< 2 Kings 20 >

1 In those days Hezekiah fell sick unto death; and there came to him Isaiah the son of Amoz the prophet, and said unto him, Thus hath said the Lord, Give thy charge to thy house; for thou shalt die, and not live.
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da rashin lafiya har ya kusa mutuwa. Sai annabi Ishaya ɗan Amoz ya zo wurinsa ya ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, ka kintsa gidanka domin za ka mutu, ba za ka warke ba.”
2 Then did he turn his face to the wall, and prayed unto the Lord, saying,
Hezekiya ya juya fuskarsa wajen bango ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce,
3 I beseech thee, O Lord, remember now that I have walked before thee in truth, and with an undivided heart, and have done what is good in thy eyes. And Hezekiah wept aloud.
“Ya Ubangiji, ka tuna yadda na yi tafiya a gabanka da aminci da zuciya ɗaya, na kuma aikata abin da yake daidai a gabanka.” Sai Hezekiya ya yi kuka mai zafi.
4 And it came to pass, before Isaiah was gone out into the middle court, that the word of the Lord came to him, saying,
Kafin Ishaya yă bar tsakiyar filin gida, sai maganar Ubangiji ta zo masa cewa,
5 Return, and say to Hezekiah the ruler of my people, Thus hath said the Lord, the God of David thy father, I have heard thy prayer, I have seen thy tears; behold, I will heal thee: on the third day shalt thou go up unto the house of the Lord.
“Ka koma ka ce wa Hezekiya, shugaban mutanena, ‘Ga abin da Ubangiji Allah na mahaifinka Dawuda ya ce, na ji addu’arka na kuma ga hawayenka; zan warkar da kai. A rana ta uku daga yau za ka haura zuwa haikalin Ubangiji.
6 And I will add unto thy days fifteen years; and out of the hand of the king of Assyria will I deliver thee and this city; and I will shield this city for my own sake, and for the sake of David my servant.
Zan ƙara maka shekara goma sha biyar. Zan kuma cece ka daga hannun sarkin Assuriya. Zan kāre birnin nan saboda kaina da kuma bawana Dawuda.’”
7 And Isaiah said, Fetch a lump of figs. And they fetched and laid it on the inflammation, and he recovered.
Sai Ishaya ya ce, “A kwaɓa ɓaure.” Sai aka yi haka, aka shafa wa marurun, ya kuma warke.
8 And Hezekiah said unto Isaiah, What sign shall there be that the Lord will heal me, and that I shall go up into the house of the Lord the third day?
Hezekiya ya tambayi Ishaya, “Wace alama ce za tă nuna cewa Ubangiji zai warkar da ni, kuma cewa in tafi haikalin Ubangiji kwana uku daga yanzu?”
9 And Isaiah said, This shall be unto thee the sign from the Lord, that the Lord will do the thing that he hath spoken: Shall the shadow go forward ten degrees, or go back ten degrees?
Sai Ishaya ya ce, “Ga alamar Ubangiji zuwa gare ka da za tă nuna cewa Ubangiji zai cika alkawarinsa. Kana so inuwa tă yi gaba da taki goma, ko tă koma baya da taki goma?”
10 And Hezekiah said, It is a light thing for the shadow to go forward ten degrees: no; but let the shadow return backward ten degrees.
“Ai, abu mai sauƙi ne inuwa tă yi gaba da taki goma.” In ji Hezekiya, “Gwamma dai tă koma baya da taki goma.”
11 And Isaiah the prophet called unto the Lord; and he caused the shadow to return, by the degrees which the [sun] was gone down on the dial of Achaz, backward, ten degrees.
Sai annabi Ishaya ya roƙi Ubangiji, Ubangiji kuwa ya sa inuwa ta koma baya da taki goma bisa ga magwajin rana wanda Sarki Ahaz ya gina.
12 And at that time sent Berodach-baladan, the son of Baladan, the king of Babylon, letters and a present unto Hezekiah; for he had heard that Hezekiah had been sick.
A wannan lokaci, Merodak-Baladan ɗan Baladan sarkin Babilon ya aika wa Hezekiya wasiƙu tare da kyauta, domin ya sami labarin rashin lafiyar Hezekiya.
13 And Hezekiah listened unto them, and showed them the whole of his treasure-house, the silver, and the gold, and the spices, and the precious oil, and the whole of his armor-house, and all that was found in his treasures: there was nothing that Hezekiah showed them not, in his house and in all his dominion.
Hezekiya ya karɓi jakadun, ya nuna musu dukan abin da yake a ɗakunan ajiyarsa, azurfa, zinariya, kayan ƙanshi da mai, wurin ajiye makamansa da kuma dukan abin da aka samu a ɗakin ajiyarsa. Babu wani abu a fadansa ko a dukan mulkinsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
14 Then came Isaiah the prophet unto king Hezekiah, and said unto him, What did these men say? and whence did they come unto thee? And Hezekiah said, From a far off country are they come, from Babylon.
Sai annabi Ishaya ya tafi wurin Sarki Hezekiya ya tambaye shi ya ce, “Me mutanen nan suka ce, kuma daga ina suka fito?” Sai Hezekiya ya ce, “Daga ƙasa mai nisa. Daga Babilon.”
15 And he said, What did they see in thy house? And Hezekiah answered, All that is in my house have they seen: there was nothing that I did not show them in my treasures.
Annabin ya yi tambaya, “Me suka gani a fadanka?” Hezekiya ya ce, “Ba abin da yake a ma’ajina da ban nuna musu ba.”
16 And Isaiah said unto Hezekiah, Hear the word of the Lord,
Sai Ishaya ya ce wa Hezekiya, “Ka ji kalmar Ubangiji.
17 Behold, days are coming, when all that is in thy house, and that which thy fathers have laid up in store until this day, shall be carried to Babylon: nothing shall be left, saith the Lord.
Lokaci yana zuwa da za a kwashe kome a fadanka da kuma dukan abubuwan da kakanninka suka tara har yă zuwa yau, a kai su Babilon. Ba abin da za a rage, in ji Ubangiji.
18 And of thy sons that will issue from thee, whom thou wilt beget, shall they take; and they shall be court-servants in the palace of the king of Babylon.
Za a kuma kwashe waɗansu daga cikin zuriyarka, na jiki da jininka waɗanda za a haifa maka, su zama bābānni a fadan sarkin Babilon.”
19 Then said Hezekiah unto Isaiah, Good is the word of the Lord which thou hast spoken. And he said, Is it not so, if there be peace and stability in my days?
Hezekiya ya ce, “Maganar Ubangiji da ka faɗa ta yi kyau.” Gama ya yi tunani cewa, “Ai, ba ni da damuwa, tun da yake za a yi zaman lafiya da salama a kwanakina.”
20 And the rest of the acts of Hezekiah, and all his mighty deeds, and how he made the pool, and the aqueduct, and brought the water into the city, behold, they are written in the book of the chronicles of the kings of Judah.
Game da sauran ayyukan mulkin Hezekiya, dukan nasarorinsa da yadda ya yi tafki da kuma bututun ruwa inda ya kawo ruwa cikin birni, duk a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Yahuda.
21 And Hezekiah slept with his fathers: and Menasseh his son became king in his stead.
Hezekiya ya huta tare da kakanninsa. Manasse ɗansa kuma ya gāje shi.

< 2 Kings 20 >