< Haggai 1 >

1 In the second year of king Darius, in the sixth month, on the first day of the month, came the word of the Lord through means of Haggai the prophet unto Zerubbabel the son of Shealthiel, the governor of Judah, and to Joshua the son of Jehozadak, the high priest, saying,
A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
2 Thus hath said the Lord of hosts, saying, This people have said, The time is not yet come, the time for the Lord's house to be built.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
3 And the word of the Lord came by means of Haggai the prophet, saying,
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
4 Is it time for you, O ye, to dwell in your ceiled houses, while this house lieth in ruins?
“Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
5 Now therefore, thus hath said the Lord of hosts, Direct your heart unto your ways.
To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
6 Ye have sown much, and bring in little; ye eat, but it doth not satisfy hunger; ye drink, but it doth not appease thirst; ye clothe yourselves, but no one is warm; and he that earneth something earneth it for a bag with holes.
Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
7 Thus hath said the Lord of hosts, Direct your heart to your ways.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
8 Go up to the mountain, and bring wood, and build the house: that I may take pleasure in it, and be glorified, saith the Lord.
Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
9 [Till now] ye looked for much, and lo, it came to be little; and when ye brought it home, I blew upon it. For what cause? saith the Lord of hosts. Because of my house that lieth in ruins, while ye run every man unto his own house.
“Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
10 Therefore do the heavens for your sake withhold the dew, and the earth withholdeth her products.
Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
11 And I called for a drought over the land, and over the mountains, and over the corn, and over the new wine, and over the oil, and over what the ground bringeth forth, and over men, and over cattle, and over all the labor of the hands.
Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
12 Then hearkened Zerubbabel the son of Shealthiel, and Joshua the son of Jehozadak, the high priest, with all the remnant of the people, unto the voice of the Lord their God, and to the words of Haggai the prophet, as the Lord their God had sent him, and the people were afraid of the Lord.
Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
13 Then said Haggai the messenger of the Lord by the Lord's message unto the people saying, I am with you, saith the Lord.
Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
14 And the Lord stirred up the spirit of Zerubbabel the son of Shealthiel, the governor of Judah, and the spirit of Joshua the son of Jehozadak, the high priest, and the spirit of all the remnant of the people, and they came and did work on the house of the Lord of hosts, their God.
Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
15 On the four and twentieth day of the sixth month, in the second year of king Darius.
a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,

< Haggai 1 >