangiji ya aike shi yă yi a Masar, da a kan Fir’auna, da a kan dukan shugabanninsa, da kuma a kan dukan ƙasarsa.
12 And in respect to all that mighty hand, and in all the great terrific deeds which Moses displayed before the eyes of all Israel.
Gama babu wani wanda ya taɓa nuna iko mai ƙarfi, ko yă aikata ayyukan banrazana waɗanda Musa ya yi a gaban dukan Isra’ila.

< Deuteronomy 34 >