< Haggai 2 >

1 In the seventh [month], on the one and twentieth day of the month, came the word of the Lord by means of Haggai the prophet, saying,
a ranar ashirin da ɗaya ga watan bakwai, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
2 Do say to Zerubbabel the son of Shealthiel, the governor of Judah, and to Joshua the son of Jehozadak, the high priest, and to the residue of the people, saying,
“Ka yi magana da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel wanda yake gwamna a Yahuda, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma dukan raguwar mutane. Ka tambaye su ka ce,
3 Who is there yet left among you that hath seen this house in its first glory? and how do ye see it now? is it not in comparison with it as nothing in your eyes?
‘Wane ne a cikinku ya ragu da ya ga wannan gida a darajarsa ta dā? Yaya yake a gare ku a yanzu? Bai yi kamar a bakin kome ba, ko ba haka ba?
4 Yet now be strong, O Zerubbabel, saith the Lord, and be strong O Joshua, the son of Jehozadak, the high priest, and be strong, all ye people of the land, saith the Lord, and do; [for I am with you, saith the Lord of hosts, ]
Amma yanzu ka ƙarfafa, ya Zerubbabel,’ in ji Ubangiji. ‘Ka ƙarfafa, ya Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist. Ku ƙarfafa, dukanku mutanen ƙasar,’ in ji Ubangiji, ‘ku yi aiki. Gama ina tare da ku,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
5 [In accordance with] the word that I covenanted with you when ye came out of Egypt, so [will] my spirit remain among you: fear nought.
‘Wannan shi ne alkawarin da na yi da ku a lokacin da kuka fito daga Masar. Ruhuna kuwa yana tare da ku. Kada ku ji tsoro.’
6 For thus hath said the Lord of hosts, Yet one thing more [will I do], it is but little, when I will cause to quake the heavens, and the earth, and the sea, and the dry land;
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ba da jimawa ba zan sāke girgiza sammai da kuma ƙasa, teku da busasshiyar ƙasa.
7 And I will cause to quake all the nations, and the precious things of all the nations shall come [hither]: and I will fill this house with glory, saith the Lord of hosts.
Zan girgiza dukan al’ummai, marmarin kowace al’umma kuma zai taso, sa’an nan zan cika gidan nan da ɗaukaka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
8 Mine is the silver, and mine is the gold, saith the Lord of hosts.
‘Da zinariya da azurfa duka nawa ne,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 Greater shall be the glory of this latter house than that of the former, saith the Lord of hosts: and in this place will I give peace, saith the Lord of hosts.
‘Ɗaukakar gidan nan na yanzu za tă fi ɗaukakar gidan nan na dā,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki. ‘A wannan wuri kuma zan ba da salama,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
10 On the four and twentieth day of the ninth month, in the second year of Darius, came the word of the Lord by means of Haggai the prophet, saying,
A ranar ashirin da huɗu ga watan tara, a shekara ta biyu ta mulkin Dariyus, maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai cewa,
11 Thus hath said the Lord of hosts, Do ask the priests concerning the law, saying,
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘Ku tambayi firist abin da doka ta ce.
12 Lo! if one should carry holy flesh in the corner of his garment, and touch with his corner bread, or pottage, or wine, or oil, or any food, shall it become holy? And the priests answered and said, No.
Idan mutum yana riƙe da naman da aka keɓe a rigarsa, sa’an nan kuma wannan rigar ta taɓa burodi, ko dafaffen abinci, ko ruwan inabi, ko mai, ko kowane irin abinci, wannan zai sa abin yă zama tsarkake?’” Firistoci suka amsa, suka ce, “A’a.”
13 Then said Haggai, If one that is unclean by a dead body shall touch any of these, will it become unclean? And the priests answered and said, It will become unclean.
Sa’an nan Haggai ya ce, “In mutumin da ya ƙazantar da kansa ta wurin taɓa gawa, ya taɓa wani daga cikin waɗannan abubuwa, za su ƙazantu?” Firistoci suka amsa, suka ce, “I, zai ƙazantu.”
14 Then answered Haggai, and said, So is this people, and so is this nation before me, saith the Lord; and so are all works of their hands; and what they offer there is unclean.
Sai annabi Haggai ya ce, “‘Haka yake da wannan mutane da kuma wannan al’umma a gabana,’ in ji Ubangiji. ‘Duk abin da suke yi da kuma dukan abin da suke miƙawa ƙazantattu ne.
15 And now direct, I pray you, your heart from this day and upward, before the time that a stone was laid upon a stone in the temple of the Lord:
“‘Yanzu kuwa sai ku yi la’akari da wannan daga wannan rana zuwa gaba, ku tuna yadda al’amura suke kafin a ɗora wani dutse bisa wani a haikalin Ubangiji.
16 Since those days were, when one came to a heap of sheaves of twenty [in number], and there were but ten; when one came to the winepress for to draw off fifty measures out of the vat, and there were but twenty.
A lokacin, idan wani ya tafi wurin tsibin da zai auna mudu ashirin, sai yă iske mudu goma kawai. Idan kuma wani ya tafi wurin matse ruwan inabi don yă ɗebo lita hamsin, sai yă tarar da lita ashirin kawai.
17 I smote you with blasting and with mildew and with hail in all the labors of your hands: yet ye [turned] not [back] to me, saith the Lord.
Na mai da aikin da kuka sha wahala kuka yi ya zama banza ta wurin saukar da burtuntuna, da fumfuna, da ƙanƙara, duk da haka ba ku juyo gare ni ba,’ in ji Ubangiji.
18 Direct, I pray you, your heart from this day and upward, from the four and twentieth day of the ninth month, even from the day that the foundation of the Lord's temple was laid, direct your heart [to this].
‘Daga wannan rana zuwa gaba, wato, rana ta ashirin da huɗu ga watan tara, ku lura da ranar da aka kafa harsashin haikalin Ubangiji. Ku lura da kyau.
19 Is the seed yet in the barn? yes, as yet the vine, and the fig-tree, and the pomegranate, and the olive-tree, have not brought forth; [but] from this day will I bless you.
Akwai sauran irin da ya rage a rumbu? Har yanzu, kuringar inabi da itacen ɓaure, rumman da itacen zaitun ba su ba da’ya’ya ba tukuna. “‘Amma daga wannan rana zuwa gaba zan sa muku albarka.’”
20 And the word of the Lord came the second time unto Haggai on the four and twentieth day of the month, saying,
Maganar Ubangiji ta zo wa annabi Haggai sau na biyu a rana ta ashirin da huɗu ga wata cewa,
21 Speak to Zerubbabel the governor of Judah, saying, I will cause to quake the heavens and the earth;
“Ka faɗa wa Zerubbabel gwamnan Yahuda cewa zan girgiza sammai da ƙasa.
22 And I will overthrow the throne of kingdoms, and I will destroy the strength of the kingdoms of the nations; and I will overthrow chariots, and those that ride in them; and the horses and their riders shall come down, every one by the sword of his brother.
Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
23 On that day, saith the Lord of hosts, will I take thee, O Zerubbabel, the son of Shealthiel, my servant, saith the Lord, and I will place thee as a signet; for of thee have I made choice, saith the Lord of hosts.
“‘A wannan rana,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘Zan ɗauke ka, bawana Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel,’ in ji Ubangiji, ‘in kuma maishe ka kamar zoben hatimi, gama na zaɓe ka,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”

< Haggai 2 >