< 1 Kings 12 >

1 And Rehobo'am went to Shechem; for all Israel were come to Shechem to make him king.
Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ila sun je can don su naɗa shi sarki.
2 And it came to pass, when Jerobo'am the son of Nebat, heard of it, (but he was yet in Egypt, whither he was fled from the presence of king Solomon, and Jerobo'am dwelt in Egypt;
Sa’ad da Yerobowam ɗan Nebat ya ji labari (gama har yanzu yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon), sai ya dawo daga Masar.
3 And they had sent and called him; ) that Jerobo'am and all the congregation of Israel came, and spoke unto Rehobo'am, saying,
Saboda haka mutane suka aika Yerobowam yă zo, sai shi da dukan taron Isra’ila suka tafi wurin Rehobowam, suka ce masa,
4 Thy father made our yoke hard; but do thou now make lighter the hard service of thy father, and his heavy yoke which he put upon us, and we will serve thee.
“Mahaifinka ya sa mana kaya mai nauyin gaske, amma yanzu ka sassauta wannan aiki mai zafi, da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
5 And he said unto them, Go away yet for three days, and then return to me. And the people went away.
Rehobowam ya amsa, “Ku tafi, bayan kwana uku, ku dawo.” Sai mutane suka watse.
6 Then consulted king Rehobo'am with the old men, that had stood before Solomon his father while he yet lived, and said, How do ye advise that I should give an answer to this people?
Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawa waɗanda suka yi wa mahaifinsa Solomon, hidima a kwanakinsa. Ya ce, “Wace shawara ce za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
7 And they spoke unto him, saying, If thou wilt this day be a servant unto this people, and wilt serve them, and be attentive to them, and speak to them good words; then will they be servants unto thee for all times.
Suka amsa, “In a yau za ka zama bawan waɗannan mutane, ka kuma yi musu hidima, ka ba su amsa mai kyau, kullum za su kasance bayinka.”
8 But he forsook the counsel of the old men, which they had given him, and consulted with the young men that were grown up with him, those who stood before him:
Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawan suka ba shi, sai ya nemi shawarar matasa waɗanda suka yi girma tare, waɗanda kuma suke masa hidima.
9 And he said unto them, What do you counsel how we should give an answer to this people, who have spoken to me, saying, Make lighter the yoke which thy father did put upon us?
Ya tambaye su, “Mece ce shawararku? Yaya za mu amsa wa waɗannan mutane masu cewa, ‘Ka sassauta nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
10 Then spoke unto him the young men that were grown up with him, saying, Thus must thou say unto this people that have spoken unto thee, saying, Thy father made our yoke heavy, but do thou make it lighter unto us: thus must thou speak unto them, My little finger is thicker than my father's loins.
Matasan, waɗanda suka yi girma tare da shi, suka amsa, “Faɗa wa waɗannan mutanen da suka ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sassauta kayanka.’ Ka ce musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun tsohona kauri.
11 And now, if my father hath burdened you with a heavy yoke, I will even add to your yoke; if my father hath chastised you with whips, then will I chastise you with scorpion-thorns.
Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.’”
12 When now Jerobo'am and all the people came to Rehobo'am on the third day, as the king had spoken, saying, Return to me on the third day.
Bayan kwana uku, Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam yadda sarki ya faɗa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
13 The king answered the people harshly, and forsook the old men's counsel that they had advised him;
Sai Sarki ya amsa wa mutane da zafi. Yana ƙin shawarar da dattawa suka ba shi.
14 And he spoke to them after the counsel of the young men, saying, My father made your yoke heavy, and I will even add to your yoke; my father chastised you with whips, but I will chastise you with scorpion-thorns.
Ya bi shawarar matasa, ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.”
15 Thus the king hearkened not unto the people; for it was so brought about from the Lord, in order that he might fulfill his word, which the Lord had spoken by means of Achiyah the Shilonite unto Jerobo'am the son of Nebat.
Saboda haka sarki bai saurare mutane ba, gama wannan abin da ya faru daga wurin Ubangiji ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi wa Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya, mutumin Shilo.
16 So when all Israel saw that the king hearkened not unto them, the people gave the king an answer saying, What portion have we in David? nor have we an inheritance in the son of Jesse; to your tents, O Israel: now see to thy own house, David. So did Israel go away unto their tents.
Da dukan Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, “Ina ruwanmu da Dawuda! Ai! Ba mu da gādo wurin ɗan Yesse. Ya Isra’ila, kowa yă koma tentinsa! Dawuda, sai ka lura da gidanka!” Saboda haka Isra’ilawa suka watse zuwa gida.
17 But as for the children of Israel who dwelt in the cities of Judah, over them did Rehobo'am reign.
Amma ga Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da mulki a kansu.
18 Then sent king Rehobo'am Adoram, who was over the tribute; but all Israel stoned him with stones, that he died. Therefore king Rehobo'am made speed with all his might to get up into his chariot, to flee to Jerusalem.
Sarki Rehobowam ya aiki Adoniram wanda yake shugaban aikin gandu, amma Isra’ila suka jajjefe shi da dutse har ya mutu. Sarki Rehobowam, ya sullale ya hau keken yaƙinsa ya tsere zuwa Urushalima.
19 So did Israel rebel against the house of David unto this day.
Tun daga wannan ranar ne mutanen Isra’ila suka shiga gāba da gidan Dawuda har wa yau.
20 And it came to pass, when all Israel heard that Jerobo'am was returned, that they sent and called him unto the congregation, and made him king over all Israel: there was none that followed the house of David, save the tribe of Judah alone.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ji Yerobowam ya dawo, sai suka aika, suka kira shi zuwa taro, suka kuma naɗa shi sarki bisa dukan Isra’ila. Kabila Yahuda kaɗai ta kasance mai biyayya ga gidan Dawuda.
21 And when Rehobo'am was come to Jerusalem, he assembled all the house of Judah, with the tribe of Benjamin, a hundred and eighty thousand chosen men, warriors, to fight against the house of Israel, to bring back the kingdom to Rehobo'am the son of Solomon.
Da Rehobowam ya isa Urushalima, ya tattara dukan gidan Yahuda da kabilar Benyamin, ya sami sun kai mayaƙa dubu da tamanin. Sai aka shirya don su yaƙi gidan Isra’ila, su kuma mayar da masarautar wa Rehobowam ɗan Solomon.
22 But the word of God came unto Shema'yah the man of God, saying,
Amma waɗannan kalmomin Allah suka zo wa Shemahiya, mutumin Allah, cewa,
23 Say unto Rehobo'am, the son of Solomon, the king of Judah, and unto all the house of Judah and Benjamin, and to the remnant of the people, saying,
“Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon, sarkin Yahuda, ka faɗa wa dukan gidan Yahuda da Benyamin, da kuma dukan sauran mutane,
24 Thus hath said the Lord, Ye shall not go up, nor fight with your brethren the children of Israel: return every man to his house; for from me hath this thing been brought about. And they hearkened to the word of the Lord, and returned to go home, according to the word of the Lord.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku, Isra’ilawa. Ku koma gida, kowannenku, gama wannan aikina ne.”’” Saboda haka suka yi biyayya da maganar Ubangiji, suka sāke watse zuwa gida, yadda Ubangiji ya umarta.
25 And Jerobo'am built Shechem in the mountain of Ephraim, and dwelt therein; and he went out from there and built Penuel.
Sai Yerobowam ya ƙara gina Shekem a ƙasar tudu ta Efraim, ya zauna a can. Daga can ya tafi ya gina Fenuwel.
26 And Jerobo'am said in his heart, Now may the kingdom return to the house of David:
Yerobowam ya yi tunani a ransa ya ce, “Mai yiwuwa mulkin yă koma gidan Dawuda.
27 If this people go up to prepare sacrifices in the house of the Lord at Jerusalem, then may the heart of this people turn again unto their Lord, even unto Rehobo'am the king of Judah, and they might kill me, and return to Rehobo'am the king of Judah.
In waɗannan mutane sun riƙa haurawa don su miƙa hadayu a haikalin Ubangiji a Urushalima. Za su sāke nuna biyayya ga mai girma, Rehobowam, sarkin Yahuda. Za su kashe ni su kuma koma ga Sarki Rehobowam.”
28 Whereupon the king took counsel, and he made two calves of gold, and said unto the people, You have been long enough going up to Jerusalem: behold, here are thy gods, O Israel, which have brought thee up out of the land of Egypt.
Bayan ya nemi shawara, sai sarki ya yi siffofin’yan maruƙa biyu na zinariya. Ya ce wa mutane, “Kun daɗe kuna haurawa zuwa can Urushalima. Ga allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga ƙasar Masar.”
29 And he placed the one in Beth-el, and the other put he in Dan.
Sai ya kafa ɗaya a Betel, ɗaya kuma a Dan.
30 And this thing became a sin; and the people went before the one, as far as Dan.
Wannan ya zama zunubi, gama mutane suna tafiya yin wa wannan da yake a Betel sujada, su kuma je har Dan don su yi wa ɗayan sujada.
31 And he made a house of the high-places, and made priests of the lowest of the people, who were not of the sons of Levi.
Yerobowam ya gina masujadai da suke kan tuddai, ya kuma naɗa firistoci barkatai daga cikin mutanen da ba na zuriyar Lawi ba.
32 And Jerobo'am made a feast in the eighth month, on the fifteenth day of the month, like unto the feast that is in Judah, and he offered upon the altar; so did he in Beth-el, sacrificing unto the calves that he had made: and he stationed at Beth-el the priests of the high-places whom he had made.
Ya kafa biki a rana ta goma sha biyar ta watan takwas, kamar bikin da ake yi a Yahuda, ya kuma miƙa hadayu a bisa bagade. Ya yi haka a Betel, yana miƙa wa siffofin maruƙan da ya yi hadayu. A Betel kuma ya naɗa firistoci a wuraren tudun da ya yi.
33 So he offered upon the altar which he had made in Beth-el on the fifteenth day of the eighth month, in the month which he had falsely devised of his own heart; and he ordained a feast unto the children of Israel, and he went up to the altar, to burn incense.
A rana ta goma sha biyar ta watan takwas, watan da ya zaɓa, ya miƙa hadayu a bisa bagaden da ya gina a Betel. Saboda haka ya kafa biki don Isra’ilawa, ya kuma haura zuwa bagade don yă miƙa hadayu.

< 1 Kings 12 >